< Néhémie 11 >
1 Or les princes du peuple habitèrent dans Jérusalem; mais le reste du peuple jeta le sort, afin que l’on prît une partie sur dix, laquelle devait habiter dans Jérusalem, la ville sainte, mais les neuf autres parties dans les autres villes.
To, fa, shugabannin mutane suka zauna a Urushalima, sauran mutanen kuma suka jefa ƙuri’a don su kawo mutum ɗaya daga kowane mutum goma don su zauna a Urushalima, birni mai tsarki, yayinda sauran tara suka zauna a garuruwansu.
2 Et le peuple bénit tous les hommes qui s’étaient spontanément offerts pour habiter dans Jérusalem.
Sai mutane suka yaba wa dukan mutanen da suka ba da kansu da yardar rai su zauna a Urushalima.
3 Voici donc les princes de la province qui habitèrent dans Jérusalem et dans les villes de Juda. Or chacun habita dans sa possession, dans ses villes, Israël, les prêtres, les Lévites, les Nathinéens, et les fils des serviteurs de Salomon.
Waɗannan su ne shugabannin yankuna waɗanda suka zauna a Urushalima (ko da yake waɗansu Isra’ilawa, da firistoci, da Lawiyawa, da ma’aikatan haikali, da zuriyar bayin Solomon, suka yi zama a cikin garuruwan Yahuda, kowanne a mallakarsa cikin garuruwa dabam-dabam,
4 Ainsi habitèrent dans Jérusalem des fils de Juda et des fils de Benjamin. D’entre les fils de Juda, Athaïas, fils d’Aziam, fils de Zacharie, fils d’Amarias, fils de Saphatias, fils de Malaléel. D’entre les fils de Pharès,
yayinda sauran mutane daga Yahuda da Benyamin suka zauna a Urushalima). Daga zuriyar Yahuda akwai, Atahiya ɗan Uzziya, ɗan Zakariya, ɗan Amariya, ɗan Shefatiya, ɗan Mahalalel, wani zuriyar Ferez;
5 Maasia, fils de Baruch, fils de Cholhoza, fils d’Hazia, fils d’Adaïa, fils de Joïarib, fils de Zacharie, fils du Silonite.
da Ma’asehiya ɗan Baruk, ɗan Kol-Hoze, ɗan Hazahiya, ɗan Adahiya, ɗan Yohiyarib, ɗan Zakariya, zuriyar Shela.
6 Tous ces fils de Pharès, qui habitèrent dans Jérusalem, étaient quatre cent soixante-huit hommes vaillants.
Zuriyar Ferez waɗanda suka zauna a Urushalima sun kai ɗari huɗu da sittin da takwas, dukansu kuwa muhimman mutane ne.
7 Or voici les fils de Benjamin: Sellum, fils de Mosollam, fils de Joëd, fils de Phadaïa, fils de Colaïa, fils de Masia, fils d’Éthéel, le fils d’Isaïe.
Daga zuriyar Benyamin akwai, Sallu ɗan Meshullam, ɗan Yowed, ɗan Fedahiya, ɗan Kolahiya, ɗan Ma’asehiya, ɗan Itiyel, ɗan Yeshahiya,
8 Et après lui Gebbaï, Sellaï: neuf cent vingt-huit.
da mabiyansa, Gabbai da Sallai, mutum 928.
9 Et Joël, fils de Zéchri, leur préposé, et Juda, fils de Sénua, le second sur la ville.
Yowel ɗan Zikri ne babban shugabansu, Yahuda kuma ɗan Hassenuwa, ya shugabanci Yanki na Biyu na birni.
10 Et d’entre les prêtres, Idaïa, fils de Joïarib, Jachin,
Daga firistoci akwai, Yedahiya ɗan Yohiyarib, da Yakin,
11 Saraïa, fils d’Helcias, fils de Mosollam, fils de Sadoc, fils de Méraïoth, fils d’Achitob, prince de la maison de Dieu,
da Serahiya ɗan Hilkiya, ɗan Meshullam, ɗan Zadok, ɗan Merahiyot, ɗan Ahitub, mai lura da abubuwa a cikin gidan Allah,
12 Et leurs frères, faisant les ouvrages du temple: huit cent vingt-deux. Et Adaïa, fils de Jéroham, fils de Phélélia, fils d’Amsi, fils de Zacharie, fils de Pheshur, fils de Melchias,
tare da’yan’uwansu waɗanda suke aiki domin haikali, su 822 ne. Akwai kuma Adahiya ɗan Yeroham, ɗan Felaliya, ɗan Amzi, ɗan Zakariya, ɗan Fashhur, ɗan Malkiya,
13 Et ses frères, les princes des pères: deux cent quarante-deux. Et Amassai, fils d’Azréel, fils d’Ahazi, fils de Mosollamoth, fils d’Emmer,
da’yan’uwansa waɗanda suke shugabannin iyalai, su 242. Sai kuma Amashsai ɗan Azarel, ɗan Ahzai, ɗan Meshillemot, ɗan Immer,
14 Et leurs frères, très puissants: cent vingt-huit, et leur préposé, Zabdée, fils des puissants.
da’yan’uwansa, su 128 ne muhimman mutane. Babban shugabansu shi ne Zabdiyel ɗan Haggedolim.
15 Et d’entre les Lévites, Séméia, fils d’Hasub, fils d’Azaricam, fils d’Hasabia, fils de Boni,
Daga Lawiyawa kuwa akwai, Shemahiya ɗan Hasshub, ɗan Azrikam, ɗan Hashabiya, ɗan Bunni,
16 Et Sabathaï et Jozabed établis sur tous les ouvrages qui se faisaient au dehors à la maison de Dieu, étant d’entre les princes des Lévites,
da Shabbetai, da kuma Yozabad, biyu cikin shugabanni Lawiyawa waɗanda suke da nawayar aiki waje da gidan Allah.
17 Et Mathania, fils de Micha, fils de Zébédéi, fils d’Asaph, prince pour louer et glorifier le Seigneur dans la prière; et Becbécia, le second d’entre ses frères, et Abda, fils de Samua, fils de Galal, fils d’Idithun.
Sai kuma Mattaniya ɗan Mika, ɗan Zabdi, ɗan Asaf, shugaban da yake bi da hidimar godiya da kuma addu’a. Sai Bakbukiya, na biyu a cikin’yan’uwansa; da Abda ɗan Shammuwa, ɗan Galal, ɗan Yedutun.
18 Tous les Lévites, dans la ville sainte, furent deux cent quatre-vingt-quatre.
Lawiyawan da suke cikin birni mai tsarki sun kai 284.
19 Et les portiers, Accub, Telmon, et leurs frères, qui gardaient les portes, cent soixante-douze.
Matsaran ƙofofi kuwa su ne, Akkub, da Talmon, da’yan’uwansu waɗanda suke tsaron ƙofofi, su 172 ne.
20 Et les autres d’Israël, les prêtres et les Lévites, étaient dans toutes les villes de Juda, chacun dans sa possession.
Sauran Isra’ilawa tare da firistoci, da Lawiyawa sun kasance a dukan garuruwan Yahuda, kowanne a mallakar kakansa.
21 Et les Nathinéens, qui habitaient dans Ophel; et Siaha et Gaspha étaient d’entre les Nathinéens.
Ma’aikatan haikali sun zauna a kan tudun Ofel. Ziha, da Gishfa ne suke lura da su.
22 Et le chef des Lévites à Jérusalem était Azzi, fils de Bani, fils de Hasabia, fils de Mathanias, fils de Micha. D’entre les fils d’Asaph étaient les chantres, dans le ministère de la maison de Dieu.
Babban shugaban Lawiyawa a Urushalima shi ne Uzzi ɗan Bani, ɗan Hashabiya, ɗan Mattaniya, ɗan Mika. Uzzi yana ɗaya daga zuriyar Asaf, waɗanda suke mawaƙan da suke da nawayar hidima a gidan Allah.
23 Car il y avait le commandement du roi à leur sujet, et un ordre observé parmi les chantres tous les jours.
Mawaƙa sun bi umarnan sarki, a kan abin da za su yi kowace rana.
24 Mais Phathahia, fils de Mésézebel, d’entre les fils de Zara, le fils de Juda, étaient sous la main du roi, pour toutes les affaires du peuple,
Fetahahiya ɗan Meshezabel, ɗaya daga zuriyar Zera ɗan Yahuda ne, wakilin sarki cikin dukan al’amuran da suka shafi mutane.
25 Et pour les maisons dans toutes leurs contrées. Des fils de Juda habitèrent à Cariatharbé et en ses filles, à Dibon et en ses filles, à Cabséel et en ses bourgades,
Game da ƙauyukan da filayensu, waɗansu mutanen Yahuda suka zauna a Kiriyat Arba da ƙauyukanta, da Dibon da ƙauyukanta, da Yekabzeyel da ƙauyukanta.
26 À Jésué, à Molada, à Bethphaleth,
Akwai su kuma a Yeshuwa, da Molada, da Bet-Felet,
27 À Hasersual, à Bersabée et en ses filles,
da Hazar Shuwal, da Beyersheba da ƙauyukanta.
28 À Sicéleg, à Mochona et en ses filles,
Akwai su a Ziklag, da Mekona da ƙauyukanta.
29 À Remmon, à Saraa, à Jérimuth,
Suna nan kuma a En Rimmon, da Zora, da Yarmut,
30 À Zanoa, à Odollam et dans leurs villages, à Lachis et en ses contrées, à Azéca et en ses filles. Et ils demeurèrent à Bersabée jusqu’à la vallée d’Ennom;
da Zanowa, da Adullam da ƙauyukansu, da Lakish da gonakinta, da kuma Azeka da ƙauyukanta. Saboda haka sun yi zama tun daga Beyersheba har zuwa Kwarin Hinnom.
31 Mais les fils de Benjamin, depuis Géba, Mechmas, Haï, Béthel et ses filles,
Zuriyar mutanen Benyamin daga Geba sun zauna a Mikmash, da Aiya, da Betel da ƙauyukanta,
da Anatot, da Nob, da Ananiya,
da Hazor, da Rama, da Gittayim,
34 Hadid, Séboïm, Neballat, Lod,
da Hadid, da Zeboyim, da Neballat,
35 Et Ono, la vallée des Ouvriers.
da Lod, da Ono, da kuma a Kwarin Masu sana’a.
36 Et les Lévites avaient des portions de Juda et de Benjamin.
Waɗansu gundumomin Lawiyawan Yahuda sun zauna a Benyamin.