< Marc 9 >

1 Il leur disait encore: En vérité, je vous le dis, il y en a parmi ceux ici présents qui ne goûteront pas de la mort, qu’ils n’aient vu le royaume de Dieu venant dans sa puissance.
Sai ya ce masu, “Hakika, ina gaya maku, akwai wasun ku anan da ba za su mutu ba, sai sun ga mulkin Allah ya bayyana da iko.”
2 Six jours après, Jésus prit Pierre, Jacques et Jean, et il les conduisit seuls à l’écart sur une haute montagne, et il fut transfiguré devant eux.
Bayan kwana shida Yesu ya dauki Bitrus, da Yakubu, da Yahaya, ya kai su kan wani dutse mai tsawo, su kadai. Sai kamaninsa ya sake a gabansu.
3 Ses vêtements devinrent resplendissants et très blancs comme la neige, d’une blancheur telle, qu’aucun foulon sur la terre ne pourrait l’égaler.
Sai tufafinsa ya zama fari fat, yadda ba mai rinin da zai iya rininsa haka a duniya.
4 Et Elie leur apparut avec Moïse; et ils s’entretenaient avec Jésus.
Sai Iliya da Musa suka bayyana gare su, suna magana da Yesu.
5 Alors, prenant la parole, Pierre dit à Jésus: Maître, il nous est bon d’être ici. Faisons trois tentes, une pour vous, une pour Moïse, et une pour Elie.
Sai Bitrus ya amsa ya ce, malam, bari mu da muke anan mu kafa bukka uku, daya ta ka, daya ta Musa, da ta Iliya,
6 Car il ne savait ce qu’il disait, parce qu’ils étaient saisis de crainte.
Ya rasa abin da zai fada ne, don sun tsorota kwarai.)
7 Cependant il se fit une nuée qui les couvrit de son ombre; et il vint de la nuée une voix disant: Celui-ci est mon fils bien-aimé; écoutez-le.
Sai ga wani gajimare ya zo ya rufe su, aka kuma ji wata murya daga gajimaren, “ta ce Wannan shine kaunataccen Dana, Ku saurare shi.
8 Et aussitôt, regardant tout autour, ils ne virent plus personne, si ce n’est Jésus seul avec eux.
Nan take da suka duba, ba su ga kowa ba, sai Yesu shi kadai.
9 Mais lorsqu’ils descendaient de la montagne, il leur commanda de ne raconter à personne ce qu’ils avaient vu, jusqu’à ce que le Fils de l’homme fût ressuscité d’entre les morts.
Suna cikin gangarowa daga dutsen, sai ya kwabe su kada su gaya wa kowa abin da suka gani, sai bayan da Dan Mutum ya tashi daga mattatu.
10 Et ils gardèrent cette parole en eux-mêmes, se demandant ce que voulait dire: Jusqu’à ce qu’il fût ressuscité d’entre les morts.
Sai suka bar zancen a tsakaninsu, amma suka tamabayi junansu “mene ne tashin matattu” ke nufi.
11 Et ils l’interrogeaient, disant: Pourquoi donc les pharisiens et les scribes disent-ils qu’il faut qu’Elie vienne auparavant?
Suka tambaye shi yaya malaman attaura suka ce Iliya zai fara zuwa?”
12 Jésus répondant, leur dit: Elie viendra auparavant, et il rétablira toutes choses; et, comme il est écrit du Fils de l’homme, il faudra qu’il souffre beaucoup et qu’il soit rejeté avec mépris.
Ya ce masu, laile ne Iliya ya fara zuwa ya raya dukan abubuwan. Don me a ka rubuta cewa Dan Mutum, zai sha wuya iri iri a kuma ki shi?
13 Mais je vous dis qu’Elie est déjà venu (et ils lui ont fait tout ce qu’ils ont voulu), ainsi qu’il est écrit de lui.
Amma ina gaya muku Iliya ya riga, ya zo, amma sun yi masa abin da suke so su yi kamar yadda littatafai suka yi magana a kansa.”
14 Et venant vers ses disciples, il vit une grande foule autour d’eux, et des scribes disputant avec eux.
Sa'adda suka dawo wurin sauran almajiran, suka ga taron jama'a masu yawa suna ta muhawara tare da manyan malaman attaura.
15 Aussitôt tout le peuple apercevant Jésus, fut saisi d’étonnement et de frayeur; et, accourant, ils le saluaient.
Da ganin sa, sai dukan taron yayi mamaki kwarai da gaske, suka dungumo wurinsa a guje, suna gaishe shi.
16 Alors il leur demanda: De quoi disputez-vous ensemble?
Ya tambayi almajiransa, “Wacce muhawara ce kuke yi da su?”
17 Et un homme de la foule prenant la parole, dit: Maître, je vous ai amené mon fils, qui a en lui un esprit muet;
Daya daga cikin taron ya amsa masa”malam, ga shi na kawo maka dana don yana da beben aljani.
18 Lequel, partout où il s’empare de lui, le brise contre terre, et l’enfant écume, grince des dents, et il se dessèche. J’ai dit à vos disciples de le chasser, mais ils ne l’ont pu.
Duk lokacin da ya tasar masa yakan buga shi har kasa, na kuma yi wa almajiranka magana su fitar sun kasa.
19 Jésus, s’adressant à eux, dit: Ô race incrédule, jusqu’à quand serai-je avec vous? jusqu’à quand vous supporterai-je? Amenez-le-moi.
Ya amsa masu ya ce ya ku mutanen zamaninnan marasa bangaskiya, har yaushe zan kasance tare da ku ina jimrewa? ku dai kawo mini shi.
20 Et ils le lui amenèrent. Or sitôt qu’il eut vu Jésus, l’esprit le tourmenta; et, brisé contre terre, il se roulait en écumant.
Sai suka kawo masa yaron. Da ruhun ya ga Yesu, nan da nan ya buge yaron jikinsa na rawa. Sai yaron ya fadi yana ta birgima, bakinsa yana kumfa.
21 Jésus demanda à son père: Combien y a-t-il de temps que cela lui arrive? Depuis son enfance, dit le père.
Yesu ya tambayi mahaifin yaron, Tun yaushe wannan abu ya same shi? Mahaifin yaron ya ce tun yana karami.
22 Souvent il l’a jeté dans le feu et dans l’eau pour le faire périr; mais si vous pouvez quelque chose, ayez pitié de nous et secourez-nous.
Ya kuwa sha jefa shi a ruwa da wuta, don ya halakar da shi. Idan zaka iya yin wani abu, ka ji tausayinmu ka taimakemu.
23 Jésus lui dit: Si tu peux croire, tout est possible à celui qui croit.
Yesu ya ce masa, “In zan iya? Ai dukan abu mai yiwuwa ne, ga duk wanda ya gaskata.
24 Et aussitôt le père de l’enfant s’écria, disant avec larmes: Je crois, Seigneur; aidez mon incrédulité.
Nan da nan mahaifin yaron ya daga murya ya ce, Na ba da gaskiya. A kore mini rashin bangaskiyata.
25 Et Jésus voyant une foule qui accourait, menaça l’esprit impur, lui disant: Esprit sourd et muet, je te le commande, sors de cet enfant et n’y rentre plus.
Da Yesu ya ga taron na dungumowa a guje, sai ya tsawata wa bakin aljanin ya ce masa, “kai, beben aljani na umarce ka, ka fita daga wannan yaron kar ka sake shigar sa.
26 Et poussant un grand cri et le déchirant violemment, il sortit de l’enfant qui devint comme mort; de sorte que beaucoup disaient: Il est mort.
Sai wannan aljanin ya daga murya ya fita ya rabu da wannan yaron. Sai yaro ya zama kamar mattacce, sai sauran mutanen suka ce, “Ai, yaron ya mutu.
27 Mais Jésus, prenant sa main et le soulevant, il se leva.
Yesu ya kama hannunsa, ya daga shi, sai yaron ya mike tsaye.
28 Et lorsque Jésus fut entré dans une maison, ses disciples lui demandèrent en secret: Pourquoi, nous, n’avons-nous pu le chasser?
Da Yesu ya shiga gida, sai almajiransa suka tambaye shi a kadaice, me ya sa muka kasa fitar da shi?”
29 Il leur dit: Ce genre de démons ne peut se chasser que par la prière et le jeûne.
Ya ce masu, “Ai, irin wannan ba ya fita sai da addu'a.”
30 Etant partis de là, ils traversèrent la Galilée; et il ne voulait pas que personne le sût.
Sai suka ratsa cikin Galili, amma ba ya son kowa ya san inda suke.
31 Cependant il instruisait ses disciples, et leur disait: Le Fils de l’homme sera livré entre les mains des hommes, et ils le tueront, et le troisième jour après sa mort, il ressuscitera.
Da yake koyar da almajiransa, ya ce masu lokaci na zuwa da za'a ba da Dan mutum a hannun mutane, za su kuwa kashe shi, sa'adda aka kashe shi kuma, bayan kwana uku zai tashi.
32 Mais ils ne comprenaient point cette parole, et ils craignaient de l’interroger.
Amma fa ba su fahimci maganar ba, suna kuma jin tsoron tambayarsa.
33 Ils vinrent ensuite à Capharnaüm; et, lorsqu’ils furent dans la maison, il leur demanda: Que discutiez-vous en chemin?
Sai suka zo kafarnahum. A lokacin da ya ke cikin gida, ya tambayi Al'majiransa, Menene ku ke magana a kansa a hanya?
34 Et ils se taisaient, parce que dans le chemin ils avaient disputé ensemble qui d’entre eux était le plus grand.
Amma suka yi shiru. don suna gardama da junansu akan hanya, a kan wane ne mafi girma.
35 Et, s’étant assis, il appela les douze, et leur dit: Si quelqu’un veut être le premier, il sera le dernier de tous et le serviteur de tous.
Sai ya zauna, ya kira al'majiransa goma sha biyu, yace masu duk wanda ya ke so ya zama na fari, dole ya kankantar da kansa, sa'annan ya bautawa sauran duka.
36 Puis, prenant un enfant, il le mit au milieu d’eux; et après l’avoir embrassé, il leur dit:
Sai ya dauko karamin yaro a hannunsa ya sa shi a tsakiyarsu. Ya rumgome shi a kafadarsa ya ce masu.
37 Quiconque reçoit en mon nom un petit enfant comme celui-ci, me reçoit; et quiconque me reçoit, reçoit non pas moi, mais celui qui m’a envoyé.
Dukan wanda ya karbi dan karamin yaron nan a cikin sunana ni ya karba, kuma dukan wanda ya karbi wani, ni ya karba, bai kuma karbeni ni kadai ba, duk da wanda ya aiko ni.”
38 Jean, prenant la parole, lui dit: Maître, nous avons vu quelqu’un qui chassait les démons en votre nom, et qui ne nous suit pas, et nous l’en avons empêché.
Sai Yahaya ya ce masa, Malam mun ga wani yana fitar da aljanu da sunanka mun yi kokari mu hana shi domin ba ya tare da mu.
39 Mais Jésus leur répondit: Ne l’en empêchez point; car il n’y a personne qui fasse un miracle en mon nom, et qui puisse incontinent mal parler de moi;
Sai Yesu ya ce masu ku kyale shi domin babu wanda zai yi irin wannan babban aikin, sa'annan ya fadi wasu maganganu mara sa kyau a kanmu.
40 Car qui n’est pas contre vous, est pour vous.
Duk wanda ba ya gaba da mu, na mu ne.
41 Et quiconque vous donnera un verre d’eau en mon nom, parce que vous êtes au Christ, en vérité, je vous le dis, il ne perdra point sa récompense.
Duk wanda ya ba ku ruwa ku sha domin kuna na Almasihu, gaskiya nake fada maku ba za ya rasa ladansa ba.
42 Mais quiconque scandalisera un de ces petits qui croient en moi, il vaudrait mieux pour lui que l’on mît autour de son cou une meule de moulin, et qu’on le jetât dans la mer.
Amma duk wanda ya sa kananan nan tuntube, ya fi kyau a rataya masa dutsen nika a jefa shi a cikin teku.
43 Que si votre main vous scandalise, coupez-la: il vaut mieux pour vous entrer dans la vie, privé d’une main, que d’aller, ayant deux mains, dans la géhenne du feu qui ne peut s’éteindre, (Geenna g1067)
Idan har hannun ka zai sa ka yi tuntube, zai fi kyau ka yanke shi. Domin zai fi kyau ka shiga aljanna da hannu daya da ka shiga jahannama da hannu biyu. (Geenna g1067)
44 Où leur ver ne meurt point, et leur feu ne s’éteint pas.
(Inda tsutsotsi basu mutuwa, wutar kuma bata mutuwa).
45 Et si votre pied vous scandalise, coupez-le: il vaut mieux pour vous entrer, privé d’un pied, dans la vie éternelle, que d’être jeté, ayant deux pieds, dans la géhenne du feu qui ne peut s’éteindre, (Geenna g1067)
Idan kafarka za ta sa ka yi tuntube, ka yanke ta ka yar. Zai fi kyau ka shiga aljanna da kafa daya da ka shiga jahannama da kafa biyu. (Geenna g1067)
46 Où leur ver ne meurt point, et leur feu ne s’éteint pas.
(Inda tsutsotsi basu mutuwa, wutar kuma bata mutuwa).
47 Que si votre œil vous scandalise, arrachez-le: il vaut mieux pour vous entrer, privé d’un œil, dans le royaume de Dieu, que d’être jeté, ayant deux yeux, dans la géhenne du feu, (Geenna g1067)
Idan idonka zai sa ka yi tuntube, ka kwakule shi ka yar, domin gwamma ka shiga mulkin Allah da ido daya, da a jefa ka cikin wuta da idanu biyu. (Geenna g1067)
48 Où leur ver ne meurt point, et leur feu ne s’éteint pas.
Inda tsutsotsi basu mutuwa, wutar kuma bata mutuwa.
49 Car tous seront salés par le feu, comme toute victime doit être salée par le sel.
Domin da wuta za a tsarkake kowa.
50 Le sel est bon; mais si le sel perd sa vertu, avec quoi l’assaisonnerez-vous? Ayez du sel en vous, et conservez la paix entre vous.
Gishiri yana da kyau, amma idan ya rasa zakinsa, ta ya ya za ka sa shi yayi zaki kuma? Ku kasance da zaki, kuma ku yi zaman lafiya da kowa.

< Marc 9 >