< Nombres 34 >

1 Le Seigneur parla encore à Moïse, disant:
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Ordonne aux enfants d’Israël, et tu leur diras: Lorsque vous serez entrés dans la terre de Chanaan, et qu’elle vous sera échue en possession par le sort, c’est par ces frontières qu’elle sera bornée:
“Ka umarci Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka shiga Kan’ana, ƙasar da aka ba ku gādo za tă kasance da waɗannan iyakoki.
3 La partie méridionale commencera au désert de Sin, qui est près d’Edom; et elle aura pour frontière vers l’orient la mer très salée;
“‘Gefenku na kudu zai haɗa da wani sashin Hamadan Zin ta iyakar Edom. A gabas, iyakarku ta kudu za tă fara daga ƙarshen Tekun Gishiri,
4 Ces frontières environneront la partie australe par la montée du Scorpion, en sorte qu’elles passent à Senna, et qu’elles viennent depuis le midi jusqu’à Cadesbarné, d’où elles iront par les lieux limitrophes jusqu’au village du nom d’Adar, et s’étendront jusqu’à Asémona;
tă ƙetare Mashigin Kunama a kudu, tă ci gaba zuwa Zin, sa’an nan tă nufi kudu da Kadesh Barneya. Sa’an nan za tă zarce zuwa Hazar Addar, tă nausa zuwa Azmon,
5 Puis la limite ira en tournant d’Asémona jusqu’au torrent d’Egypte, et elle finira au rivage de la grande mer.
inda za tă juya tă haɗu da Rafin Masar, tă kuma ƙarasa a Bahar Rum.
6 Mais la partie occidentale commencera à la grande mer, et sera fermée par cette limite même.
“‘Iyakarku a yammanci, za tă kasance bakin Bahar Rum. Wannan ce za tă zama iyakarku a yamma.
7 Or, vers la partie septentrionale, les limites commenceront à la grande mer, parvenant jusqu’à la très haute montagne,
“‘Iyakarku a arewanci kuwa za tă tashi daga Bahar Rum zuwa Dutsen Hor,
8 De laquelle elles viendront à Emath jusqu’aux confins de Sédada;
za tă kuma tashi daga Dutsen Hor, zuwa Lebo Hamat. Sa’an nan tă miƙe zuwa Zedad,
9 Puis, elles iront par les lieux limitrophes jusqu’à Zéphrona, et au village d’Enan. Telles seront les limites dans la partie de l’aquilon.
tă ci gaba zuwa Zifron, sa’an nan tă ƙarasa a Hazar-Enan. Wannan ce za tă zama iyakarku a arewa.
10 De là les frontières se mesureront contre la partie orientale, depuis le village d’Enan jusqu’à Séphama;
“‘Iyakarku a gabashi, za tă tashi daga Hazar-Enan zuwa Shefam.
11 Et de Séphama, les limites descendront à Rébla, contre la fontaine de Daphnim: de là elles parviendront contre l’orient à la mer de Cénéreth,
Iyakar za tă gangara daga Shefam zuwa Ribla a gefen gabashin Ayin, sa’an nan tă ci gaba a gangaren gabashin Tekun Kinneret.
12 S’étendront jusqu’au Jourdain, et enfin seront fermées par la mer très salée. C’est cette terre que vous aurez selon ses frontières dans son contour.
Sa’an nan tă gangara ta Urdun, tă ƙarasa a Tekun Gishiri. “‘Wannan za tă zama ƙasarku, tare da iyakokinta a kowane gefe.’”
13 Moïse ordonna donc aux enfants d’Israël, disant: Ce sera la terre que vous posséderez par le sort, et que le Seigneur a commandé qu’on donnât aux neuf tribus et à la demi-tribu.
Sai Musa ya umarci Isra’ilawa ya ce, “Ku raba wannan ƙasa da za ku gāda ta hanyar jefa ƙuri’a. Ubangiji ya umarta cewa a ba da ita ga kabilu tara da rabi,
14 Car la tribu des enfants de Ruben, selon ses familles, et la tribu des enfants de Gad, selon le nombre de sa parenté, et aussi la demi-tribu de Manassé,
saboda iyalan kabilar Ruben, kabilar Gad da rabin kabilar Manasse sun riga sun sami gādonsu.
15 C’est-à-dire deux tribus et demie, ont reçu leur part au-delà du Jourdain, contre Jéricho, à la partie orientale.
Waɗannan kabilu biyu da rabi, sun sami gādonsu a wancan hayin Urdun a gabashin Yeriko wajen fitowar rana.”
16 Le Seigneur dit aussi à Moïse:
Ubangiji ya ce wa Musa,
17 Voici les noms des hommes qui vous partageront la terre: Eléazar, le prêtre, et Josué, fils de Nun,
“Waɗannan su ne sunayen mutanen da za su raba muku ƙasar gādo. Eleyazar firist, da Yoshuwa ɗan Nun.
18 Et chaque prince de chaque tribu,
Ka kuma naɗa shugaba guda ɗaya daga kowace kabila domin yă taimaka a rabon ƙasar.
19 Dont voici les noms: De la tribu de Juda, Caleb, fils de Jéphoné;
“Ga sunayensu. “Kaleb ɗan Yefunne, daga kabilar Yahuda;
20 De la tribu de Siméon, Samuel, fils d’Ammiud;
Shemuyel ɗan Ammihud, daga kabilar Simeyon
21 De la tribu de Benjamin, Elidad, fils de Chasélon;
Elidad ɗan Kislon, daga kabilar Benyamin;
22 De la tribu des enfants de Dan, Bocci, fils de Jogli;
Bukki ɗan Yogli, shugaba daga kabilar Dan;
23 Des enfants de Joseph: de la tribu de Manassé, Hanniel, fils d’Ephod;
Hanniyel ɗan Efod, shugaba daga kabilar Manasse ɗan Yusuf;
24 De la tribu d’Ephraïm, Camuel, fils de Sephtan;
Kemuwel ɗan Shiftan, shugaba daga kabilar Efraim ɗan Yusuf;
25 De la tribu de Zabulon, Elisaphan, fils de Pharnach;
Elizafan ɗan Farnak, shugaba daga kabilar Zebulun;
26 De la tribu d’Issachar, le chef Phaltiel, fils d’Ozan;
Faltiyel ɗan Azzan, shugaba daga kabilar Issakar;
27 De la tribu d’Aser, Ahiud, fils de Salomi:
Ahihud ɗan Shelomi, shugaba daga kabilar Asher;
28 De la tribu de Nephthali, Phédaël, fils d’Ammiud.
Fedahel ɗan Ammihud, shugaba daga kabilar Naftali.”
29 Tels sont ceux auxquels le Seigneur ordonna de partager aux enfants d’Israël la terre de Chanaan.
Waɗannan su ne mutanen da Ubangiji ya umarta su raba gādo ga Isra’ilawa a ƙasar Kan’ana.

< Nombres 34 >