< Néhémie 1 >

1 Paroles de Néhémias, fils de Helchias. Et il arriva au mois de Casleu, en l’année vingtième, que j’étais dans le château de Suse.
Kalmomin Nehemiya ɗan Hakaliya. A cikin watan Kisleb a shekara ta ashirin, yayinda nake a fadar Shusha.
2 Et Hanani, un de mes frères, vint, lui et des hommes de Juda; et je les interrogeai sur ceux des Juifs, qui étaient restés de la captivité, et qui vivaient encore, et sur Jérusalem.
Hanani, ɗaya daga cikin’yan’uwana, ya zo daga Yahuda tare da waɗansu mutane. Na kuwa tambaye shi game da raguwar Yahudawan da suka tsira daga kwasan zuwa zaman bauta, da kuma game da Urushalima.
3 Et ils me répondirent: Ceux qui sont restés et qui ont été laissés de la captivité là dans la province, sont dans une grande affliction et dans l’opprobre; et le mur de Jérusalem est tombé, et ses portes ont été brûlées au feu.
Suka ce mini, “Waɗanda suka tsira daga kwasan zuwa zaman bauta da kuma suka komo cikin yankin suna cikin babban damuwa da wulaƙanci. An rushe katangar Urushalima aka kuma ƙone ƙofofin da wuta.”
4 Lorsque j’eus ouï de telles paroles, je m’assis, je pleurai, et je gémis durant plusieurs jours; je jeûnais, et je priais devant la face du Dieu du ciel.
Da na ji waɗannan abubuwa, sai na zauna na yi kuka. Na yi kwanaki ina makoki da azumi, na kuma yi addu’a a gaban Allah na sama.
5 Et je dis: Je vous prie. Seigneur, Dieu du ciel, fort, grand et terrible, qui gardez l’alliance et la miséricorde avec ceux qui vous aiment et qui gardent vos commandements,
Na ce, “Ya Ubangiji Allah na sama, Allah mai girma da mai banrazana, wanda yake kiyaye alkawarinsa na ƙauna da waɗanda suke ƙaunarsa, suke kuma yin biyayya da umarnansa,
6 Que vos oreilles deviennent attentives et vos yeux, ouverts pour en cendre la prière de votre serviteur, que je fais aujourd’hui devant vous, nuit et jour, pour les enfants d’Israël, vos serviteurs; et je confesse les péchés des enfants d’Israël, par lesquels ils ont péché contre vous: moi et la maison de mon père, nous avons péché.
ka sa kunne ka kuma buɗe idanunka ka ji addu’ar da bawanka yake yi a gabanka dare da rana saboda bayinka, mutanen Isra’ila. Na furta zunuban da mu Isra’ilawa, har da ni da kuma gidan mahaifina muka yi maka.
7 Nous avons été séduits par la vanité, et nous n’avons pas gardé votre commandement, vos cérémonies, et les ordonnances que vous avez prescrites à Moïse, votre serviteur.
Mun yi mugunta gare ka. Ba mu yi biyayya da umarnai, ƙa’idodi da kuma dokokin da ka ba wa bawanka Musa ba.
8 Souvenez-vous de la parole que vous avez confiée à Moïse, votre serviteur, disant: Lorsque vous aurez transgressé, moi je vous disperserai parmi les peuples:
“Ka tuna da umarnan da ka ba wa bawanka Musa, kana cewa, ‘In kun yi rashin aminci, zan warwatsar da ku a cikin al’ummai,
9 Et si vous revenez à moi, et que vous gardiez mes préceptes, et que vous les accomplissiez, quand même vous auriez été emmenés jusqu’aux extrémités du ciel, je vous rassemblerai de là, et je vous ramènerai au lieu que j’ai choisi pour que mon nom y habite.
amma in kuka dawo gare ni kuka kuma yi biyayya da umarnaina, to, ko mutanenku da aka kwasa zuwa zaman bauta suna can wuri mafi nisa, zan tattara su daga can in kawo su wurin da na zaɓa yă zama wurin zama don Sunana.’
10 Et ceux-ci sont vos serviteurs et votre peuple, que vous avez rachetés par votre grande force et par votre main puissante.
“Su bayinka ne da kuma mutanenka da ka fansa ta wurin ƙarfinka mai girma da kuma hannunka mai iko.
11 Je vous conjure, Seigneur, que votre oreille soit attentive à la prière de votre serviteur, et à la prière de vos serviteurs, qui veulent craindre votre nom; et dirigez votre serviteur aujourd’hui, et donnez-lui miséricorde devant cet homme: car moi j’étais l’échanson du roi.
Ya Ubangiji, ka kasa kunne ga addu’ar wannan bawanka da kuma ga addu’ar bayinka waɗanda suke farin cikin girmama sunanka. Ka ba wa bawanka nasara a yau ta wurinsa yă sami tagomashi a gaban wannan mutum.” Ni ne mai riƙon kwaf sarki.

< Néhémie 1 >