< Matthieu 11 >
1 Et il arriva que lorsque Jésus eut fini de donner ces commandements à ses douze disciples, il partit de là pour enseigner et prêcher dans leurs villes.
Bayan Yesu ya gama yi wa almajiransa gargadi, sai ya bar wannan wuri, ya tafi biranensu domin yayi koyorwa, da wa'azi.
2 Or, Jean, quand il eut appris dans la prison les œuvres de Jésus-Christ, envoyant deux de ses disciples,
Da Yahaya mai baftisma ya ji daga kurkuku irin ayyukan da Yesu ke yi, sai ya aika sako ta wurin almajiransa.
3 Lui dit: Est-ce vous qui devez venir, ou est-ce un autre que nous attendons?
Ya ce masa. “Kai ne mai zuwa”? ko mu sa ido ga wani.
4 Et Jésus, répondant leur dit: Allez, rapportez à Jean ce que vous avez entendu et vu:
Yesu ya amsa ya ce masu, “Ku je ku gaya wa Yahaya abin da ku ka gani da abin da ku ka ji.
5 Des aveugles voient, des boiteux marchent, des lépreux sont guéris, des sourds entendent, des morts ressuscitent, des pauvres sont évangélisés.
Makafi suna samun ganin gari, guragu na tafiya, ana tsarkake kutare, kurame na jin magana kuma, ana tada matattu, mabukata kuma ana ba su bishara.
6 Et heureux est celui qui ne se scandalisera point de moi.
Kuma mai albarka ne wanda baya tuntube sabili da ni.
7 Comme ils s’en retournaient, Jésus commença à dire de Jean à la multitude: Qu’êtes-vous allés voir au désert? un roseau agité par le vent?
Bayan wadannan sun tafi, sai Yesu ya fara wa jama'a jawabi game da Yahaya mai baftisma, yana cewa, “Me ake zuwa gani a jeji - ciyawa ce da iska ke busawa?
8 Mais encore, qu’êtes-vous allés voir? un homme vêtu mollement? Mais ceux qui se vêtent mollement sont dans les maisons des rois.
Shin menene kuke zuwa gani a jeji - mutum mai sanye da tufafi masu laushi? Hakika, masu sa tufafi masu laushi suna zaune ne a fadar sarakuna.
9 Qu’êtes-vous donc allés voir? un prophète? Oui. je vous le dis, et plus qu’un prophète;
Amma me ku ke zuwa gani, annabi? Hakika ina fada maku, fiye ma da annabi.
10 Car c’est lui dont il est écrit: Voici que moi j’envoie mon ange devant votre face, lequel préparera votre voie devant vous.
Wannan shine wanda aka rubuta game da shi, 'Duba, ina aika manzona, wanda za ya tafi gabanka domin ya shirya maka hanya inda za ka bi'.
11 En vérité, je vous le dis, il ne s’est pas élevé entre les enfants des femmes de plus grand que Jean-Baptiste; mais celui qui est le plus petit dans le royaume des cieux est plus grand que lui.
Ina gaya maku gaskiya, cikin wadanda mata suka haifa, babu mai girma kamar Yahaya mai baftisma. Amma mafi kankanta a mulkin sama ya fi shi girma.
12 Or, depuis les jours de Jean-Baptiste jusqu’à présent, le royaume des cieux souffre violence, et ce sont des violents qui le ravissent.
Tun daga kwanakin Yahaya mai baftisma zuwa yanzu, mulkin sama yana shan gwagwarmaya, masu husuma kuma su kan kwace shi da karfi.
13 Car tous les prophètes et la loi ont prophétisé jusqu’à Jean.
Gama dukan annabawa da shari'a sun yi annabci har zuwa lokacin Yahaya.
14 Et si vous voulez le comprendre, il est lui-même Élie qui doit venir.
kuma in zaku karba, wannan shine Iliya wanda za ya zo.
15 Que celui qui a des oreilles pour entendre, entende.
Wanda ke da kunnuwan ji, ya ji.
16 Mais à qui comparerai-je cette génération? Elle est semblable à des enfants assis dans la place qui, criant à leurs compagnons,
Da me zan kwatanta wannan zamani? Ya na kamar yara masu wasa a kasuwa, sun zauna suna kiran juna
17 Disent: nous avons chanté pour vous, et vous n’avez point dansé; nous nous sommes lamentés, et vous n’avez poussé ni plaintes ni gémissements.
suna cewa mun busa maku sarewa baku yi rawa ba, mun yi makoki, baku yi kuka ba.
18 Jean, en effet, est venu ne mangeant, ni ne buvant, et ils disent: Il est démoniaque.
Gama Yahaya ya zo, baya cin gurasa ko shan ruwan inabi, sai aka ce, “Yana da aljannu”.
19 Le Fils de l’homme est venu mangeant et buvant, et ils disent: Voilà un homme de bonne chère et adonné au vin, ami des publicains et des pécheurs. Mais la sagesse a été justifiée par ses enfants.
Dan mutum ya zo yana ci yana sha, sai aka ce, 'Duba, ga mai hadama, mashayi kuma, abokin masu karbar haraji da masu zunubi!' Amma hikima, ta wurin aikin ta ake tabbatar da ita.
20 Alors il commença à faire des reproches aux villes dans lesquelles s’était opéré le plus grand nombre de ses miracles, de ce qu’elles n’avaient pas fait pénitence.
Sannan Yesu ya fara tsautawa biranen nan inda ya yi yawancin ayukansa, domin ba su tuba ba.
21 Malheur à toi, Corozaïn; malheur à toi, Bethsaïde! car si les miracles qui ont été faits au milieu de vous avaient été faits dans Tyr et Sidon, elles auraient fait pénitence autrefois sous le cilice et dans la cendre.
“Kaiton ki Korasinu, kaiton ki Batsaida! In da an yi irin ayuka masu ban mamaki a Taya da Sidon! Yadda aka yi a cikinku, da tuni sun tuba suna sanye da tsumma da yafa toka.
22 Aussi, je vous le dis: Pour Tyr et pour Sidon, il y aura plus de rémission au jour du jugement que pour vous.
Amma zai zama da sauki a kan Taya da Sidon a ranar shari'a fiye da ku.
23 Et toi, Capharnaüm, est-ce jusqu’au ciel que tu t’élèveras? Tu descendras jusqu’aux enfers, parce que, si dans Sodome avaient été faits les miracles qui ont été faits au milieu de toi, elle aurait peut-être subsisté jusqu’à ce jour. (Hadēs )
Ke kafarnahum, kina tsammani za a daukaka ki har zuwa sama? A'a za a saukar da ke kasa zuwa hades. Gama in da an yi irin al'ajiban da aka yi a cikin ki a Sodom, da tana nan har yanzu. (Hadēs )
24 Bien plus, je vous dis que pour le pays de Sodome, il y aura au jour du jugement plus de rémission que pour toi.
Amma ina ce maku, za a saukaka wa Sodom a ranar shari'a fiye da ku.”
25 En ce temps-là, Jésus prenant la parole, dit: Mon Père, Seigneur du ciel et de la terre, je vous rends gloire de ce que vous avez caché ces choses aux sages et aux prudents, et que vous les avez révélées aux petits.
A wannan lokaci Yesu ya ce, “Ina yabon ka, ya Uba, Ubangijin sama da kasa, domin ka boye wa masu hikima da fahimta wadannan abubuwa, ka bayyana wa marasa sani, kamar kananan yara.
26 Oui, mon Père, parce qu’il vous a plu ainsi.
I, ya Uba gama wannan shine ya yi daidai a gare ka.
27 Toutes choses m’ont été données par mon Père. Et nul ne connaît le Fils, si ce n’est le Père; et nul ne connaît le Père, si ce n’est le Fils, et celui à qui le Fils aura voulu le révéler.
An mallaka mani dukan abu daga wurin Ubana. Sannan babu wanda ya san Dan, sai Uban, babu kuma wanda ya san Uban, sai Dan, da duk wanda ya so ya bayyana masa.
28 Venez à moi, vous tous qui prenez de la peine et qui êtes chargés, et je vous soulagerai.
Ku zo gare ni, dukanku masu wahala da fama da nauyin kaya, ni kuma zan ba ku hutawa.
29 Prenez mon joug sur vous, et apprenez de moi que je suis doux et humble de cœur, et vous trouverez du repos pour vos âmes.
Ku dauki karkiya ta ku koya daga gare ni, gama ni mai tawali'u ne da saukin hali a zuciya, sannan zaku sami hutawa ga rayukanku.
30 Car mon joug est doux et mon fardeau léger.
Gama karkiyata mai sauki ce, kaya na kuma ba shi da nauyi.”