< Proverbes 24 >
1 Ne porte pas envie aux hommes méchants, et ne désire pas d’être avec eux;
Kada ka yi ƙyashin mugaye, kada ka yi sha’awar ƙungiyarsu;
2 Parce que leur âme médite des rapines, et que leurs lèvres parlent fraudes.
gama leɓunansu suna maganar tā-da-na-zaune-tsaye ne.
3 C’est par la sagesse que se bâtira une maison, et par la prudence qu’elle s’affermira.
Ta wurin hikima ce ake gina gida, kuma ta wurin fahimi ake kafa ta;
4 Par la science, les celliers se rempliront de toute sorte de biens précieux et très beaux.
ta wurin sani ɗakunanta sukan cika da kyawawan kayayyaki masu daraja.
5 L’homme sage est puissant, et l’homme instruit est robuste et vigoureux.
Mutum mai hikima yana da iko sosai, kuma mutum mai sani yakan ƙaru da ƙarfi;
6 Parce que c’est avec réflexion que s’entreprend une guerre; et que le salut sera où il y a beaucoup de conseils.
don yin yaƙi kana bukatar bishewa, kuma don ka yi nasara kana bukatar mashawarta masu yawa.
7 Bien élevée est pour l’insensé la sagesse à la porte de la ville, il n’ouvrira pas la bouche.
Hikima ta yi wa wawa nisa ƙwarai a cikin taro a ƙofar gari ba shi da ta cewa.
8 Celui qui pense à faire le mal sera appelé insensé.
Duk mai ƙulla mugunta za a ɗauka shi mai kuta hargitsi ne.
9 La pensée de l’insensé est péché; et c’est l’abomination des hommes, que le médisant.
Makircin wawa zunubi ne, mutane kuma sukan yi ƙyamar mai ba’a.
10 Si, fatigué au jour de l’angoisse, tu désespères, ta force sera diminuée.
In ba ka da ƙarfi a lokacin wahala, ka tabbatar kai marar ƙarfi ne sosai!
11 Arrache au péril ceux qui sont conduits à la mort, et, ceux que l’on traîne à la destruction, ne cesse pas de les délivrer.
Ka kuɓutar da waɗanda ake ja zuwa inda za a kashe su; ka riƙe waɗanda suke tangaɗi zuwa wajen yanka.
12 Si tu dis: Les forces me manquent; celui qui observe le cœur le discerne lui-même, rien ne trompe le conservateur de ton âme; et il rendra à l’homme selon ses œuvres.
In kuka ce, “Ai, ba mu san wani abu a kai wannan ba,” shi da yake awon ba shi da zuciyar ganewa ne? Shi da yake tsare ranka bai sani ba ne? Ba zai sāka wa kowane mutum bisa ga abin da ya aikata ba?
13 Mange, mon fils, le miel, parce qu’il est bon, et le rayon doux à ton gosier.
Ka sha zuma, ɗana, ka sha zuma gama tana da kyau; zuma daga kaki yana da zaƙi a harshenka.
14 Telle est la doctrine de la sagesse à ton âme: quand tu l’auras trouvée, tu auras à tes derniers moments l’espérance et ton espérance ne périra pas.
Ka kuma san cewa hikima tana da zaƙi ga rai; in ka same ta, akwai sa zuciya ta nan gaba dominka, kuma sa zuciyarka ba za tă zama a banza ba.
15 Ne dresse pas d’embûches, et ne cherche pas l’impiété dans la maison du juste, et ne détruis pas son repos.
Kada ka kwanta kana fako kamar ɗan iska don ƙwace gidan adali, kada ka ƙwace masa wurin zama;
16 Car le juste tombera sept fois et se relèvera; mais les impies seront abattus dans le malheur.
gama ko da adali ya fāɗi sau bakwai, yakan tashi kuma, amma bala’i kan kwantar da mugaye.
17 Lorsque ton ennemi sera tombé, ne Le réjouis pas: et qu’à sa ruine ton cœur n’exulte pas;
Kada ka yi dariya sa’ad da abokin gāba ya fāɗi; sa’ad da ya yi tuntuɓe, kada ka yi farin ciki,
18 De peur que le Seigneur ne le voie, et que cela ne lui déplaise; et qu’il ne retire de lui sa colère.
in ba haka ba in Ubangiji ya gani ba zai amince ba ya kuma juye fushinsa daga gare shi.
19 Ne dispute pas avec les hommes très méchants; et ne porte pas envie aux impies;
Kada ka ji tsoro saboda masu mugunta ko ka yi ƙyashin mugaye,
20 Parce qu’ils n’ont pas l’espérance des choses futures, les méchants, et que la lampe des impies s’éteindra.
gama mugu ba shi da zuciya ta nan gaba, kuma fitilar mugaye za tă mutu.
21 Crains, mon fils, le Seigneur et le roi, et ne te lie pas avec les médisants;
Ka ji tsoron Ubangiji da kuma sarki, ɗana, kuma kada ka haɗa kai da masu tayarwa,
22 Parce que tout à coup s’élèvera leur perte, et la ruine de l’un et de l’autre, qui la connaît?
gama za a tura waɗannan biyu zuwa hallaka nan da nan, kuma wa ya sani irin bala’in da za su iya kawowa?
23 Voici aussi pour les sages: Faire acception de la personne dans le jugement n’est pas bon.
Waɗannan ma maganganun masu hikima ne, Nunan sonkai a shari’a ba shi da kyau.
24 Quant à ceux qui disent à l’impie: Tu es juste; les peuples les maudiront et les tribus les détesteront.
Duk wanda ya ce wa mai laifi, “Ba ka da laifi”, mutane za su la’ance shi al’umma kuma za tă ce ba a san shi ba.
25 Ceux qui le reprennent seront loués; et sur eux viendra la bénédiction.
Amma zai zama da lafiya ga duk waɗanda suka hukunta masu laifi, kuma babban albarka zai zo a kansu.
26 Il baisera les lèvres, celui qui répond des paroles droites.
Amsa da take ta gaskiya tana kamar sumba a leɓuna.
27 Prépare au dehors ton œuvre, et avec soin cultive ton champ; afin qu’ensuite tu bâtisses ta maison.
Ka gama aikinka ka kuma shirya gonakinka; bayan haka, ka gina gidanka.
28 Ne sois pas témoin sans raison contre ton prochain; et ne séduis personne par tes lèvres.
Kada ka ba da shaida a kan maƙwabcinka ba tare da isashen dalili ba, ko ka yi amfani da leɓunanka ka yi ruɗu.
29 Ne dis pas: Comme il m’a fait, ainsi je lui ferai: je rendrai à chacun selon son œuvre.
Kada ka ce, “Zan yi masa kamar yadda ya yi mini; zan rama abin da wannan mutum ya yi mini.”
30 J’ai passé dans le champ du paresseux, et par la vigne de l’insensé:
Na wuce cikin gonar rago, na wuce cikin gonar inabin mutumin da ba shi da azanci;
31 Et voilà que tout était rempli d’orties; et que les épines en avaient couvert la surface, et que la muraille de pierres était détruite.
ƙayayyuwa sun yi girma ko’ina, ciyayi sun rufe ƙasar, katangar duwatsu duk ta rushe.
32 Ce qu’ayant vu, je l’ai mis dans mon cœur, et par cet exemple je me suis instruit.
Na yi tunani a zuciyata na kuwa koyi darasi daga abin da na gani.
33 Tu dormiras un peu, dis-je, tu sommeilleras modérément, tu mettras faiblement les mains l’une dans l’autre, afin que tu reposes:
Ɗan barci, ɗan gyangyaɗi, ɗan naɗin hannuwa don a huta,
34 Et viendra à toi, comme un coureur, la détresse; et la mendicité, comme un homme armé.
sai talauci ya shigo maka kamar’yan fashi rashi kuma ya zo maka kamar mai hari.