< Proverbes 8 >

1 Est-ce que la sagesse ne crie pas, et que la prudence ne fait pas entendre sa voix?
Hikima ba ta yin kira ne? Fahimi ba ya tā da muryarsa ne?
2 Sur les plus hauts et les plus élevés sommets, au-dessus de la voie, se tenant au milieu des sentiers,
A ƙwanƙoli a kan hanya, inda hanyoyi suka haɗu, ta ɗauki matsayinta;
3 Près des portes de la cité, à l’entrée même de la ville, elle parle, disant:
kusa da ƙofofin shiga cikin birni, a mashigai, ta tā da murya,
4 Ô hommes, c’est à vous que je crie, et ma voix s’adresse aux fils des hommes.
“Gare ku, ya mutane, nake kira; na tā da muryata ga dukan’yan adam.
5 Apprenez, ô tout petits, la finesse, et vous, insensés, faites attention.
Ku da kuke marasa azanci, ku yi hankali; ku da kuke wawaye, ku nemi fahimi.
6 Ecoutez, car je vais parler de grandes choses, et mes lèvres s’ouvriront pour proclamer la droiture.
Ku saurara, gama ina da abubuwa masu darajan da zan faɗa; na buɗe leɓunana don in faɗa abin da yake daidai.
7 Ma bouche s’exercera à la vérité, et mes lèvres détesteront ce qui est impie.
Bakina yana magana abin da yake gaskiya, gama leɓunana sun ƙi mugunta.
8 Tous mes discours sont justes, il n’y a rien de dépravé ni de pervers.
Dukan kalmomin bakina suna da adalci; babu waninsu da ya karkace ko kuwa ƙarya ne.
9 Ils sont droits pour ceux qui ont de l’intelligence, et équitables pour ceux qui trouvent la science.
Ga mai tunani dukansu daidai ne; ba su da laifi ga waɗanda suke da sani.
10 Recevez ma discipline et non de l’argent: choisissez la doctrine plutôt que l’or.
Ku zaɓi umarnina a maimakon azurfa, sani a maimakon zinariya zalla,
11 Car mieux vaut la sagesse que toutes les choses les plus précieuses; et tout ce qu’il y a de désirable ne peut lui être comparé.
gama hikima ta fi lu’ulu’ai daraja, kuma ba abin da kake sha’awa da za a kwatanta da ita.
12 Moi, sagesse, j’habite dans le conseil, et je suis présente aux savantes pensées.
“Ni, hikima, ina zama tare da hankali; ina da sani da iya rarrabewa.
13 La crainte du Seigneur hait le mal: l’arrogance et l’orgueil, une voie dépravée, et une langue double, je les déteste.
Jin tsoron Ubangiji shi ne ƙin mugunta; ina ƙin girman kai da fariya, halin mugunta da kuma muguwar magana.
14 À moi est le conseil et l’équité: à moi est la prudence, à moi est la force.
Shawara da yin tunani mai kyau nawa ne; ina da fahimi da kuma iko.
15 Par moi les rois règnent, et les législateurs décrètent des choses justes;
Ta wurina sarakuna suke mulki masu mulki kuma suke yin dokokin da suke da adalci;
16 Par moi les princes commandent, et les puissants rendent la justice.
ta wurina sarakuna suke mulki, da kuma dukan manyan mutanen da suke mulkin duniya.
17 Moi, j’aime ceux qui m’aiment, et ceux qui dès le matin veillent pour me chercher me trouveront.
Ina ƙaunar waɗanda suke ƙaunata, kuma waɗanda suke nemana sukan same ni.
18 Avec moi sont les richesses et la gloire, des biens superbes, et la justice.
Tare da ni akwai wadata da girmamawa, dukiya da wadata masu dawwama.
19 Car mieux vaut mon fruit que l’or et les pierres précieuses, et mieux valent mes produits que l’argent le meilleur.
’Ya’yan itacena sun fi zinariya zalla; amfanin gonar da nake bayar ya fi azurfa mafi kyau.
20 Je marche dans les voies de la justice, au milieu des sentiers du jugement,
Ina tafiya a hanyar adalci, a kan hanyoyin gaskiya,
21 Afin d’enrichir ceux qui m’aiment, et de remplir leurs trésors.
ina ba da wadata ga waɗanda suke ƙaunata ina sa wuraren ajiyarsu su cika.
22 Le Seigneur m’a possédée au commencement de ses voies, avant qu’il fît quelque chose dès le principe.
“Ubangiji ya kawo ni a matsayi na farko na ayyukansa, kafin ayyukansa na tuntuni;
23 Dès l’éternité j’ai été établie, dès les temps anciens, avant que la terre fût faite.
an naɗa ni tun fil azal, daga farko, kafin duniya ta kasance.
24 Les abîmes n’étaient pas encore, et moi déjà j’avais été conçue; les sources des eaux n’avaient pas encore jailli:
Sa’ad da babu tekuna, aka haife ni, sa’ad da babu maɓulɓulai masu ruwa;
25 Les montagnes à la pesante masse n’étaient pas encore affermies, et moi, avant les collines, j’étais engendrée:
kafin a kafa duwatsu a wurarensu, kafin tuddai ma, an haife ni,
26 Il n’avait pas encore fait la terre et les fleuves, et les pôles du globe de la terre.
kafin ya yi duniya ko gonaki ko wata ƙurar duniya.
27 Quand il préparait les cieux, j’étais présente: quand par une loi inviolable il entourait d’un cercle les abîmes:
Ina nan sa’ad da ya kafa sammai a wurarensu, sa’ad da ya shata sararin sama a kan fuskar zurfafa,
28 Quand il affermissait en haut la voûte éthérée, et qu’il mettait en équilibre les sources des eaux:
sa’ad da ya kafa gizagizai a bisa ya kuma kafa maɓulɓulan zurfafa daram,
29 Quand il mettait autour de la mer ses limites, et qu’il imposait une loi aux eaux, afin qu’elles n’allassent point au-delà de leurs bornes; quand il pesait les fondements de la terre:
sa’ad da ya ba wa teku iyakarsa domin kada ruwaye su zarce umarninsa, da kuma sa’ad da ya shata tussan duniya.
30 J’étais avec lui, disposant toutes choses; et je me réjouissais chaque jour, me jouant, en tout temps, devant lui:
A lokacin ni ne mai tsara abubuwa a gefensa. Na cika da murna kowace rana, kullum ina farin ciki a gabansa,
31 Me jouant dans le globe de la terre; et mes délices sont d’être avec les fils des hommes.
ina farin ciki da dukan duniyarsa ina murna da’yan adam.
32 Maintenant donc, mes fils, écoutez-moi: Bienheureux ceux gardent mes voies.
“Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; masu albarka ne waɗanda suke kiyaye hanyoyina.
33 Ecoutez la discipline, et soyez sages, et n’allez pas la rejeter.
Ku saurari umarnina ku kuma zama masu hikima; kada ku ƙyale ta.
34 Bienheureux l’homme qui m’écoute, et qui veille tous les jours à l’entrée de ma demeure, et se tient en observation auprès de ma porte.
Mai albarka ne wanda ya saurare ni; yana tsaro kullum a ƙofofina, yana jira a ƙofar shigata.
35 Celui qui me trouvera trouvera la vie, et puisera le salut dan? le Seigneur:
Gama duk wanda ya same ni ya sami rai zai kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
36 Mais celui qui péchera contre moi blessera son âme. Tous ceux qui me haïssent aiment la mort.
Amma duk wanda ya kāsa samuna ya cuci kansa; dukan waɗanda suke ƙina suna ƙaunar mutuwa ke nan.”

< Proverbes 8 >