< Nombres 25 >

1 Or, en ce temps-là Israël demeurait à Settim, et le peuple forniqua avec les filles de Moab,
Lokacin da Isra’ila suke a sansani a Shittim, sai maza suka fara yin lalata da matan Mowabawa,
2 Qui les appelèrent à leurs sacrifices; et eux en mangèrent et ils adorèrent leurs dieux,
waɗanda suka gayyace su zuwa wajen hadayu na allolinsu. Mutane suka ci suka kuma yi wa waɗannan alloli sujada.
3 Et Israël fut initié au culte de Béelphégor; et le Seigneur irrité,
Ta haka Isra’ila suka sa kai a bautar gumaka Ba’al-Feyor. Ubangiji kuwa ya husata da su.
4 Dit à Moïse: Prends tous les princes du peuple, et suspends-les à des potences à la face du soleil, afin que ma fureur se détourne d’Israël.
Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka kama dukan shugabannin mutanen nan, ka kashe su, ka kuma bar su a tsakar rana a gaban Ubangiji, don Ubangiji yă huce daga fushin da nake yi da Isra’ila.”
5 Moïse dit donc aux juges d’Israël: Que chacun tue ses proches, qui ont été initiés au culte de Béelphégor.
Saboda haka Musa ya ce wa alƙalan Isra’ila, “Dole kowannenku yă kashe mutanen nan da suka haɗa kai cikin bautar Ba’al-Feyor.”
6 Et voilà qu’un des enfants d’Israël entra devant ses frères chez une prostituée madianite, Moïse le voyant, ainsi que toute la multitude des enfants d’Israël, qui pleuraient devant la porte du tabernacle.
Sa’an nan wani mutumin Isra’ila ya kawo wata Bamidiyana a iyalinsa a idon Musa da dukan taron jama’ar Isra’ila, yayinda suke kuka a ƙofar Tentin Sujada.
7 Ce qu’ayant vu Phinéès, fils d’Eléazar, fils d’Aaron, le prêtre, il se leva du milieu de la multitude, et, un poignard pris,
Da Finehas ɗan Eleyazar, ɗan Haruna, firist, ya ga haka, sai ya bar taron, ya ɗauki māshi
8 Il entra après l’Israélite, dans la tente de prostitution, perça tous deux, c’est-à-dire l’homme et la femme dans les parties secrètes: et la plaie fut détournée des enfants d’Israël;
ya bi mutumin Isra’ilan nan cikin tenti, ya soke dukansu biyu, māshin ya ratsa jikin mutumin Isra’ilan har zuwa jikin macen. Sa’an nan aka tsai da annoban nan a kan Isra’ilawa.
9 Or, vingt-quatre mille hommes furent tués.
Waɗanda suka mutu a wannan annoba, sun kai mutum 24,000.
10 Et le Seigneur dit à Moïse:
Ubangiji ya ce wa Musa,
11 Phinéès, fils d’Eléazar, fils d’Aaron, le prêtre, a détourné ma colère des enfants d’Israël, parce qu’il a été animé de mon zèle contre eux, afin que moi-même je ne détruisisse point les enfants d’Israël dans mon zèle.
“Finehas ɗan Eleyazar, ɗan Haruna, firist, ya kawar da fushina daga Isra’ilawa; saboda ya yi kishi irin nawa a gabansu, don haka saboda ɗaukakata ban kawo ƙarshensu ba.
12 C’est pourquoi dis-lui: Voici que je lui donne la paix de mon alliance;
Saboda haka ka faɗa masa cewa zan yi alkawarin salama da shi.
13 Et ce sera tant pour lui que pour sa postérité un pacte perpétuel de sacerdoce, parce qu’il a été zélé pour son Dieu, et qu’il a expié le crime des enfants d’Israël.
Shi da zuriyarsa za su kasance da alkawari na zama firist har abada, saboda kishinsa domin ɗaukakar Allahnsa, ya kuma yi kafara domin Isra’ilawa.”
14 Or le nom de l’homme Israélite, qui fut tué avec la Madianite, était Zambri, fils de Salu, chef de la parenté et de la tribu de Siméon.
Sunan mutumin Isra’ilan da aka kashe tare da macen nan Bamidiyana kuwa Zimri ne, ɗan Salu, shugaban mutanen Simeyon.
15 Et la femme madianite qui pareillement fut tuée, s’appelait Cozbi, fille de Sur, prince très noble des Madianites.
Sunan macen nan Bamidiyana da aka kashe kuwa Kozbi ne,’yar Zur, wani basaraken iyalin Midiyawa.
16 Le Seigneur parla encore à Moïse, disant:
Ubangiji ya ce wa Musa,
17 Que les Madianites sentent que vous êtes leurs ennemis, et frappez-les,
“Ka ɗauki Midiyawa a matsayin abokan gāba, ka kuma kashe su,
18 Parce qu’eux-mêmes aussi vous ont traités hostilement, et vous ont trompés insidieusement par l’idole de Phogor, et par Cozbi, fille du chef de Madian, leur sœur, qui fut frappée au jour de la plaie, à cause du sacrilège de Phogor.
gama sun ɗauke ku a matsayin abokan gāba, sa’ad da suka ruɗe ku a kan al’amuran Feyor da’yar’uwarsu Kozbi’yar shugaban Midiyawa, macen da aka kashe a annoba ta dalili Feyor.”

< Nombres 25 >