< Matthieu 2 >
1 Lors donc que Jésus fut né en Bethléem de Juda, aux jours du roi Hérode, voilà que des mages vinrent de l’Orient à Jérusalem,
Bayanda aka haifi Yesu a Baitalami ta kasar Yahudiya, a zamanin sarki Hirudus, sai ga wadansu masana daga gabas suka zo Urushalima, suna cewa,
2 Disant: Où est celui qui est né roi des Juifs? car nous avons vu son étoile en Orient, et nous sommes venus l’adorer.
''Ina wanda aka haifa sarkin Yahudawa? Mun ga tauraronsa a gabas mun kuma zo mu yi masa sujada.''
3 Ayant appris cela, le roi Hérode se troubla, et tout Jérusalem avec lui.
Da sarki Hirudus ya ji haka, sai ya damu kwarai, haka kuma dukan mutanen Urushalima.
4 Et assemblant tous les princes des prêtres et les scribes du peuple, il s’enquit d’eux où naîtrait le Christ.
Hirudus ya tara dukan manyan firistoci da marubuta na jama'a, ya tambaye su, “Ina za a haifi Almasihun?”
5 Or eux lui dirent: À Bethléem de Juda; car il a été ainsi écrit par le prophète:
Suka ce masa, ''A Baitalami ne ta kasar Yahudiya, domin haka annabin ya rubuta,
6 Et toi, Bethléem, terre de Juda, tu n’es pas la moindre parmi les principales villes de Juda; car c’est de toi que sortira, le chef qui doit régir Israël mon peuple.
'Ke kuma, Baitalami, ta kasar Yahudiya, ba ke ce mafi kankanta ba a cikin shugabanin Yahudiya, domin daga cikin ki mai mulki zai fito wanda zai zama makiyayin jama'a ta Isra'ila.'''
7 Alors Hérode, les mages secrètement appelés, s’enquit d’eux avec soin du temps où l’étoile leur était apparue;
Sai Hirudus ya kira masanan a asirce ya tambaye su aininhin lokacin da tauraron ya bayyana.
8 Et, les envoyant à Bethléem, il dit: Allez, informez-vous exactement de l’enfant; et lorsque vous l’aurez trouvé, faites-le-moi savoir, afin que moi aussi j’aille l’adorer.
Ya aike su Baitalami, ya ce, ''Ku je ku binciko mani dan yaron da kyau. Idan kun same shi, ku kawo mani labari, don ni ma in je in yi masa sujada.”
9 Ceux-ci donc, après avoir entendu le roi, s’en allèrent; et voilà que l’étoile qu’ils avaient vue en Orient les précédait jusqu’à ce qu’elle vint et s’arrêta au-dessus du lieu où était l’enfant.
Bayan sun ji maganar sarkin, sai suka yi tafiyar su, ga shi kuwa, tauraron da suka gani a gabas yana tafe a gaban su, har ya zo ya tsaya bisa inda dan yaron nan yake.
10 Or, voyant l’étoile, il se réjouirent d’une grande joie.
Da suka ga tauraron, sai suka yi matukar farin ciki.
11 Et, entrant dans la maison, ils trouvèrent l’enfant avec Marie, sa mère, et, se prosternant, ils l’adorèrent; puis, leurs trésors ouverts, ils lui offrirent des présents, de l’or, de l’encens et de la myrrhe.
Sai suka shiga gidan, suka ga dan yaron tare da mahaifiyarsa Maryamu. Suka rusuna gabansa suka yi masa sujada. Sa'an nan suka kwance kayansu, suka mika masa kyautar su ta zinariya da lubban, da mur.
12 Mais ayant été avertis en songe de ne point retourner vers Hérode, ils revinrent dans leur pays par un autre chemin.
Allah kuma ya gargade su a mafarki kada su koma wurin Hirudus, sai suka koma kasarsu ta wata hanya dabam.
13 Après qu’ils furent partis, voilà qu’un ange du Seigneur apparut à Joseph pendant son sommeil, et dit: Lève-toi, prends l’enfant et sa mère, fuis en Egypte et restes-y, jusqu’à ce que je te parle; car il arrivera qu’Hérode cherchera l’enfant pour le faire mourir.
Bayan sun tashi, sai ga wani mala'ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusufu a mafarki, ya ce, ''Tashi, ka dauki dan yaron da mahaifiyarsa, ka gudu zuwa kasar Masar, ka zauna a can sai na fada maka, don Hirudus yana shirin binciko dan yaron ya hallaka shi.”
14 Joseph, s’étant levé, prit l’enfant et sa mère pendant la nuit et se retira en Egypte;
A wannan dare fa Yusufu ya tashi ya dauki dan yaron da mahafiyarsa ya tafi Masar.
15 Et il s’y tint jusqu’à la mort d’Hérode, afin que fût accomplie cette parole que le Seigneur a dite par le prophète: J’ai rappelé mon fils de l’Egypte.
Ya zauna a can har mutuwar Hirudus. Wannan kuwa domin a cika abin da Ubangiji ya fada ne ta bakin annabin, ''Daga Masar na kirawo Da na.''
16 Alors Hérode, voyant qu’il avait été trompé par les mages, entra en une grande colère, et il envoya tuer tous les enfants qui étaient dans Bethléem et dans tous ses environs, depuis deux ans et au-dessous, selon le temps dont il s’était enquis des mages.
Da Hirudus ya ga masanan nan sun shashantar da shi, sai ya hasala kwarai, ya aika a karkashe dukan 'yan yara maza da suke Baitalami da kewayenta, daga masu shekara biyu zuwa kasa, gwargwadon lokacin da ya tabbatar a gun masanan.
17 Ce fut alors que s’accomplit la parole du prophète Jérémie, disant:
A lokacin ne aka cika fadar Annabi Irmiya,
18 Une voix a été entendue dans Rama, des pleurs et des cris déchirants souvent répétés: c’était Rachel pleurant ses fils et ne voulant point se consoler, parce qu’ils ne sont plus.
''An ji wata murya a Rama, tana kuka da bakin ciki mai zafi, Rahila ce take kuka saboda 'ya'yanta, kuma ta ki ta ta'azantu, domin ba su.
19 Hérode étant mort, voilà qu’un ange du Seigneur apparut à Joseph pendant son sommeil en Egypte,
Sa'adda Hirudus ya mutu, sai ga mala'ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusufu a mafarki a Masar ya ce,
20 Disant: Lève-toi, prends l’enfant et sa mère, et va dans la terre d’Israël; car ils sont morts, ceux qui recherchaient la vie de l’enfant.
''Tashi ka dauki dan yaron da mahaifiyarsa, ka tafi kasar Isra'ila, domin masu neman ran dan yaron sun mutu.''
21 Joseph s’étant levé, prit l’enfant et sa mère et vint dans la terre d’Israël.
Yusufu ya tashi, ya dauki dan yaron da mahaifiyarsa, ya zo kasar Isra'ila.
22 Mais ayant appris qu’Archélaüs régnait en Judée à la place d’Hérode, son père, il appréhenda d’y aller; et, averti pendant son sommeil, il se retira dans le pays de Galilée.
Amma da ya ji Arkilayus ya gaji mahaifinsa Hirudus, yana mulkin kasar Yahudiya, sai ya ji tsoron isa can. Bayan da Allah ya yi masa gargadi a mafarki, sai ya ratse zuwa kasar Galili
23 Etant donc venu, il habita une ville qui est appelée Nazareth, afin que s’accomplît ce qui a été dit par les prophètes: Il sera appelé Nazaréen.
sai ya je ya zauna a wani gari da ake kira Nazarat. Wannan ya cika abin da aka fada ta bakin annabawa, cewa, za a kira shi Banazare.