< Marc 14 >
1 Or c’était la Pâque et les azymes deux jours après; et les princes des prêtres et les scribes cherchaient comment ils se saisiraient de lui par ruse, et le feraient mourir.
To, saura kwana biyu ne kaɗai a yi Bikin Ƙetarewa da Bikin Burodi Marar Yisti, sai manyan firistoci da malaman dokoki, suka nemi wani dalili su kama Yesu a ɓoye, su kashe.
2 Mais ils disaient: Non pas un jour de la fête, de peur qu’il ne s’élevât quelque tumulte dans le peuple.
Suka ce, “Ba a lokacin Biki ba, don kada mutane su yi tawaye.”
3 Et comme Jésus se trouvait à Béthanie, dans la maison de Simon le lépreux, et qu’il était à table, il vint une femme ayant un vase d’albâtre plein d’un parfum de nard d’épi d’un grand prix. Or, le vase rompu, elle répandit le parfum sur sa tête.
Yayinda yake a Betani, a gidan wani mutumin da ake kira Siman Kuturu, yana cin abinci, sai wata mace ta zo da wani ɗan tulu na turaren alabasta da aka yi da nardi zalla, mai tsadan gaske. Ta fasa tulun, ta kuma zuba turaren a kansa.
4 Quelques-uns s’en indignèrent en eux-mêmes, et ils disaient: Pourquoi avoir ainsi perdu ce parfum?
Waɗansu daga cikin waɗanda suke wurin, suka ji haushi, suka ce wa juna, “Me ya sa za a ɓata turaren nan haka?
5 Il pouvait en effet, ce parfum, se vendre plus de trois cents deniers, et être donné aux pauvres. Et ils murmuraient contre elle.
Da an sayar da shi, ai, da an sami kuɗi fiye da albashi ma’aikaci na shekara guda, a ba wa matalauta. Sai suka tsawata mata da zafi.”
6 Mais Jésus dit: Laissez-la: pourquoi lui faites-vous de la peine? C’est une bonne œuvre qu’elle a faite envers moi;
Yesu ya ce, “Ku ƙyale ta mana. Don me kuke damunta? Ta yi abu mai kyau a gare ni.
7 Car les pauvres, vous les avez toujours avec vous, et quand vous voulez, vous pouvez leur faire du bien; mais moi, vous ne m’avez pas toujours.
Matalauta dai suna tare da ku kullum, za ku kuma iya taimakonsu a duk lokacin da kuke so. Amma ni ba zan kasance da ku kullum ba.
8 Ce qu’a pu celle-ci, elle l’a fait; elle a d’avance parfumé mon corps pour la sépulture.
Ta yi abin da ta iya yi. Ta zuba turare a jikina kafin lokaci, don shirin jana’izata.
9 En vérité, je vous le dis: Partout où sera prêché cet Evangile, dans le monde entier, ce que celle-ci vient de faire, sera même raconté en mémoire délie.
Gaskiya nake gaya muku, duk inda aka yi wa’azin bishara ko’ina a duniya, za a faɗi abin da ta yi, domin tunawa da ita.”
10 Alors Judas Iscariote, un des douze, alla trouver les princes des prêtres, pour le leur livrer.
Sai Yahuda Iskariyot, ɗaya daga cikin Sha Biyun nan, ya je wajen manyan firistoci don yă bashe Yesu a gare su.
11 Ceux-ci l’entendant, se réjouirent, et promirent de lui donner de l’argent. Aussi cherchait-il une occasion favorable pour le leur livrer.
Suka yi murna da jin haka, suka yi alkawari za su ba shi kuɗi. Don haka, ya fara neman zarafi yă ba da shi.
12 Or le premier jour des azymes, auquel on immolait la pâque, ses disciples lui dirent: Où voulez-vous que nous allions vous préparer ce qu’il faut pour manger la pâque?
A rana ta fari ta Bikin Burodi Marar Yisti, lokacin da akan yanka ɗan ragon hadayar kafara, bisa ga al’ada ta tunawa da Bikin Ƙetarewa, sai almajiran Yesu suka tambaye shi, suka ce, “Ina kake so mu je mu shirya maka wurin da za ka ci Bikin Ƙetarewa?”
13 Et il envoya deux de ses disciples, et leur dit: Allez dans la ville; vous rencontrerez un homme portant une cruche d’eau, suivez-le;
Sai ya aiki biyu daga cikin almajiransa ya ce, “Ku shiga cikin birni, za ku sadu da wani ɗauke da tulun ruwa. Ku bi shi.
14 Et, quelque part qu’il entre, dites au maître de la maison: Le Maître dit: Où est le lieu où je pourrai manger la pâque avec mes disciples?
Gidan da ya shiga, ku gaya wa maigidan cewa, ‘Malam yana tambaya, ina ɗakin baƙina, inda zan ci Bikin Ƙetarewa tare da almajiraina?’
15 Et il vous montrera un grand cénacle meublé; faites-y les préparatifs pour nous.
Zai nuna muku wani babban ɗakin sama da aka shirya domin baƙi. Ku yi mana shirin a can.”
16 Ses disciples s’en allèrent donc; ils vinrent dans la ville, trouvèrent les choses comme il leur avait dit, et préparèrent la pâque.
Almajiran suka tafi, suka shiga cikin birnin, suka kuwa tarar da kome kamar yadda Yesu ya faɗa musu. Sai suka shirya Bikin Ƙetarewa.
17 Le soir étant venu, il vint avec les douze.
Da yamma ta yi, sai Yesu ya zo tare da Sha Biyun.
18 Et comme ils étaient à table et qu’ils mangeaient, Jésus leur dit: En vérité, je vous le dis, un de vous qui mange avec moi me trahira.
Yayinda suke cin abinci a tebur, sai ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, ɗaya daga cikinku zai bashe ni, wani wanda yake ci tare da ni.”
19 Alors les disciples commencèrent à s’attrister, et à lui demander chacun en particulier: Est-ce moi?
Suka cika da baƙin ciki, da ɗaya-ɗaya suka ce masa, “Tabbatacce, ba ni ba ne, ko?”
20 Il leur répondit: Un des douze, qui met avec moi la main dans le plat.
Ya ce, “Ɗaya daga cikin Sha Biyun ne, wanda yake ci tare da ni a kwano.
21 Pour le Fils de l’homme, il s’en va, ainsi qu’il est écrit de lui; mais malheur à l’ homme par qui le Fils de l’homme sera livré! Il vaudrait mieux pour cet homme qu’il ne fut pas né.
Ɗan Mutum zai tafi kamar yadda yake a rubuce game da shi, amma kaiton mutumin da ya bashe Ɗan Mutum! Zai fi masa, da ba a haife shi ba.”
22 Et pendant qu’ils mangeaient, Jésus prit du pain, et puis l’ayant béni, il le rompit, le leur donna, et dit: Prenez, ceci est mon corps.
Yayinda suke cin abinci, sai Yesu ya ɗauki burodi, ya yi godiya, ya kakkarya, ya ba wa almajiransa, yana cewa, “Ku karɓa, wannan jikina ne.”
23 Et, ayant pris le calice et rendu grâces, il le leur donna, et ils en burent tous.
Sai kuma ya ɗauki kwaf ruwan inabi, ya yi godiya, ya kuma miƙa musu, dukansu suka sha daga ciki.
24 Et il leur dit: Ceci est mon sang, le sang du Nouveau Testament, qui sera répandu pour un grand nombre.
Sai ya ce musu, “Wannan jinina ne na alkawari, wanda aka zubar da shi saboda mutane da yawa.
25 En vérité je vous le dis, je ne boirai plus de ce fruit de la vigne, jusqu’au jour où je le boirai nouveau dans le royaume de Dieu.
Gaskiya nake gaya muku, ‘Ba zan ƙara sha daga’ya’yan inabi ba, sai ranan nan, da zan sha shi sabo a mulkin Allah.’”
26 Et, l’hymne dit, ils s’en allèrent au mont des Oliviers.
Da suka rera waƙa, sai suka fita, suka tafi Dutsen Zaitun.
27 Et Jésus leur dit: Vous vous scandaliserez tous de moi cette nuit; car il est écrit: Je frapperai le pasteur, et les brebis se disperseront.
Yesu ya ce musu, “Dukanku za ku ja da baya ku bar ni, gama yana a rubuce cewa, “‘Zan bugi makiyayin tumaki, tumakin kuwa za su warwatse.’
28 Mais après que je serai ressuscité, je vous précéderai en Galilée.
Amma bayan na tashi, zan sha gabanku zuwa Galili.”
29 Pierre lui dit alors: Quand tous les autres se scandaliseraient de vous, moi, non.
Bitrus ya ce, “Ko da duka sun ja da baya suka bar ka, ba zan bar ka ba.”
30 Et Jésus lui repartit: En vérité je te le dis, aujourd’hui, cette nuit même, avant qu’un coq ait chanté deux fois, tu me renieras trois fois.
Yesu ya ce, “Gaskiya nake faɗa maka, yau, tabbatacce, a daren nan, kafin zakara yă yi cara sau biyukai da kanka za ka yi mūsun sanina sau uku.”
31 Mais Pierre insistait: Quand il me faudrait mourir avec vous, je ne vous renierai pas. Et tous disaient de même.
Amma Bitrus ya yi ta nanatawa da ƙarfi ya ce, “Ko da zan mutu tare da kai, ba zan taɓa yin mūsun saninka ba.” Duk sauran ma suka ce haka.
32 Etant venu à une maison de campagne nommée Gethsémani, il dit à ses disciples: Asseyez-vous ici pendant que je prierai.
Suka tafi wani wurin da ake kira Getsemane, Yesu ya kuma ce wa almajiransa, “Ku zauna a nan, yayinda ni kuwa in yi addu’a.”
33 Et il prit avec lui Pierre, Jacques et Jean, et il commença à s’effrayer et à tomber dans l’abattement.
Ya tafi tare da Bitrus, Yaƙub da kuma Yohanna. Sai ya fara baƙin ciki da damuwa ƙwarai.
34 Et il leur dit: Mon âme est triste jusqu’à la mort; demeurez ici et veillez.
Sai ya ce musu, “Raina yana cike da baƙin ciki har ma kamar zan mutu. Ku dakata a nan ku yi tsaro.”
35 Et, s’étant avancé un peu, il tomba la face contre terre, et il demandait que, s’il était possible, cette heure s’éloignât de lui.
Sai ya yi gaba kaɗan, ya fāɗi a ƙasa, ya yi addu’a, ya ce in mai yiwuwa ne, a ɗauke masa wannan sa’a.
36 Et il dit: Abba, Père, toutes choses vous sont possibles, éloignez ce calice de moi; toutefois, non ma volonté, mais la vôtre.
Ya ce, “Ya Abba, Uba, kome mai yiwuwa ne a gare ka. Ka ɗauke mini wannan kwaf. Amma ba abin da nake so ba, sai dai abin da kake so.”
37 Il revint ensuite, et, comme il les trouva dormant, il dit à Pierre: Simon, tu dors? Tu n’as pas pu veiller une heure?
Sai ya koma wajen almajiransa, ya same su suna barci. Ya ce wa Bitrus, “Siman, kana barci ne? Ka kāsa yin tsaro na sa’a ɗaya?
38 Veillez et priez, afin que vous n’entriez point en tentation. L’esprit est prompt, mais la chair est faible.
Ku yi tsaro, ku kuma yi addu’a, domin kada ku fāɗi cikin jarraba. Ruhu yana so, sai dai jiki raunana ne.”
39 Et, s’en allant de nouveau, il priait, disant les mêmes paroles.
Ya sāke komawa, ya maimaita addu’ar da ya yi.
40 Etant revenu, il les trouva encore dormant (car leurs yeux étaient appesantis), et ils ne savaient que lui répondre.
Da ya dawo, ya sāke tarar da su suna barci, domin barci ya cika musu ido. Suka rasa abin da za su ce masa.
41 Il vint une troisième fois et leur dit: Dormez maintenant et reposez-vous. C’est assez; l’heure est venue, voilà que le Fils de l’homme sera livré aux mains des pécheurs.
Da ya koma sau na uku, sai ya ce musu, “Har yanzu kuna barci, kuna hutawa ba? Ya isa! Lokaci ya yi. Duba an ba da Ɗan Mutum a hannun masu zunubi.
42 Levez-vous, allons; voici que celui qui me livrera approche.
Ku tashi! Mu tafi! Ga mai bashe ni ɗin yana zuwa!”
43 Jésus parlant encore. Judas Iscariote, l’un des douze, vint, et, avec lui, une grande troupe armée d’épées et de bâtons, et envoyée par les princes des prêtres, et par les scribes et les anciens.
Yana cikin magana ke nan, sai Yahuda, ɗaya daga cikin Sha Biyun ya bayyana. Ya zo tare da taro da suke riƙe da takuba da sanduna. Manyan firistoci da malaman dokoki, da kuma dattawa ne suka turo taron.
44 Or le traître leur avait donné un signe, disant: Celui que je baiserai, c’est lui-même, saisissez-le, et emmenez-le avec précaution.
Mai bashe shi ɗin ya riga ya shirya alama da su cewa, “Wanda na yi wa sumba, shi ne mutumin, ku kama shi, ku riƙe sosai.”
45 Etant donc venu, il s’approcha aussitôt de lui, disant: Maître, je vous salue; et il le baisa.
Nan da nan Yahuda ya je wurin Yesu ya ce, “Rabbi!” Ya kuma yi masa sumba.
46 Et eux mirent la main sur lui, et le saisirent.
Mutanen kuwa suka kama Yesu, suka riƙe shi.
47 Un de ceux qui étaient présents, tirant son épée, en frappa le serviteur du grand prêtre, et il lui coupa l’oreille.
Sai wani cikin waɗanda suke tsattsaye kusa ya zāre takobinsa, ya sare kunnen bawan babban firist.
48 Alors prenant la parole, Jésus leur dit: Vous êtes venus comme à un voleur, avec des épées et des bâtons, afin de me prendre.
Yesu ya ce, “Ina jagoran wani tawaye ne da kuka fito da takuba da kuma sanduna domin ku kama ni?
49 J’étais tous les jours parmi vous, enseignant dans le temple, et vous ne m’avez point pris; mais c’est pour que les Ecritures s’accomplissent.
Kowace rana ina tare da ku, ina koyarwa a filin haikali, ba ku kama ni ba. Amma dole a cika Nassi.”
50 Alors ses disciples l’abandonnant, s’enfuirent tous.
Sai kowa ya yashe shi ya gudu.
51 Un jeune homme le suivait, couvert seulement d’un linceul; ils se saisirent de lui.
Wani saurayin da ba ya sanye da kome sai rigar lilin, yana bin Yesu. Da suka yi ƙoƙarin kama shi,
52 Mais, laissant le linceul, il s’enfuit nu d’au milieu d’eux.
sai ya gudu ya bar rigarsa, ya gudu tsirara.
53 Cependant ils amenèrent Jésus chez le grand prêtre, où s’assemblèrent tous les prêtres, et les scribes, et les anciens.
Suka kai Yesu wajen babban firist, sai dukan manyan firistoci, dattawa da kuma malaman dokoki suka taru.
54 Pierre le suivit de loin jusque dans la cour du grand prêtre; et il était assis près du feu avec les serviteurs, et se chauffait.
Bitrus ya bi shi daga nesa, har cikin filin gidan babban firist. A can, ya zauna tare da masu gadi, yana jin ɗumin wuta.
55 Or les princes des prêtres et tout le conseil cherchaient un témoignage contre Jésus pour le faire mourir, et ils n’en trouvaient point.
Manyan firistoci da dukan’yan Majalisa, suka shiga neman shaidar laifin da za a tabbatar a kan Yesu, domin su kashe shi. Amma ba su sami ko ɗaya ba.
56 Car beaucoup témoignaient faussement contre lui; mais les témoignages ne s’accordaient point.
Da yawa suka ba da shaidar ƙarya a kansa, amma shaidarsu ba tă zo ɗaya ba.
57 Et quelques-uns, se levant, portaient contre lui un faux témoignage, disant:
Sai waɗansu suka miƙe tsaye, suka ba da wannan shaida ƙarya a kansa, suka ce,
58 Nous l’avons entendu dire: Je détruirai ce temple fait de main d’homme, et en trois jours j’en rebâtirai un autre non fait de main d’homme.
“Mun ji shi ya ce, ‘Zan rushe wannan haikali da mutum ya gina, cikin kwana uku, in sāke gina wani wanda ba ginin mutum ba.’”
59 Mais leur témoignage n’était pas uniforme.
Duk da haka ma, shaidarsu ba tă zo ɗaya ba.
60 Alors le grand prêtre se levant au milieu d’eux interrogea Jésus, disant: Tu ne réponds rien à ce que ceux-ci déposent contre toi?
Sai babban firist ya tashi a gabansu, ya tambayi Yesu ya ce, “Ba za ka amsa ba? Wane shaida ke nan waɗannan mutane suke kawowa a kanka?”
61 Mais Jésus se taisait, et il ne répondit rien. Le grand prêtre l’interrogea de nouveau et lui dit: Es-tu le Christ, le Fils du Dieu béni?
Amma Yesu ya yi shiru, bai kuwa amsa ba. Babban firist ya sāke tambayarsa ya ce, “Kai ne Kiristi, Ɗan Mai Albarka?”
62 Et Jésus lui dit: Je le suis; et vous verrez le Fils de l’homme assis à la droite de la majesté de Dieu, et venant sur les nuées du ciel.
Yesu ya ce, “Ni ne. Za ku kuwa ga Ɗan Mutum yana zaune a hannun dama na Mai Iko, yana kuma zuwa a cikin gizagizan sama.”
63 Alors le grand prêtre déchirant ses vêtements, dit: Qu’avons-nous encore besoin de témoins.
Babban firist ya yage tufafinsa, ya yi ce, “Ina dalilin neman waɗansu shaidu kuma?
64 Vous avez entendu le blasphème: que vous en semble? Tous le condamnèrent comme étant digne de mort.
Kun dai ji saɓon. Me kuka gani?” Duka suka yanke masa hukuncin kisa.
65 Aussitôt quelques-uns se mirent à cracher sur lui, à voiler sa face, à le déchirer à coups de poing et à lui dire: Prophétise! et les serviteurs le déchiraient de soufflets.
Sai waɗansu suka fara tattofa masa miyau, suka rufe masa idanu, suka bubbuge shi da hannuwansu, suka ce, “Yi annabci!” Masu gadin kuma suka ɗauke shi, suka yi masa duka.
66 Et pendant que Pierre était en bas dans la cour, vint une des servantes du grand prêtre;
Yayinda Bitrus yake ƙasa a filin gidan, sai wata yarinya, baiwa, ɗaya daga cikin ma’aikatan babban firist, ta zo can.
67 Et lorsqu’elle eut aperçu Pierre qui se chauffait, le regardant, elle dit: Toi aussi tu étais avec Jésus le Nazaréen.
Da ta ga Bitrus yana jin ɗumi, sai ta dube shi da kyau. Ta ce, “Kai ma kana tare da Yesu, Banazare.”
68 Mais il nia, disant: Je ne sais ni ne connais ce que tu veux dire. Et il sortit devant la cour, et un coq chanta.
Amma ya yi mūsu ya ce, “Ban san abin da kike magana ba, balle ma in fahimce ki.” Sai ya fita zuwa zaure.
69 Or la servante l’ayant encore vu, dit à ceux qui étaient présents: Celui-ci est un d’entre eux.
Da baiwar ta gan shi a can, sai ta sāke gaya wa waɗanda suke tsattsaye a wurin, ta ce, “Wannan mutum yana ɗaya daga cikinsu.”
70 Mais il le nia de nouveau. Et peu après ceux qui étaient là disaient à Pierre: Tu es certainement un d’entre eux, car tu es aussi Galiléen.
Sai ya sāke yin musu. Bayan ɗan lokaci kaɗan, sai waɗanda suke tsattsaye kusa suka ce wa Bitrus, “Lalle, kana ɗaya daga cikinsu, gama kai mutumin Galili ne.”
71 Alors il se mit à faire des imprécations et à jurer: Je ne connais point cet homme que vous dites.
Sai ya fara la’antar kansa, yana rantsuwa musu, yana cewa, “Ban san wannan mutumin da kuke magana a kai ba.”
72 Et aussitôt un coq chanta encore. Et Pierre se ressouvint de la parole que lui avait dite Jésus: Avant qu’un coq chante deux fois, tu me renieras trois fois. Et il se mit à pleurer.
Nan da nan zakara ya yi cara sau na biyu. Sai Bitrus ya tuna da maganar da Yesu ya yi masa cewa, “Kafin zakara yă yi cara sau biyu, za ka yi mūsun sanina sau uku.” Sai ya fashe da kuka.