< Psaumes 107 >
1 Louez le Seigneur, parce qu’il est bon, parce que pour jamais est sa miséricorde.
Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 Qu’ils le disent, ceux qui ont été rachetés par le Seigneur, qu’il a rachetés de la main d’un ennemi, qu’il a rassemblés en les retirant des contrées,
Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
3 De l’orient et du couchant, de l’aquilon et de la mer.
su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
4 Ils ont erré dans la solitude, dans un lieu sans eau; ils n’ont pas trouvé de voie vers une cité habitée;
Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
5 Affamés et altérés, leur âme a défailli en eux-mêmes.
Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
6 Ils ont crié vers le Seigneur, lorsqu’ils étaient dans la tribulation, et il les a arrachés à leurs nécessités pressantes.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
7 Et il les a conduits dans une voie droite, afin qu’ils allassent dans une cité habitable.
Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
8 Qu’elles louent le Seigneur, ses miséricordes et ses merveilles en faveur des fils des hommes.
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
9 Parce qu’il a rassasié l’âme vide, et qu’il a rassasié de biens l’âme affamée;
gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
10 Ceux qui étaient assis dans des ténèbres et dans l’ombre de la mort, enchaînés dans l’indigence et les fers;
Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
11 Parce qu’ils aigrirent
gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
12 Aussi leur cœur a été humilié dans les travaux, ils ont été affaiblis, et il n’y eut personne qui les secourût.
Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
13 Ils ont crié vers le Seigneur, lorsqu’ils étaient dans la tribulation, et il les a délivrés de leurs nécessités pressantes.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
14 Et il les a tirés des ténèbres et de l’ombre de la mort, et il a rompu leurs liens.
Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
15 Qu’elles louent le Seigneur, ses miséricordes et ses merveilles en faveur des fils des hommes.
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
16 Parce qu’il a brisé des portes d’airain, et rompu des verroux de fer.
gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
17 Il les a recueillis en les tirant de la voie de leur iniquité; car à cause de leurs injustices, ils avaient été humiliés.
Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
18 Leur âme avait eu horreur de toute nourriture; aussi ils approchèrent jusqu’aux portes de la mort.
Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
19 Ils ont crié vers le Seigneur, lorsqu’ils étaient dans la tribulation, et il les a délivrés de leurs nécessités pressantes.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
20 Il a envoyé sa parole, et il les a guéris, et il les a arrachés à leur destruction.
Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
21 Qu’elles louent le Seigneur, ses miséricordes et ses merveilles en faveur des fils des hommes;
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
22 Qu’ils sacrifient un sacrifice de louange, et qu’ils annoncent ses œuvres dans l’exultation.
Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
23 Ceux qui descendent sur la mer dans des navires, et qui font la manœuvre sur les grandes eaux.
Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
24 Ceux-là même ont vu les œuvres du Seigneur, et ses merveilles dans le profond de l’abîme.
Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
25 Il a dit, et un vent de tempête s’est levé, et les flots de la mer se sont soulevés.
Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
26 Ils montent jusqu’aux cieux, et ils descendent jusqu’aux abîmes; leur âme dans les maux se consumait.
Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
27 Ils ont été troublés, ils ont chancelé comme un homme ivre, et toute leur sagesse a été absorbée.
Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
28 Ils ont crié vers le Seigneur, lorsqu’ils étaient dans la tribulation, et il les a délivrés de leurs nécessités pressantes.
Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
29 Il a changé la tempête en une brise légère, et les flots de la mer se sont tenus en silence.
Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
30 Et ils se sont réjouis de ce que les flots se tenaient en silence, et il les a conduits au port de leur désir.
Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
31 Qu’elles louent le Seigneur, ses miséricordes et ses merveilles en faveur des fils des hommes.
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
32 Et qu’on l’exalte dans l’assemblée du peuple, et que dans la chaire des anciens, on le loue.
Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
33 Il a changé des fleuves en désert, et des cours d’eau en un sol aride,
Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
34 Une terre fertile en un champ de sel, à cause de la malice de ceux qui y habitaient.
ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
35 Mais ensuite il a changé un désert en un étang plein d’eau, et une terre sans eau en des cours d’eaux.
Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
36 Il a placé là ceux qui étaient affamés, et ils ont élevé une cité habitable.
a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
37 Ils ont ensemencé des champs, et ont planté des vignes: et elles ont fait naître du fruit.
Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
38 Et il les a bénis, ils se sont multipliés, et il n’a pas diminué leurs bestiaux.
ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
39 Mais ils sont devenus en petit nombre, et tourmentés par la tribulation des maux et par la douleur.
Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
40 Le mépris s’est répandu sur leurs princes, et le Seigneur les a fait errer dans un lieu sans chemin frayé, et non dans une voie.
shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
41 Et il a aidé le pauvre en le délivrant de son indigence, et il a fait ses familles nombreuses comme des brebis.
Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
42 Les justes verront et se réjouiront, et toute iniquité fermera sa bouche.
Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
43 Qui est sage et gardera ces choses, et comprendra les miséricordes du Seigneur?
Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.