< Proverbes 31 >
1 Paroles de Lamuel roi. Vision par laquelle l’a instruit sa mère.
Maganganun Sarki Lemuwel, magana ce horarriya mahaifiyarsa ta koya masa,
2 Que te dirai-je, mon bien aimé, que te dirai-je, bien aimé de mon sein, que te dirai-je, bien-aimé de mes vœux?
“Ka saurara, ya ɗana! Ka saurara, ɗan cikina! Ka saurara, ya ɗan amshin addu’ata!
3 Ne donne pas aux femmes ton bien, et tes richesses pour perdre des rois.
Kada ka ba da ƙarfinka a kan mata, ƙarfinka ga waɗanda suka hallaka sarakuna.
4 Non aux rois, ô Lamuel, non aux rois, ne donne pas de vin, parce qu’il n’est nul secret où règne l’ivresse:
“Ba na sarakuna ba ne, ya Lemuwel, ba na sarakuna ba ne su sha ruwan inabi, ba na masu mulki ba ne su yi marmarin barasa,
5 Et de peur qu’ils ne boivent et qu’ils n’oublient les jugements, et qu’ils ne changent la cause des fils du pauvre.
don kada su sha su manta da abin da doka ta umarta, su hana wa waɗanda aka danne hakkinsu.
6 Donnez de la cervoise à ceux qui sont affligés, et du vin à ceux qui ont le cœur dans l’amertume;
A ba da barasa ga waɗanda suke cikin halin ƙaƙa naka yi, ruwan inabi ga waɗanda suke cikin wahala;
7 Qu’ils boivent et qu’ils oublient leur détresse, et que de leur douleur ils ne se souviennent plus.
bari su sha su manta da talaucinsu kada kuma su ƙara tunawa da ɓacin ransu.
8 Ouvre ta bouche pour le muet, et pour les causes de tous les fils qui passent;
“Yi magana domin bebaye, domin hakkin dukan waɗanda suke naƙasassu.
9 Ouvre ta bouche, décrète ce qui est juste, et juge l’homme qui est sans ressources, et le pauvre.
Yi magana a kuma yi shari’ar adalci; a tsare hakkin talakawa da masu bukata.”
10 Une femme forte, qui la trouvera? au-dessus de ce qui vient de loin et des derniers confins du monde est son prix.
Wa yake iya samun mace mai halin kirki? Darajarta ta fi ta lu’ulu’ai.
11 Le cœur de son mari se confie en elle; et il ne manquera pas de dépouilles.
Mijinta yana da cikakken amincewa da ita kuma ba ya rasa wani abu mai daraja.
12 Elle lui rendra le bien et non le mal, tous les jours de sa vie.
Takan yi masa alheri ba mugunta ba, dukan kwanakin ranta.
13 Elle a cherché la laine et le lin, et elle a travaillé par le conseil de ses mains.
Takan zaɓi ulu da lilin ta yi ta saƙa da hannuwanta da farin ciki.
14 Elle est devenue comme le vaisseau d’un marchand, portant de loin son pain.
Ita kamar jirgin’yan kasuwa ne tana kawo abincinta daga nesa.
15 Et de nuit elle s’est levée, et elle a donné de la nourriture aux personnes de sa maison, et des vivres à ses servantes.
Takan farka tun da sauran duhu; ta tanada wa iyalinta abinci ta kuma shirya wa’yan matan gidanta ayyukan da za su yi.
16 Elle a considéré un champ et l’a acheté: du fruit de ses mains, elle a planté une vigne.
Takan lura da gona sosai ta kuma saye ta; daga abin da take samu na kuɗin shiga take shuka gonar inabi.
17 Elle a ceint de force ses reins, et elle a affermi son bras.
Takan himmantu tă yi aikinta tuƙuru; hannuwanta suna da ƙarfi domin ayyukanta.
18 Elle a goûté et elle a vu que son commerce est bon: pendant la nuit, sa lampe ne s’éteindra pas.
Takan tabbata akwai riba a kasuwancinta, kuma fitilarta ba ya mutuwa da dare.
19 Elle a mis sa main à des choses fortes; et ses doigts ont pris le fuseau.
Da hannunta take riƙe abin kaɗi ta kuma kama abin saƙa da yatsotsinta.
20 Elle a ouvert sa main à l’homme sans ressources, et ses paumes, elles les a détendues vers le pauvre.
Takan marabci talakawa takan kuma taimaki masu bukata.
21 Elle ne craindra pas pour sa maison le froid de la neige, car toutes les personnes de sa maison ont un double vêtement.
Sa’ad da ƙanƙara ta fāɗi, ba ta jin tsoro saboda gidanta; gama dukansu suna da tufafi masu kauri.
22 Elle s’est fait une couverture: le fin lin et la pourpre forment son vêtement.
Takan yi wa gadonta kayan shimfiɗa; tufafinta kuma na lilin ne mai laushi na shunayya.
23 Illustre sera son mari aux portes de la ville, quand il siégera avec les sénateurs de la terre.
Ana girmama mijinta a ƙofar shiga birni inda yakan zauna a cikin dattawan gari.
24 Elle a fait un fin tissu, et elle l’a vendu; et elle a livré une ceinture au Chananéen.
Takan yi riguna na lilin ta sayar; takan kuma sayar wa’yan kasuwa da ɗamara.
25 La force et la beauté sont son vêtement, et elle rira au jour dernier.
Ƙarfi da mutunci su ne suturarta; za tă iya yin dariyar kwanaki masu zuwa.
26 Elle a ouvert sa bouche à la sagesse, et la loi de la clémence est sur sa langue.
Tana magana da hikima, kuma umarnai mai aminci yana a harshenta.
27 Elle a considéré les sentiers de sa maison, et elle n’a pas mangé de pain dans l’oisiveté.
Tana lura da sha’anin gidanta kuma ba ta cin abincin ƙyuya.
28 Ses fils se sont levés et l’ont proclamée très heureuse; son mari s’est levé, et l’a louée.
’Ya’yanta sukan tashi su ce da ita mai albarka; haka mijinta ma, yakan kuma yabe ta yana cewa,
29 Beaucoup de filles ont amassé des richesses: mais toi, tu les as toutes surpassées.
“Mata da yawa suna yin abubuwan yabo, amma ke kin fi su duka.”
30 Trompeuse est la grâce, et vaine est la beauté: la femme qui craint le Seigneur est celle qui sera louée.
Kayan tsari yana ruɗu, kyau kuma kan shuɗe; amma mace mai tsoron Ubangiji abar yabo ce.
31 Donnez-lui le fruit de ses mains, et que ses œuvres la louent aux portes de la ville.
Ka ba ta ladar da ya dace tă samo wa kanta, bari kuma ayyukanta su kawo mata yabo a ƙofar shiga birni.