< Marc 1 >

1 Commencement de l’Evangile de Jésus-Christ, fils de Dieu.
Wannan itace farkon bisharar Yesu Almasihu, Dan Allah.
2 Comme il est écrit dans le prophète Isaïe: Voilà que j’envoie mon ange devant votre face, lequel préparera votre voie devant vous.
kamar yadda aka rubuta cikin littafin annabi Ishaya. Duba, ina aika manzona, a gabanka, wanda zai shirya maka hanya.
3 Voix de quelqu’un qui crie dans le désert: Préparez la voie du Seigneur, faites droits ses sentiers.
Akwai murya mai kira a jeji, tana cewa ka shirya hanyar Ubangiji. ka daidaita ta.
4 Jean a été dans le désert, baptisant et prêchant le baptême de pénitence pour la rémission des péchés.
Yahaya ya zo, yana baptisma acikin jeji yana wa'azin tuba, domin gafarar zunubai.
5 Et tout le pays de Judée, et tous les habitants de Jérusalem allaient à lui; et ils étaient baptisés par lui dans le fleuve du Jourdain, confessant leurs péchés.
Dukan kasar Yahudiya da mutanen Urshalima suka zo wurin sa, a ka kuma yi masu baptisma a kogin urdun. suna furta zunubansu.
6 Or Jean était vêtu de poils de chameau, et d’une ceinture de cuir autour de ses reins; et il se nourrissait de sauterelles et de miel sauvage; et il prêchait, disant:
Yahaya yana saye da tufa ta gashin rakumi, yana kuma da damara ta fata a kugunsa, abincinsa fara ce da zuma.
7 Il vient après moi un plus puissant que moi; et je ne suis pas digne, me prosternant, de délier les cordons de sa chaussure.
Yana wa'azi, ya ce “akwai mai zuwa a bayana wanda ya ke da iko fiye da ni. wanda ko maballin takalminsa ban isa in kwance ba.
8 Moi je vous ai baptisés dans l’eau; mais lui vous baptisera dans l’Esprit-Saint.
Ni ina yi maku baptisma da ruwa, amma mai zuwa a bayana zai yi maku baptisma da Ruhu Mai Tsarki''.
9 Or il arriva qu’en ces jours-là Jésus vint de Nazareth, ville de Galilée, et qu’il fut baptisé par Jean dans le Jourdain.
Sai ya kasance a kwanakin nan Yesu ya zo daga Nazarat ta Galili, sai Yahaya ya yi masa baptisma a kogin urdun.
10 Et soudain, sortant de l’eau, il vit les deux ouverts, et l’Esprit descendant en forme de colombe, et se reposant sur lui.
Sa'adda Yesu ya fito daga ruwan, sai sama ta bude, sai Ruhu ya sauko a bisansa da kamanin kurciya.
11 Et une voix vint des cieux: Vous êtes mon fils bien-aimé; c’est en vous que j’ai mis mes complaisances.
Sai wata murya ta zo daga sama, tana cewa, “Kai kaunataccen Dana ne. zuciyata ta na murna da kai kwarai''.
12 Et aussitôt l’Esprit le poussa dans le désert.
Sai Ruhu ya iza shi zuwa jeji.
13 Et il passa dans le désert quarante jours et quarante nuits; et il fut tenté par Satan; et il était parmi les bêtes, et les anges le servaient.
Yana a jeji kwana arba'in, Shaidan yana jarabtar sa. Yana cikin jeji da dabobi, sai malaiku su ka yi masa hidima.
14 Mais après que Jean eut été livré, Jésus vint en Galilée, prêchant l’Evangile du royaume de Dieu,
Bayan da aka kama Yahaya, Yesu ya shiga kasar Galili yana wa'azin bisharar Allah.
15 Et disant: Parce que le temps est accompli, et que le royaume de Dieu est proche, faites pénitence et croyez à l’Evangile.
Yana cewa, “Lokaci ya yi, gama mulkin Allah ya kusato. Ku tuba ku bada gaskiya ga bishara”.
16 Or passant le long de la mer de Galilée, il vit Simon et André son frère, qui jetaient leurs filets dans la mer, car ils étaient pêcheurs;
Sa'adda ya ke wucewa a gefen takun Galili, sai ya ga Saminu da Andarawus, dan'uwansa suna jefa taru a teku, domin su masunta ne.
17 Et Jésus leur dit: Suivez-moi, et je vous ferai devenir pêcheurs d’hommes.
Yesu ya ce masu ku zo, ku biyo ni, ni kuwa sai in maisheku masuntan mutane”.
18 Et aussitôt, laissant leurs filets, ils le suivirent.
Nan da nan suka bar tarun su, suka bi shi.
19 De là s’étant un peu avancé, il vit Jacques fils de Zébédée, et Jean son frère, qui raccommodaient leurs filets dans leur barque:
Sa'adda Yesu ya yi tafiya kadan, sai ya ga Yakubu dan Zabadi da Yahaya dan'uwansa; suna gyaran tarunsu a jirgin ruwa.
20 Et au moment même, il les appela. Or laissant leur père Zébédée dans la barque avec les ouvriers, ils le suivirent.
Sai ya kira su, su kuwa suka bar mahaifinsu Zabadi a jirgin ruwan da ma'aikatansu, sai su ka bi shi.
21 Ils vinrent ensuite à Capharnaüm; et d’abord entrant le jour du sabbat dans la synagogue, il les instruisait.
Da su ka shigo cikin kafanahum, a ranar asabar, Yesu ya shiga majami'a ya koya masu.
22 Et ils s’étonnaient de sa doctrine; car il les enseignait comme ayant autorité, et non comme les scribes.
Su ka yi mamakin koyarwarsa, domin ya na koya masu da iko ba kamar marubuta ba.
23 Or il y avait dans leur synagogue un homme possédé d’un esprit impur, et il s’écria,
A nan cikin majami'a akwai wani mutum mai kazamin ruhu, sai ya yi ihu da karfi.
24 Disant: Qu’importe à nous et à vous, Jésus de Nazareth? Êtes-vous venu pour nous perdre? Je sais que vous êtes le saint de Dieu.
Yana cewa Ina ruwan mu da kai, Yesu Banazarat? Ka zo ne domin ka halakar da mu? Na san wanene kai. Kai ne Mai Tsarki na Allah”.
25 Et Jésus le menaça disant: Tais-toi et sors de cet homme.
Sai Yesu ya tsauta wa kazamin ruhun ya ce, “Ka yi shiru ka fita daga cikinsa”.
26 Alors l’esprit impur le déchirant, et criant d’une voix forte, sortit de lui.
Bayan da kazamin ruhun ya buga shi kasa, sai kazamin ruhun ya yi ihu sa'annan ya fita daga jikinsa.
27 Et ils furent tous saisis d’étonnement, de sorte qu’ils s’interrogeaient entre eux, disant: Qu’est ceci? quelle est cette doctrine nouvelle? Car il commande avec empire, même aux esprits impurs, et ils lui obéissent.
Sai dukan mutanen su ka yi mamaki kwarai, suna tambayar junansu menene wannan? wace sabuwar koyarwa ce da iko haka? har yana umartar kazaman ruhohi suna kuwa yi masa biyayya!”
28 Et sa renommée se répandit promptement dans tout le pays de Galilée.
Nan da nan labarinsa ya bazu ko'ina a dukkan kewayen kasar Galili.
29 Et aussitôt, sortant de la synagogue, ils vinrent dans la maison de Simon et d’André, avec Jacques et Jean.
Bayan da suka bar majami'a, sai su ka shiga gidan Saminu da Andarawus, suna kuma tare da Yakubu da Yahaya.
30 Or la belle-mère de Simon était au lit, ayant la fièvre: et incontinent ils lui parlèrent d’elle.
Surikar Saminu tana kwance ba lafiya tana fama da zazzabi. Sai suka gaya wa Yesu game da ita.
31 Alors s’approchant, il la fit lever en prenant sa main; et sur-le-champ la fièvre la quitta, et elle les servait.
Sai ya zo, ya kama hannunta, ya daga ta, sai zazzabin ya sake ta, ta fara yi masu hidima.
32 Cependant, le soir venu, lorsque le soleil fut couché, ils lui amenèrent tous les malades, et les démoniaques.
Da yamman nan, bayan da rana ta fadi, sai su ka kawo masa dukan marasa lafiya da masu fama da aljanu.
33 Et toute la ville était assemblée à la porte.
Dukan mutanen garin su ka taru a bakin kofa.
34 Et il guérit beaucoup de malades affligés de diverses infirmités, et il chassait beaucoup de démons; mais il ne leur permettait pas de dire qu’ils le connaissaient.
ya warkar da masu ciwo da yawa da masu chututtuka iri-iri, ya kuma fitar da bakaken aljanu, amma bai yarda aljanun su yi magana ba domin sun san shi.
35 Le lendemain, s’étant levé de grand matin, il sortit et s’en alla en un lieu désert, où il priait.
Ya tashi da sassafe, tun da sauran dare, ya tafi wurin da ba kowa, a can ya yi add'ua.
36 Simon et ceux qui étaient avec lui le suivirent.
Saminu da wandanda suke tare da shi suka neme shi.
37 Quand ils l’eurent trouvé, ils lui dirent: Tout le monde vous cherche.
Suka sa me shi, sai su ka ce masa, “kowa yana nemanka”.
38 Il leur répondit: Allons dans les villages et les villes voisines, afin que je prêche là aussi; car c’est pour cela que je suis venu.
Ya ce, bari mu tafi wani wuri, zuwa wadansu garuruwan da ke kewaye, Saboda in yi wa'azi a can kuma. Wannan shi yasa na zo nan''.
39 Il prêchait donc dans leurs synagogues et dans toute la Galilée; et il chassait les démons.
Ya tafi dukan kasar Galili, yana wa'azi a majimi'un su yana kuma fitar da aljanu.
40 Or un lépreux vint à lui, le suppliant et se jetant à genoux, il lui dit: Si vous voulez, vous pouvez me guérir.
Wani kuturu ya zo wurinsa. Yana rokonsa, ya durkusa. Ya ce masa, “in ka yarda kana iya warkar da ni.
41 Jésus, ému de compassion, étendit sa main, et le touchant, lui dit: Je le veux, sois guéri.
Sai ya yi juyayi, Yesu ya mi ka hannun sa ya ta ba shi ya na ce masa “Na yarda. Ka sarkaka”.
42 Lorsqu’il eut parlé, la lèpre disparut soudain de cet homme, et il fut guéri.
Nan da nan kuturtar ta barshi, ya kuma sa mu tsarkakewa.
43 Mais Jésus le renvoya aussitôt, le menaça,
Yesu ya yi masa gargadi sosai, ya salame shi.
44 Et lui dit: Garde-toi de rien dire à personne; mais va et montre-toi au prince des prêtres, et offre pour ta guérison ce que Moïse a ordonné, en témoignage pour eux.
Ya ce masa “ka tabbata fa kada ka gayawa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, sai ka je ka yi hadaya domin tsarkakewa kamar yadda Musa ya umurta, domin shaida.
45 Mais celui-ci étant parti, se mit à raconter et à publier partout ce qui s’était passé; de sorte que Jésus ne pouvait plus paraître publiquement dans la ville, mais qu’il se tenait dehors dans des lieux déserts; et l’on venait à lui de tous côtés.
Amma da ya fita sai ya fara gaya wa kowa, ya baza maganar a ko'ina, har Yesu bai iya tafiya a sake a garin ba. Ya tafi ya tsaya a wuraren da ba kowa, mutane kuwa su ka zo wurinsa daga ko'ina.

< Marc 1 >