< Matthieu 20 >
1 Le royaume des cieux est semblable à un père de famille qui sortit de grand matin, afin de louer des ouvriers pour sa vigne.
Gama mulkin sama yana kama da wani mai gona, wanda ya fita da asuba ya nemi 'yan kwadago da za su yi aiki a gonarsa.
2 Or, convention faite avec les ouvriers d’un denier par jour, il les envoya à sa vigne.
Bayan sun shirya kudin da zai biya ma'aikata kimanin dinari daya a kowanne yini, sai ya aike su gonarsa suyi aiki.
3 Et étant sorti de nouveau, vers la troisième heure, il en vit d’autres qui se tenaient sur la place sans rien faire.
Misalin sa'a ta uku sai ya sake fita, sai ya ga wasu ma'aikata suna tsaye a bakin kasuwa, babu aiki.
4 Et il leur dit: Allez, vous aussi, à ma vigne, et ce qui sera juste, je vous le donnerai.
Sai ya ce masu, 'Kuzo kuyi aiki a gonar, duk abinda ya wajaba, zan ba ku,' Sai suka tafi su yi aikin.
5 Et ils y allèrent. Il sortit encore vers la sixième et la neuvième heure, et il fit la même chose.
Sai ya sake fita a sa'a ta shida ya kuma sake fita a sa'a ta tara, ya sake yin hakan din.
6 Enfin, vers la onzième heure, il sortit, et il en trouva d’autres qui étaient là, et il leur dit: Pourquoi êtes-vous ici, tout le jour, sans rien faire?
Ya kuma sake yin haka a sa'a ta sha daya, da ya fita sai ya ga wasu a tsaye da ba sa yin kome. Sai ya ce masu, 'Me yasa kuke tsaye ba ku yin kome dukan yini?'
7 Ils répondirent: Parce que personne ne nous a loués. Il leur dit: Allez, vous aussi, à ma vigne.
Sai suka ce masa, 'Ai babu wanda ya dauke mu aiki, shi yasa.' Sai ya ce masu, 'ku ma, kuje cikin gonar.
8 Or, lorsqu’il se fit soir, le maître de la vigne dit à son intendant: Appelle les ouvriers, et paye-les, en commençant par les derniers jusqu’aux premiers.
Da yamma ta yi, sai mai gonar ya ce wa manajansa, 'Ka kira ma'aikatan nan ka biya su hakkin su, amma ka fara da wadanda suka zo a karshe, zuwa na farkon.'
9 Ceux donc qui étaient venus vers la onzième heure s’étant approchés, reçurent chacun un denier.
Sa'adda wadanda suka fara aiki da yamma suka zo, an biya su daidai yadda ake biya a yini.
10 Or les premiers venant ensuite, pensèrent qu’ils devraient recevoir davantage; mais ils reçurent aussi chacun un denier.
Da wadanda suka fara aiki tun safe suka zo, suna tsammani za a ba su fiye da wadanda sun zo daga baya, amma aka ba kowannensu dinari daya.
11 Et en le recevant, ils murmuraient contre le père de famille,
Da suka karbi hakkinsu, suka yi gunaguni game da mai gonar.
12 Disant: Ces derniers ont travaillé une heure, et vous les traitez comme nous, qui avons porté le poids du jour et de la chaleur.
Suka ce, 'Wadannan da suka zo a karshe, sa'a guda ce kadai suka yi aiki, amma ka ba su daidai da mu, mu da muka yi fama da aiki cikin zafin rana.'
13 Mais, répondant à l’un d’eux, il dit: Mon ami, je ne te fais point de tort; n’es-tu pas convenu d’un denier avec moi?
Amma mai gonar ya amsa wa daya daga cikin su, ya ce, 'Aboki na, ban yi maku laifi ba. Ai mun shirya zan biya ku yadda ake biya a yini, ko ba haka ba?
14 Prends ce qui est à toi et va-t’en; je veux donner même à ce dernier autant qu’à toi.
Ku karbi abin da ke na ku, ku tafi. Ganin dama ta ne, in ba wadannan da suka zo a karshe daidai da ku.
15 Ne m’est-il pas permis de faire ce que je veux? et ton œil est-il mauvais parce que je suis bon?
Ashe, ba daidai bane a gare ni, in yi abin da na ga dama da mallaka ta? Ko kishi ne kuke yi saboda kirki na?'
16 Ainsi les derniers seront les premiers, et les premiers seront les derniers; car beaucoup sont appelés, mais peu sont élus.
Haka yake, na karshe za su zama na farko, na farko kuma su zama na karshe.'' [An kira dayawa, amma kadan ne zababbu].
17 Or Jésus montant à Jérusalem prit à part les douze disciples et leur dit:
Da Yesu zai tafi Urushalima, ya dauki sha-biyun nan a gefe, yayin da suke tafiya, sai ya ce masu,
18 Voilà que nous montons à Jérusalem, et le Fils de l’homme sera livré aux princes des prêtres et aux scribes, et ils le condamneront à mort.
“Ku duba fa, zamu tafi Urushalima, kuma za a bada Dan Mutum ga manyan firistoci da marubuta. Za su kuma yanke masa hukuncin kisa,
19 Et ils le livreront aux gentils pour être moqué et flagellé et crucifié; et le troisième jour il ressuscitera.
za su kuma bada shi ga al'ummai don suyi masa ba'a, su bulale shi, su kuma gicciye shi. Amma a rana ta uku, za a tada shi.''
20 Alors la mère des fils de Zébédée s’approcha de lui avec ses fils, l’adorant et lui demandant quelque chose.
Sai uwar 'ya'yan Zabadi ta zo wurin Yesu tare da 'ya'yanta. Ta rusuna a gabansa tana neman alfarma a wurinsa.
21 Jésus lui dit: Que voulez-vous? Elle lui répondit: Ordonnez que mes deux fils que voici soient assis, l’un à votre droite, l’autre à votre gauche, dans votre royaume.
Yesu ya ce mata, Me kike so in yi maki?'' Sai ta ce masa, ''Ina so ka ba 'ya'yana izinin zama a mulkinka, daya a hannun damanka, daya kuma a hannun hagunka.
22 Mais, répondant, Jésus dit: Vous ne savez ce que vous demandez. Pouvez-vous boire le calice que je vais boire? Ils lui répondirent: Nous le pouvons.
Amma Yesu ya amsa, ya ce, ''Baku san abin da kuke roko ba. Ko zaku iya sha daga cikin kokon da zan sha bada dadewa ba?'' Sai suka ce masa, ''Zamu iya.''
23 Il leur dit: Vous boirez en effet mon calice: mais d’être assis à ma droite ou à ma gauche, il ne m’appartient pas de vous l’accorder à vous, mais à ceux à qui mon Père l’a préparé.
Sai ya ce masu, ''In dai kokon nan da zan sha ne, lallai zaku sha. Amma, zama a hannun dama na da kuma hannun hagu na, ba ni ne mai bayarwa ba, amma na wadanda Uba na ya shirya domin su ne.''
24 Or, entendant cela, les dix s’indignèrent contre les deux frères.
Sa'anda sauran almajirai goma suka ji haka, sun yi bacin rai da 'yan'uwan nan biyu.
25 Mais Jésus les appela à lui, et leur dit: Vous savez que les princes des nations les dominent, et que les grands exercent la puissance sur elles.
Amma Yesu ya kira su wurin sa, ya ce, ''Kuna sane da cewa, sarakunan al'ummai suna gwada masu mulki, manyan-gari kuma na nuna masu iko.
26 Il n’en sera pas ainsi parmi vous; mais que celui qui voudra être le plus grand parmi vous, soit votre serviteur;
Ba zai kasance haka a tsakanin ku ba. A maimakon haka, duk wanda ke da marmari ya zama da girma a tsakanin ku, ya zama baran ku.
27 Et celui qui voudra être le premier parmi vous sera votre esclave.
Wanda kuma ke da marmari ya zama na farko a cikin ku, ya zama baran ku.
28 Comme le Fils de l’homme n’est point venu pour être servi, mais pour servir et donner sa vie pour la rédemption d’un grand nombre.
Kamar dai yadda Dan mutum bai zo don a bauta masa ba, amma yayi bauta, ya kuma bada ransa fansa domin mutane dayawa.''
29 Lorsqu’ils sortaient de Jéricho, une grande foule le suivit:
Da suka fita daga Yariko, babban taro suka bi shi.
30 Et voilà que deux aveugles assis sur le bord du chemin, entendirent que Jésus passait; et ils élevèrent la voix, disant: Seigneur, fils de David, ayez pitié de nous.
Suka kuma ga makafi biyu zaune a bakin hanya. Da makafin suka ji cewa Yesu ne ke wucewa, sai suka tada murya suna cewa, ''Ya Ubangiji, Dan Dauda, kayi mana jinkai.''
31 Et la foule les gourmandait pour qu’ils se tussent; mais eux criaient encore plus, disant: Seigneur, fils de David, ayez pitié de nous.
Amma jama'ar suka tsauta masu, suka ce suyi shiru. Duk da haka, makafin suka kara tada murya fiye da na da, suka ce, ''Ya Ubangiji, Dan Dauda, kayi mana jinkai.''
32 Alors Jésus s’arrêta, les appela, et dit: Que voulez-vous que je vous fasse?
Sai Yesu ya tsaya cik, ya sa aka kira su, sai ya ce masu, ''Me kuke so in yi maku?''
33 Ils lui répondirent: Seigneur, que nos yeux s’ouvrent.
Sai suka ce masa, Ya Ubangiji, muna so mu sami ganin gari.''
34 Et ayant pitié d’eux, Jésus toucha leurs yeux; et aussitôt ils recouvrèrent la vue et ils le suivirent.
Sai Yesu yayi juyayi a cikin sa, ya taba idanunsu. Nan da nan, suka sami ganin gari, suka kuma bi shi.