< Proverbes 20 >
1 C’est une chose luxurieuse que le vin; et l’ivresse est tumultueuse: quiconque y met son plaisir ne sera pas sage.
Ruwan inabi mai yin ba’a ne, barasa kuma mai rikici ne; duk wanda suka sa ya kauce marar hikima ne.
2 Comme le rugissement du lion, ainsi est la terreur du roi: celui qui le provoque pèche contre son âme.
Fushin sarki yana kama da rurin zaki; duk wanda ya sa shi fushi zai rasa ransa.
3 C’est un honneur pour l’homme, de se séparer des contestations; mais tous les insensés s’immiscent dans des affaires ignominieuses.
Bangirma ne ga mutum ya guji faɗa, amma kowane wawa yana saurin yin faɗa.
4 À cause du froid, le paresseux n’a pas voulu labourer; il mendiera donc pendant l’été, et il ne lui sera rien donné.
Rago ba ya noma a lokacin noma; saboda haka a lokacin girbi ba ya bukata samun kome.
5 Comme une eau profonde, ainsi est le conseil dans le cœur de l’homme; mais l’homme sage l’épuisera.
Manufofin zuciyar mutum zurfafan ruwaye ne, amma mutum mai basira yakan jawo su.
6 Beaucoup d’hommes sont appelés miséricordieux; mais un homme fidèle, qui le trouvera?
Kowane mutum gani yake shi mai ƙauna marar ƙarewa ne, amma ina? Da ƙyar ka sami amintacce mutum guda.
7 Le juste qui marche dans sa simplicité laissera après lui des enfants bienheureux.
Mai adalci kan yi rayuwa marar abin zargi; masu albarka ne’ya’yan da za su biyo bayansa.
8 Le roi qui est assis sur le trône de la justice dissipe tout le mal par son regard.
Sa’ad da sarki ya zauna kan kujerarsa don yă yi shari’a, yakan ga dukan mugunta da idanunsa.
9 Qui peut dire: Mon cœur est pur, je suis pur de péché?
Wa zai iya cewa, “Na kiyaye zuciyata da tsarki; ni mai tsabta ne marar zunubi kuma”?
10 Un poids et un poids, une mesure et une mesure, l’un et l’autre sont abominables auprès de Dieu.
Ma’auni marar gaskiya da magwajin da ba daidai ba, Ubangiji ya ƙi su duka.
11 Par ses inclinations un enfant est connu: si ses œuvres sont pures et droites.
Akan san ƙananan yara ta ayyukansu, ana iya sani ko rayuwarsu amintattu ne, mai nagarta.
12 L’oreille qui entend et l’œil qui voit, le Seigneur a fait l’un et l’autre.
Kunnuwan da suke ji da kuma idanun da suke gani, Ubangiji ne ya yi su duka.
13 N’aime pas le sommeil, de peur que la détresse ne t’accable; ouvre les yeux et rassasie-toi de pain.
Kada ka so barci in ba haka ba za ka talauce; ka zauna a faɗake za ka kuwa kasance da sauran abinci.
14 C’est mauvais, c’est mauvais, dit tout acheteur; et après qu’il se sera retiré, alors il se glorifiera.
“Kai, ya yi tsada, ya yi tsada!” In ji mai saya; sa’ad da ya tafi yana taƙama a kan ya iya ciniki.
15 Il y a de l’or et une multitude de pierreries; mais c’est un vase précieux que les lèvres savantes.
Zinariya akwai ta, lu’ulu’u kuma ga shi a yalwace, amma leɓunan da suke magana da sani suna da wuyan samu kamar duwatsu masu daraja.
16 Prends le vêtement de celui qui s’est fait caution pour un étranger; et parce qu’il a répondu pour des étrangers, emporte un gage de lui.
A karɓi rigunan wanda ya ɗauki lamunin baƙo; a riƙe shi jingina in ya yi shi don mace marar aminci.
17 Un pain de mensonge est doux à l’homme; mais, ensuite, sa bouche sera remplie de gravier.
Abincin da aka samu ta hanyar zamba yakan zama da daɗi, amma mutum zai ƙarasa da baki cike da yashi.
18 Les pensées s’affermissent par les conseils, et c’est par de sages directions que doivent être conduites les guerres.
Ka yi shirye-shirye ta wurin neman shawara; in kana yaƙi, ka sami bishewa.
19 Quant à celui qui révèle les secrets, qui marche frauduleusement, et qui dilate ses lèvres, ne te lie pas avec lui.
Mai gulma yakan lalace yarda; saboda haka ka guji mutum mai yawan surutu.
20 Celui qui maudit son père et sa mère, sa lampe s’éteindra au milieu des ténèbres.
In mutum ya zargi mahaifinsa ko mahaifiyarsa, fitilarsa za tă mutu a tsakiyar duhu.
21 L’héritage vers lequel on se précipite dès le premier instant sera à la fin privé de bénédiction.
Gādon da aka samu da sauri a farkon farawa ba zai zama mai albarka a ƙarshe ba.
22 Ne dis point: Je rendrai le mal; attends le Seigneur, et il te délivrera.
Kada ka ce, “Zan rama wannan abin da aka yi mini!” Ka dogara ga Ubangiji, zai kuwa fisshe ka.
23 C’est une abomination auprès du Seigneur, qu’un poids et un poids: la balance trompeuse n’est pas bonne.
Ubangiji ya ƙi ma’aunin da ba daidai ba, da kuma magwajin da ba su gamshe shi ba.
24 Par le Seigneur sont dirigés les pas de l’homme; mais qui des hommes peut comprendre sa voie?
Ubangiji ne yake bi da matakan mutum, Ta yaya wani zai fahimci hanyarsa?
25 C’est une ruine pour l’homme de dévorer les saints, et après des vœux, de se rétracter.
Tarko ne ga mutum ya keɓe wani abu da ba tunani daga baya kuma ya yi la’akari da alkawarinsa.
26 Un roi sage dissipe les impies, et courbe sur eux un arc de triomphe.
Sarki mai hikima yakan gane mugunta; ya hukunta su ba tausayi.
27 Le souffle de l’homme est une lampe du Seigneur, laquelle découvre les parties intimes du corps.
Fitilar Ubangiji kan bincika zuciyar mutum takan bincika lamirinsa.
28 La miséricorde et la vérité gardent le roi, et par la clémence est affermi son trône.
Ƙauna da aminci kan kiyaye sarki lafiya; ta wurin ƙauna sarautarsa za tă zauna a kafe.
29 La joie des jeunes hommes, c’est leur force; et la dignité des vieillards, les cheveux blancs.
Ɗaukakar matasa maza ita ce ƙarfinsu, furfura ita ce darajar tsofaffi.
30 La lividité d’une blessure fera disparaître le mal; et les plaies dans les parties les plus intimes du corps le feront disparaître aussi.
Naushi da rauni kan share mugunta, dūka kuma kan tsabtacce lamiri.