< Psaumes 105 >
1 Louez le Seigneur, et invoquez son nom: annoncez, parmi les nations, ses œuvres.
Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
2 Chantez-le, et jouez du psaltérion en son honneur: racontez toutes ses merveilles.
Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
3 Glorifiez-vous en son nom saint: qu’il se réjouisse, le cœur de ceux qui cherchent le Seigneur.
Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
4 Cherchez le Seigneur et soyez fortifiés: cherchez sa face sans cesse.
Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
5 Souvenez-vous de ses merveilles qu’il a faites; de ses prodiges, et des jugements de sa bouche,
Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
6 Postérité d’Abraham, ses serviteurs, enfants de Jacob, ses élus.
Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
7 Lui-même est le Seigneur notre Dieu: sur toute la terre s’exercent ses jugements.
Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
8 Il s’est toujours souvenu de son alliance; de la parole qu’il a prescrite pour mille générations,
Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
9 Qu’il a donnée à Abraham; de son serment à Isaac;
alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
10 Et il a établi ce serment avec Jacob en précepte, et avec Israël en alliance éternelle,
Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
11 Disant: Je te donnerai la terre de Chanaan pour cordeau de votre héritage.
“Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
12 Lorsqu’ils étaient un petit nombre, très peu nombreux, et étrangers dans cette terre;
Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
13 Et ils passèrent de nation en nation, et d’un royaume à un autre peuple;
suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
14 Il ne permit pas qu’aucun homme leur fît du mal, il châtia même les rois à cause d’eux.
Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
15 Ne touchez pas âmes oints, et ne maltraitez pas mes prophètes.
“Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
16 Et il appela la famine sur la terre, et il brisa tout soutien de pain.
Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
17 Il envoya devant eux un homme: Joseph qui fut vendu comme esclave.
ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
18 On humilia ses pieds dans des entraves; un fer transperça son âme.
Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
19 Jusqu’à ce que s’accomplît sa parole. La parole du Seigneur l’enflamma;
sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
20 Le roi envoya et le délia: le prince des peuples envoya, et le mit en liberté.
Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya’yantar da shi.
21 Il l’établit maître de sa maison, et prince de toutes ses possessions;
Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
22 Afin qu’il instruisît ses princes comme lui-même, et qu’il enseignât la sagesse à ses vieillards.
don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
23 Et Israël entra en Egypte, et Jacob habita comme étranger dans la terre de Cham.
Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
24 Et Dieu y multiplia son peuple prodigieusement, et le rendit plus puissant que ses ennemis.
Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
25 Il changea leur cœur, afin qu’ils haïssent son peuple, et qu’ils employassent la fraude contre ses serviteurs.
waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
26 Il envoya Moïse son serviteur, et Aaron qu’il choisit aussi.
Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
27 Il leur donna l’ordre de faire des signes et des prodiges dans la terre de Cham.
Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
28 Il envoya des ténèbres, et répandit l’obscurité; et il ne rétracta pas ses paroles.
Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
29 Il changea leurs eaux en sang, et fit mourir leurs poissons.
Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
30 Leur terre produisit des grenouilles, qui pénétrèrent dans les appartements de leurs rois.
Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
31 Il dit, et il vint des myriades de mouches, et des moucherons dans tout leur pays.
Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
32 Il changea leurs pluies en grêle, et envoya un feu qui brûlait dans leur terre.
Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
33 Et il frappa leurs vignes et leurs figuiers, et brisa les arbres de leur pays.
ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu ya ragargaza itatuwan ƙasarsu.
34 Il dit, et vint la sauterelle, et la chenille qui était sans nombre;
Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito, fāran da ba su ƙidayuwa;
35 Et elle mangea toute l’herbe dans leur terre, et elle mangea tout le fruit de leur terre.
suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu, suka cinye amfanin gonarsu
36 Et il frappa tout premier-né dans leur terre, et les prémices de tout leur travail.
Sa’an nan ya karkashe dukan’yan fari a cikin ƙasarsu, nunan fari na dukan mazantakarsu.
37 Et il les fit sortir avec de l’or et de l’argent: et il n’y avait pas dans leurs tribus un seul malade.
Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
38 L’Égypte se réjouit à leur départ, parce que la crainte qu’elle avait d’eux fondit sur elle.
Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
39 Il étendit une nuée pour les couvrir, et un feu pour les éclairer pendant la nuit.
Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
40 Ils demandèrent, et la caille vint; et du pain du ciel il les rassasia.
Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
41 Il fendit un rocher, et des eaux coulèrent: et dans un lieu sec se répandirent des fleuves;
Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
42 Parce qu’il se souvint de sa parole sainte qu’il a donnée à Abraham, son serviteur.
Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
43 Et il fit sortir son peuple dans l’exultation, et ses élus dans l’allégresse.
Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
44 Et il leur donna les contrées des nations, et ils possédèrent les travaux des peuples;
ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
45 Afin qu’ils gardent ses ordonnances, et qu’ils recherchent sa loi.
don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.