< Nombres 19 >

1 Le Seigneur parla encore à Moïse et à Aaron, disant:
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
2 Voici la cérémonie de la victime qu’a déterminée le Seigneur. Ordonne aux enfants d’Israël qu’ils t’amènent une vache rousse, dans l’intégrité de l’âge, en laquelle il n’y ait aucune tache, et qui n’ait point porté le joug;
“Wannan ita ce ƙa’ida wadda Ubangiji ya umarta. Faɗa wa Isra’ilawa su kawo maka jan karsana marar lahani, ko marar aibi wadda ba a taɓa sa ta tă yi noma ba.
3 Et vous la livrerez à Eléazar, le prêtre, qui après l’avoir menée hors du camp, l’immolera en présence de tous;
Ka ba wa Eleyazar firist; a kuma kai ta bayan sansani, a yanka a gaban Eleyazar.
4 Et, trempant le doigt dans son sang, il fera l’aspersion contre la porte du tabernacle par sept fois.
Sa’an nan Eleyazar firist zai ɗiba jininta a yatsarsa, yă yayyafa sau bakwai wajen gaban Tentin Sujada.
5 Puis il la brûlera, tous le voyant, en livrant aux flammes tant sa peau et sa chair, que son sang et sa fiente.
Sa’an nan a ƙone dukan karsanar, haɗe da fatarta, naman, jinin da kayan cikin, yayinda Eleyazar yake kallo.
6 Le prêtre jettera aussi du bois de cèdre, de l’hysope et de l’écarlate deux fois teinte, dans la flamme qui brûle la vache.
Firist zai ɗauki itacen al’ul, da hizzob, da jan ulu, yă jefa su a kan karsanar da ake ƙonewa.
7 Et alors enfin, ses vêtements et son corps lavés, il entrera dans le camp et il sera souillé jusqu’au soir.
Bayan haka, dole firist yă wanke rigunarsa, yă kuma yi wanka. Sa’an nan zai iya shiga cikin sansani, amma zai kasance da ƙazanta har yamma.
8 Mais celui aussi qui l’aura brûlée, lavera ses vêtements et son corps, et il sera impur jusqu’au soir.
Dole mutumin da ya ƙone ta yă wanke rigunarsa, yă kuma yi wanka, shi ma zai kasance da ƙazanta har yamma.
9 Et un homme pur recueillera les cendres de la vache, et les déposera hors du camp dans un lieu très net, afin qu’elles soient à la garde de la multitude des enfants d’Israël, et qu’elles servent pour une eau d’aspersion; parce que c’est pour le péché que la vache a été brûlée.
“Mutumin da yake da tsarki, zai tara tokar karsanar, yă sa ta a wurin da yake da tsabta a bayan sansani. Jama’ar Isra’ilawa ne za su adana shi don amfani a ruwan tsabtaccewa; wannan domin tsarkakewa ne daga zunubi.
10 Et lorsque celui qui avait porté les cendres de la vache, aura lavé ses vêtements, il sera impur jusqu’au soir. Les enfants d’Israël et les étrangers qui habitent parmi eux tiendront cette ordonnance pour sainte par un droit perpétuel.
Dole mutumin da ya tara tokar karsanar yă wanke rigunarsa, zai kuwa kasance da ƙazanta har yamma. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ta har abada ga Isra’ilawa, da kuma baƙin da suke zama a cikinsu.
11 Celui qui aura touché le cadavre d’un homme, et qui pour cela sera impur pendant sept jours,
“Duk wanda ya taɓa gawa, zai kasance da ƙazanta har kwana bakwai.
12 Sera aspergé de cette eau au troisième et au septième jour, et c’est ainsi qu’il sera purifié. Si au troisième jour il n’a pas été aspergé, au septième il ne pourra être purifié.
Dole yă tsarkake kansa da ruwa a rana ta uku, da kuma a rana ta bakwai; sa’an nan zai zama da tsarki. Amma in bai tsarkake kansa a rana ta uku da kuma a rana ta bakwai ba, ba zai kasance da tsarki ba.
13 Quiconque aura touché le corps mort du ne âme humaine, et n’aura pas été aspergé de cette eau ainsi mêlée, souillera le tabernacle du Seigneur, et périra du milieu d’Israël: parce qu’il n’a pas été aspergé d’eau d’expiation, il sera impur et son impureté demeurera sur lui.
Duk wanda ya taɓa gawar wani, bai kuma tsarkake kansa ba, ya ƙazantar da tabanakul na Ubangiji ke nan. Dole a ware wannan mutum daga cikin Isra’ilawa. Gama ba a yayyafa ruwan tsabtaccewa a kansa ba; ya ƙazantu, ya kasance da ƙazanta ke nan.
14 Voici la loi de l’homme qui meurt dans une tente: Tous ceux qui entrent dans sa tente, et tous les vases qui y sont, seront souillés pendant sept jours.
“Ga ƙa’idar da za a bi in mutum ya mutu a cikin tenti. Duk wanda ya shiga tentin, kuma duk wanda yake cikinsa, za su zama da ƙazanta har kwana bakwai,
15 Un vase qui n’aurait point de couvercle, ni d’attache par-dessus, sera impur.
kuma kowane abin da ake zuba kaya, wanda ba shi da murfi a kansa, zai zama da ƙazanta.
16 Si quelqu’un dans un champ touche le cadavre d’un homme tué, ou mort de lui-même, ou bien un de ses os, ou son sépulcre, il sera impur pendant sept jours.
“Wanda duk yake a fili, ya kuma taɓa gawa wanda aka kashe da takobi, ko wanda ya mutu mutuwar Allah, ko ƙashin mutum, ko kabari, zai ƙazantu har bakwai.
17 On prendra des cendres de la combustion et du péché, et l’on mettra de l’eau vive sur ces cendres dans un vase;
“Ga wanda ya ƙazantu kuwa, a ɗiba toka daga hadaya ta ƙonawa ta tsarkakewa, a zuba a cikin tulu, sa’an nan a zuba ruwa mai gudu a kansu.
18 Et un homme pur y ayant trempé de l’hysope, il en aspergera toute la tente, tous les meubles et tous les hommes souillés par un tel contact
Sa’an nan wanda yake tsarkakakke, zai ɗauki hizzob yă tsoma a ruwa, yă yayyafa a tentin da dukan kayayyakinsa, da kuma a kan mutanen da suke wurin. Dole kuma yă yayyafa ruwan a kan duk wanda ya taɓa ƙashin mutu, ko kabari, ko kuma wanda aka kashe, ko wanda ya yi mutuwa ta Allah.
19 Et de cette manière le pur purifiera l’impur au troisième et au septième jour; et celui qui aura été purifié au septième jour, se lavera, lui et ses vêtements, et il sera impur jusqu’au soir.
A rana ta uku, da ta bakwai kuma mai tsarkakewa zai yayyafa wa marar tsarkin ruwa, a rana ta bakwai kuma yă tsarkake shi. Wanda aka tsarkaken kuwa, dole yă wanke rigunarsa, yă kuma yi wanka da yamma, zai kuma tsarkaka.
20 Si quelqu’un n’est pas purifié selon ce rite, son âme périra du milieu de l’assemblée, parce qu’il a souillé le sanctuaire du Seigneur, et qu’il n’a pas été aspergé d’eau de purification.
Amma in wanda yake da ƙazanta bai tsarkake kansa ba, dole a ware shi daga cikin jama’a, domin ya ƙazantar da wuri mai tsarki na Ubangiji. Ba a yayyafa masa ruwa na tsarkakewa ba, ya zama da ƙazanta.
21 Cette ordonnance sera une loi perpétuelle. Celui aussi qui aura fait les aspersions de l’eau, lavera ses vêtements. Quiconque aura touché l’eau de l’expiation sera impur jusqu’au soir.
Wannan za tă zama musu dawwammamiyar farilla. “Mutumin da ya yayyafa ruwa na tsarkakewa, shi ma dole yă wanke rigarsa. Duk wanda kuma ya taɓa ruwan tsarkakewa, zai kasance da ƙazanta har yamma.
22 Tout ce que touchera un impur, il le rendra impur: et l’homme qui touchera quelqu’une de ces choses, sera impur jusqu’au soir.
Duk abin da mai ƙazanta ya taɓa, ya ƙazantu, kowa kuma ya taɓa wannan abu, ya ƙazantu ke nan, har yamma.”

< Nombres 19 >