< Marc 5 >
1 Et ils vinrent de l’autre côté de la mer dans le pays des Géraséniens.
Da su ka zo daya ketaren tekun, wanda ya ke cikin yankin Garasinawa.
2 Et comme Jésus sortait de la barque, tout à coup accourut à lui d’au milieu des sépulcres, un homme possédé d’un esprit impur,
Sa'adda Yesu ya sauko daga cikin jirgin ruwan sai wani mutum mai aljanu ya fito daga cikin kaburbura ya tarbe shi.
3 Lequel habitait dans les sépulcres; et nul ne pouvait le tenir lié, même avec des chaînes.
Mutumin yana zama a cikin kaburbura. An daure shi da sarkoki da mari
4 Car souvent, serré de chaînes et les pieds dans les fers, il avait rompu ses chaînes et brisé ses fers, et personne ne le pouvait dompter.
An daure shi da sarkoki da mari sau da yawa, amma ya tsuntsunke sarkoki da marin. har ma ba wanda zai iya daure shi kuma.
5 Et sans cesse, le jour et la nuit, il était parmi les tombeaux et sur les montagnes criant et se meurtrissant avec des pierres.
Dare da rana a cikin kabarbarun da duwatsu mutumin ya na ihu ya na yaiyage jikinsa da duwatsu masu kaifi.
6 Or voyant Jésus de loin, il accourut et l’adora;
Sa'adda ya hango Yesu daga nesa, sai ya tarbi Yesu ya durkusa a gabansa.
7 Et, criant d’une voix forte, il dit: Qu’importe à moi et à vous, Jésus, Fils du Dieu Très-Haut? Je vous adjure par Dieu, ne me tourmentez point.
Ya tada muryarsa da karfi ya ce, ina ruwa na da kai? Yesu Dan Allah Madaukaki Ina rokon ka da sunan Allah kada ka bani wahala,
8 Car il lui disait: Esprit impur, sors de cet homme!
Gama Yesu ya ce masa kai aljani ka fito daga cikinsa.”
9 Et il lui demanda: Quel est ton nom? Et il lui répondit: Légion est mon nom; car nous sommes beaucoup.
Ya tambaye shi, “Yaya sunanka? Ya ce suna na tari gama muna da yawa.
10 Et il le suppliait avec instance de ne point le chasser hors de ce pays.
Ya yi ta rokonsa kada ya raba su da wannan yankin kasar.
11 Or il y avait là, le long de la montagne, un grand troupeau de pourceaux qui paissaient.
Akwai babban garken aladu a wurin suna kiwo a gindin tsauni.
12 Et les esprits suppliaient Jésus, disant: Envoyez-nous dans ces pourceaux, afin que nous entrions en eux.
Sai suka roke shi ya bar su su shiga cikin wadannan aladun.
13 Et Jésus le leur permit aussitôt. Les esprits impurs, sortant donc du possédé, entrèrent dans les pourceaux, et le troupeau, d’environ deux mille, se précipita impétueusement dans la mer, et s’y noya.
Shi kuma ya yardar masu. Aljanun suka fita suka shiga cikin aladun su kimanin dubu biyu. Aladun dubu biyu suka gangaro daga gindin tsaunin suka fada cikin ruwa.
14 Ceux qui les gardaient s’enfuirent et répandirent cette nouvelle dans la ville et dans les champs. Aussitôt les gens sortirent pour voir ce qui était arrivé;
Mutanen da ke kiwon aladun su ka shiga cikin gari da kewaye suka bada labarin abin da ya faru. Mutane da yawa suka je su ga abin da ya faru
15 Ils vinrent vers Jésus, et ils virent celui qui avait été tourmenté par le démon, assis, vêtu et sain d’esprit; et ils furent saisis de crainte.
Sai suka zo wurin Yesu suka ga mutumin mai aljanun a zaune, cikin hankalinsa, saye da tufafi, sai suka tsorata.
16 Et ceux qui avaient vu leur racontèrent ce qui était arrivé au possédé et aux pourceaux;
Wadanda suka zo su ka ga abin da ya faru da mutumin mai aljanun, suka je suka fada wa mutane abin da suka gani game da aladun.
17 Et ils commencèrent à prier Jésus de s’éloigner de leurs confins.
Mutanen suka roke shi ya fita daga yankin kasarsu.
18 Lorsqu’il montait dans la barque, celui qui avait été tourmenté par le démon, le supplia de lui permettre de rester avec lui;
Shi mutumin da aljanu ke iko da shi, sa'adda ya ga Yesu zai shiga cikin jirgin ruwa ya tafi, ya roki Yesu da ya bi shi.
19 Mais il le lui refusa et lui dit: Va dans ta maison, vers les tiens, et annonce-leur tout ce que le Seigneur a fait pour toi, et comme il a eu pitié de toi.
Amma Yesu bai yarda masa ba. Ya ce masa ka tafi gidanku, wurin mutanenka ka gaya ma su alherin da Ubangiji ya yi maka.
20 Il s’en alla donc, et commença à publier dans la Décapole tout ce que Jésus avait fait pour lui; et tous étaient dans l’admiration.
Mutumin ya shiga cikin Dikafolis yana shaidar babban abin da Yesu ya yi masa, dukansu suka cika da mamaki.
21 Jésus ayant repassé dans la barque de l’autre côté de la mer, il s’assembla une grande multitude autour de lui; et il était près de la mer.
Sa'adda Yesu ya sake ketaren kogin zuwa daya gefen, acikin jirgin, sai taron jama'a suka keweye shi, a gefen tekun.
22 Or vint un chef de synagogue, nommé Jaïre; le voyant, il se jeta à ses pieds,
Sai wani daya daga cikin shugabannin Majami'a mai suna Yayirus, ya zo, wurinsa sa'adda ya ganshi ya durkusa a gabansa.
23 Et il le suppliait instamment, disant: Ma fille est à l’extrémité; venez, imposez votre main sur elle, afin qu’elle guérisse et qu’elle vive.
Ya yi ta rokonsa, yana cewa, “Diya ta ba ta da lafiya har ma ta kusa mutuwa. Ina rokonka mu je gida na ka dora ma ta hannu domin ta warke. ta rayu.”
24 Et il s’en alla avec lui; et une grande multitude le suivait et le pressait.
Sai ya tafi tare da shi, babban taro suka biyo shi har ma suna matse shi.
25 Alors, une femme qui avait une perte de sang depuis douze années,
Akwai wata mace wadda ta ke zubar jini ta kai tsawon shekara goma sha biyu.
26 Et qui avait beaucoup souffert de plusieurs médecins, et avait dépensé tout son bien sans aucun fruit, se trouvant plutôt dans un état pire,
Ta sha wahala kwarai da gaske ta je wurin likitoci da yawa ta kashe kudi sosai, amma ba ta warke ba abin ma sai karuwa ya ke yi.
27 Ayant entendu parler de Jésus, vint dans la foule, par derrière, et toucha son vêtement;
Ta ji labarin Yesu. Sai ta biyo bayansa yana tafiya cikin taro, ta taba habar rigarsa.
28 Car elle disait: Si je touche seulement son vêtement, je serai guérie.
Domin ta ce “Idan dai na taba ko da habar rigarsa zan warke.”
29 Et aussitôt la source du sang tarit, et elle sentit en son corps qu’elle était guérie de son mal.
Da dai ta taba shi sai zubar jinin ta ta tsaya, ta ji a jikin ta ta warke, daga damuwarta.
30 Au même moment, Jésus connaissant en lui-même la vertu qui était sortie de lui, et se retournant vers la foule, demandait: Qui a touché mes vêtements?
Nan da nan, Yesu ya ji iko ya fita daga gare shi sai ya ce “wanene ya taba rigata?”
31 Ses disciples lui répondaient: Vous voyez la foule qui vous presse, et vous demandez: Qui m’a touché?
Almajiransa suka ce, “a cikin wannan taron mutane da yawa ka ce wanene ya taba ni?”
32 Et il regardait tout autour, pour voir celle qui l’avait fait.
Amma Yesu ya waiga ya ga ko wanene ya taba shi.
33 Alors la femme, craintive et tremblante, sachant ce qui s’était passé en elle, vint et se prosterna devant lui, et lui dit toute la vérité.
Matar ta san abin da ya faru sai ta zo cikin tsoro da rawar jiki ta durkusa a gaban Yesu ta fada masa gaskiya.
34 Jésus lui dit: Ma fille, votre foi vous a sauvée: allez en paix et soyez guérie de votre infirmité.
Sai ya ce da ita, “Diya bangaskiyarki ta warkar da ke, ki tafi lafiya kin sami warkewa daga cutarki”.
35 Comme il parlait encore, des gens du chef de synagogue vinrent, disant: Votre fille est morte; pourquoi tourmentez-vous davantage le maître?
Sa'adda ya ke magana da ita sai ga mutane daga gidan shugaban majami'a suka ce “Diyarka ta mutu me ya sa za ka dami malam?”
36 Mais Jésus, cette parole entendue, dit au chef de synagogue: Ne craignez point; croyez seulement.
Amma sa'adda Yesu ya ji abin da suka ce, sai ya ce da shugaban majami'ar, “kada ka ji tsoro ka ba da gaskiya kawai.”
37 Et il ne permit à personne de le suivre, sinon à Pierre, à Jacques et à Jean frère de Jacques.
Bai bari kowa ya kasance tare da shi ba sai Bitrus da Yakubu da Yahaya dan'uwan Yakubu.
38 En arrivant à la maison du chef de synagogue, il vit du tumulte, des gens pleurant et poussant de grands cris.
Suka zo gidan shugaban majami'ar ya ga mutane suna bakin ciki, suna kuka sosai.
39 Or, étant entré, il leur dit: Pourquoi vous troublez-vous et pleurez-vous? La jeune fille n’est pas morte, mais elle dort.
Sa'adda ya shiga gidan ya ce da mutane “Me ya sa kuke damuwa da kuka?” Yarinyar ba ta mutu ba barci ta ke yi.
40 Et ils se riaient de lui. Mais Jésus, les ayant tous renvoyés, prit le père et la mère de la jeune fille, et ceux qui étaient avec lui, et entra dans le lieu où la jeune fille était couchée.
Sai su kayi masa dariya. Amma ya fitar da su waje su duka. Ya kira baban yarinyar da mamar ta da wadansu da ke tare da shi su ka shiga wurin da yarinyar ta ke.
41 Et tenant la main de la jeune fille, il lui dit: Talitha cumi; ce que l’on interprète ainsi: Jeune fille (je vous le commande), levez-vous.
Ya kama hannun yarinyar ya ce da ita “Tilatha koum” wato yarinya na ce ki tashi”
42 Et aussitôt la jeune fille se leva, et elle marchait; car elle avait douze ans; et tous furent frappés d’une grande stupeur.
Nan da nan yarinyar ta tashi ta yi tafiya [gama shekarun ta sun kai goma sha biyu]. Nan da nan mutanen suka yi mamaki kwarai da gaske.
43 Mais il leur commanda fortement que personne ne le sût, et il dit de lui donner à manger.
Ya ummurce su da gaske kada kowa ya sani. Ya ce da su su ba ta abinci ta ci.