< Psaumes 103 >

1 De David lui-même.
Ta Dawuda. Yabi Ubangiji, ya raina; dukan abin da yake cikin cikina, yabi sunansa mai tsarki.
2 Bénis, mon âme, le Seigneur, et n’oublie point ses bienfaits.
Yabi Ubangiji, ya raina, kada kuma ka manta dukan alheransa,
3 C’est lui qui pardonne toutes tes iniquités; lui qui guérit toutes tes infirmités.
wanda yake gafarta dukan zunubai yake kuma warkar da dukan cututtuka,
4 C’est lui qui rachète de la mort ta vie; qui te couronne de miséricorde et de bontés.
wanda ya fanshi ranka daga rami ya naɗa maka rawani da ƙauna da kuma tausayi,
5 C’est lui qui remplit de biens ton désir: ta jeunesse sera renouvelée comme celle de l’aigle.
Wanda ya ƙosar da kai da abubuwa masu kyau domin a sabunta ƙuruciyarka kamar na gaggafa.
6 Le Seigneur fait miséricorde et justice à tous ceux qui souffrent une injustice.
Ubangiji yana aikata adalci da kuma gaskiya ga duk waɗanda aka danne.
7 Il a fait connaître ses voies à Moïse, aux enfants d’Israël ses volontés.
Ya sanar da hanyoyinsa wa Musa, ayyukansa ga mutanen Isra’ila.
8 Compatissant et miséricordieux est le Seigneur; lent à punir et bien miséricordieux.
Ubangiji mai tausayi ne da kuma alheri, mai jinkirin fushi, cike da ƙauna.
9 Il ne sera pas perpétuellement irrité; et éternellement il ne menacera pas.
Ba zai yi ta zargi ba ba kuwa zai yi ta jin fushi har abada ba;
10 Ce n’est pas selon nos péchés qu’il nous a traités; ni selon nos iniquités qu’il nous a rétribués.
ba ya yin da mu gwargwadon zunubanmu ko yă sāka mana bisa ga laifofinmu.
11 Puisque, selon la hauteur des cieux au-dessus de la terre, il a corroboré sa miséricorde sur ceux qui le craignent.
Gama kamar yadda sammai suke can bisa duniya, haka girmar ƙaunarsa yake wa masu tsoronsa;
12 Autant est distant l’orient de l’occident, autant il a éloigné de nous nos iniquités.
kamar yadda gabas yake daga yamma, haka ya cire laifofinmu daga gare mu.
13 De même qu’un père s’attendrit sur ses enfants, de même le Seigneur a eu pitié de ceux qui le craignent;
Kamar yadda mahaifi yake jin tausayin’ya’yansa, haka Ubangiji yake jin tausayin waɗanda suke tsoronsa;
14 Parce que lui-même sait de quoi nous sommes formés. Il s’est souvenu que nous sommes poussière;
gama ya san yadda aka yi mu, ya tuna cewa mu ƙura ne.
15 Un homme, ses jours sont comme une herbe: comme une fleur des champs, ainsi il fleurira.
Game da mutum dai, kwanakinsa suna kamar ciyawa da suke haɓaka kamar fure a gona;
16 Parce qu’un souffle passera sur elle, et elle ne subsistera pas: et on ne connaîtra plus son lieu.
iska kan hura a kansa sai ya ɓace ba a kuwa sāke tuna da inda dā yake.
17 Mais la miséricorde du Seigneur est de l’éternité et jusqu’à l’éternité sur ceux qui le craignent.
Amma daga madawwami zuwa madawwami ƙaunar Ubangiji tana tare da waɗanda suke tsoronsa, adalcinsa kuma tare da’ya’yansu,
18 Pour ceux qui gardent son alliance. Et se souviennent de ses commandements, pour les accomplir.
tare da waɗanda suke kiyaye alkawarinsa suna kuma tuna su yi biyayya da farillansa.
19 Le Seigneur dans le ciel a préparé son trône; et son empire dominera sur toutes choses.
Ubangiji ya kafa kursiyinsa a sama, masarautarsa kuwa na mulki a bisa duka.
20 Bénissez le Seigneur, vous tous ses anges, puissants en force, accomplissant sa parole, pour obéir à la voix de ses ordres.
Yabi Ubangiji, ku mala’ikunsa, ku jarumawa masu yi masa aiki, waɗanda suke yin biyayya da maganarsa.
21 Bénissez le Seigneur, vous toutes ses armées célestes; vous ses ministres, qui faites sa volonté.
Yabi Ubangiji, dukanku rundunarsa ta sama, ku bayinsa waɗanda kuke aikata nufinsa.
22 Bénissez le Seigneur, vous tous ses ouvrages, dans tous les lieux de sa domination: bénis, mon âme, le Seigneur.
Yabi Ubangiji, dukanku ayyukansa ko’ina a mulkinsa. Yabi Ubangiji, ya raina.

< Psaumes 103 >