< Luc 3 >
1 L’an quinzième du règne de César Tibère, Ponce Pilate étant gouverneur de la Judée, Hérode, tétrarque de Galilée, Philippe, son frère, tétrarque d’Iturée et du pays de Trachonite, et Lysanias tétrarque d’Abylène;
A cikin shekara ta goma sha biyar da Tibariyus Kaisar ke mulki, Bilatus Babunti kuma ke jagorar Yahudiya, Hirudus yana sarautar Galili, dan'uwansa Filibus yana sarautar yankin Ituriya da Tirakonitis, Lisaniyas kuma na sarautar yankin Abiliya,
2 Sous les grands prêtres Anne et Caïphe, la parole du Seigneur se fit entendre à Jean, fils de Zacharie, dans le désert.
kuma zamanin da Hanana da Kayafa suke manyan firistoci, maganar Allah ta zo wurin Yahaya dan Zakariya, a cikin jeji.
3 Et il vint dans toute la région du Jourdain, prêchant le baptême de pénitence pour la rémission des péchés.
Ya yi tafiya cikin dukan yankuna da ke kewaye da Kogin Urdun, yana wa'azin baftismar tuba domin gafarar zunubai.
4 Ainsi qu’il est écrit au livre des paroles du prophète Isaïe: Voix de quelqu’un qui crie dans le désert: Préparez la voie du Seigneur, faites droits ses sentiers:
Kamar yadda aka rubuta a cikin littafin annabi Ishaya, “Ga muryan wani yana kira a cikin jeji, 'Shirya hanyar Ubangiji, ka daidaita tafarkunsa!
5 Toute vallée sera comblée, et toute montagne et toute colline seront abaissées, les chemins tortueux deviendront droits, et les raboteux, unis;
Za a cika kowani kwari, za a fasa kowani dutse a kuma baje kowani tudu, za a mike karkatattun hanyoyi, za a cike hanyoyi masu gargada,
6 Et toute chair verra le salut de Dieu.
kuma dukan mutane za su ga ceton Allah.”
7 Ainsi il disait à ceux qui accouraient en foule pour être baptisés par lui: Race de vipères, qui vous a montré à fuir la colère à venir?
Sai Yahaya ya kara fada wa taron jama'ar da ke zuwa domin ya yi masu baftisma, “Ku 'ya'yan macizai masu dafi, wa ya gargadeku ku guje wa fushin nan mai zuwa?
8 Faites donc de dignes fruits de pénitence, et ne commencez pas par dire: Nous avons pour père Abraham. Car je vous dis que de ces pierres mêmes Dieu peut susciter des enfants à Abraham.
Ku ba da 'ya'ya da sun cancanci tuba, kada ku kuma fara cewa a cikinku, 'Muna da Ibrahim a matsayin Ubanmu', domin ina gaya maku, Allah yana iya ta da wa Ibrahim 'ya'ya daga cikin wadannan duwatsu.
9 Déjà la cognée a été mise à la racine des arbres. Tout arbre donc qui ne produit pas de bon fruit sera coupé et jeté au feu.
Yanzu kuwa, an rigaya an sa gatari a gindin itatuwa. Sabili da haka, duk itacen da bai ba da 'ya'ya masu kyau ba za a sare shi kasa a kuma jefa shi cikin wuta.”
10 Et la foule l’interrogeait, disant: Que ferons-nous donc?
Sai mutanen da ke cikin taron jama'ar suka tambaye shi cewa, “To me za mu yi?”
11 Et répondant, il leur disait: Que celui qui a deux tuniques en donne une à celui qui n’en a point, et que celui qui a de quoi manger fasse de même.
Ya amsa ya ce masu, “Idan wani yana da taguwa biyu, sai ya ba wanda bashi da ita daya, kuma wanda yake da abinci ya yi haka nan.”
12 Des publicains vinrent aussi pour être baptisés, et lui demandèrent: Maître, que ferons-nous?
Masu karban haraji ma suka zo domin a yi masu baftisma, suka ce masa, “Malam, me za mu yi?”
13 Et il leur répondit: Ne faites rien de plus que ce qui vous a été prescrit.
Ya ce masu, “Kada ku karba kudi fiye da yadda aka umarce ku.”
14 Et des soldats aussi l’interrogeaient, disant: Et nous, que ferons-nous? Et il leur dit: N’usez de violence ni de fraude envers personne, et contentez-vous de votre paye.
Wasu sojoji ma suka tambaye shi cewa, “To, mu fa? Yaya za mu yi?” Ya ce masu, “Kada ku kwace wa wani kudi, kada ku kuma yi wa wani zargin karya. Ku dogara ga albashinku.”
15 Or le peuple croyait et tous pensaient en leurs cœurs que Jean pourrait bien être le Christ.
Ana nan da mutane ke sauraron zuwan Almasihu, kowa yana ta tunani a zuciyar sa game da Yahaya, ko shi ne Almasihu.
16 Jean répondit, disant à tous: Pour moi, je vous baptise dans l’eau; mais viendra un plus puissant que moi, de la chaussure de qui je ne suis pas digne de délier la courroie: lui vous baptisera dans l’Esprit-Saint et le feu;
Yahaya ya amsa ya ce masu duka, “Game da ni dai, na yi maku baftisma da ruwa, amma akwai wani tafiye wanda ya fi ni iko, ban ma isa in kwance maballin takalmansa ba. Shi zai yi maku baftisma da Ruhu Mai Tsarki da kuma wuta.
17 Son van est en sa main, et il nettoiera son aire, puis il rassemblera le froment dans son grenier, et brûlera la paille dans un feu qui ne peut s’éteindre.
Kwaryar shikarsa na hanun sa domin ya share masussukarsa da kyau ya kuma tara alkama a cikin rumbunsa. Amma zai kona buntun da wuta marar mutuwa.
18 C’est ainsi qu’en lui apprenant beaucoup d’autres choses, il évangélisait le peuple.
Da gargadi masu yawa ya yi wa mutanen wa'azin bishara.
19 Mais comme il reprenait Hérode le tétrarque, au sujet d’Hérodiade, femme de son frère, et à cause de tous les maux qu’il avait faits,
Yahaya kuma ya tsauta wa sarki Hirudus domin ya auri matar dan'uwansa, Hiruduya, da kuma sauran abubuwan da Hirudus ya yi.
20 Hérode ajouta encore celui-ci à tous les autres, il fit mettre Jean en prison.
Amma Hirudus ya kara yin wani mugun abu. Ya sa an kulle Yahaya a cikin kurkuku.
21 Or il arriva que, comme tout le peuple recevait le baptême, et que Jésus ayant été baptisé, priait, le ciel s’ouvrit;
Ana nan, lokacin da ake yiwa dukan mutane baftisma, aka yiwa Yesu mai baftisma. Lokacin da yake yin addu'a, sai sama ta bude,
22 Et l’Esprit-Saint descendit sur lui sous la forme sensible d’une colombe; et une voix vint du ciel: Vous êtes mon fils bien-aimé; c’est en vous que j’ai mis mes complaisances.
kuma Ruhu Mai Tsarki ya sauko masa a kamanin kurciya, sai wata murya ta fito daga sama, “Kai ne kaunataccen Da na. Ina jin dadin ka.”
23 Or Jésus avait, quand il commença son ministère, environ trente ans, étant, comme l’on croyait, fils de Joseph, qui le fut d’Héli, qui le fut de Mathat.
Ana nan Yesu da kansa, da ya fara, yana kimanin shekara talatin. Shi dan (kamar yadda ake tsammani) Yusufu ne, dan Heli,
24 Qui le fut de Lévi, qui le fut de Melchi, qui le fut de Janné, qui le fut de Joseph,
dan Matat, dan Lawi, dan Malki, dan Yanna, dan Yusufu,
25 Qui le fut de Mathathias, qui le fut d’Amos, qui le fut de Nahum, qui le fut de Hesli, qui le fut de Naggé,
dan Matatiya, dan Amos, dan Nahum, dan Hasli, dan Najjaya,
26 Qui le fut de Mahath, qui le fut de Mathathias, qui le fut de Séméi, qui le fut de Joseph, qui le fut de Juda,
dan Ma'ata, dan Matatiya, dan Shimeya, dan Yuseka, dan Yoda,
27 Qui le fut de Joanna, qui le fut de Réza, qui le fut de Zorobabel, qui le fut de Salathiel, qui le fut de Néri,
dan Yowana, dan Resa, dan Zarubabila, dan Shiyaltiyel, dan Niri,
28 Qui le fut de Melchi, qui le fut d’Addi, qui le fut de Cosan, qui le fut d’Elmadan, qui le fut de Her,
dan Malki, dan Addi, dan Kosama, dan Almadama, dan Er,
29 Qui le fut de Jésu, qui le fut d’Eliézer, qui le fut de Jorim, qui le fut de Mathat, qui le fut de Lévi,
dan Yosi, dan Aliyeza, dan Yorima, dan Matat, dan Lawi,
30 Qui le fut de Siméon, qui le fut de Juda, qui le fut de Joseph, qui le fut de Jona, qui le fut d’Eliakim,
dan Saminu, dan Yahuda, dan Yusufu, dan Yonana, dan Aliyakima,
31 Qui le fut de Méléa, qui le fut de Menna, qui le fut de Mathatha, qui le fut de Nathan, qui le fut de David,
dan Malaya, dan Mainana, dan Matata, dan Natan, dan Dauda,
32 Qui le fut de Jessé, qui le fut d’Obed, qui le fut de Booz, qui le fut de Salmon, qui le fut de Naasson,
dan Yesse, dan Obida, dan Bu'aza, dan Salmon, dan Nashon,
33 Qui le fut d’Aminadab, qui le fut d’Aram, qui le fut d’Esron, qui le fut de Pharès, qui le fut de Juda,
dan Amminadab, dan Adimi, dan Arama, dan Hezruna, dan Feresa, dan Yahuda,
34 Qui le fut de Jacob, qui le fut d’Isaac, qui le fut d’Abraham, qui le fut de Tharé, qui le fut de Nachor,
dan Yakubu, dan Ishaku, dan Ibrahim, dan Tera, dan Nahor,
35 Qui le fut de Sarug, qui le fut de Ragaü, qui le fut de Phaleg, qui le fut d’Héber, qui le fut de Salé,
dan Serug, dan Reyu, dan Feleg, dan Abiru, dan Shela,
36 Qui le fut de Caïnan, qui le fut d’Arphaxad, qui le fut de Sem, qui le fut de Noé, qui le fut de Lamech,
dan Kainana, dan Arfakshada, dan Shem, dan Nuhu, dan Lamek,
37 Qui le fut de Mathusalé, qui le fut d’Hénoch, qui le fut de Jared, qui le fut de Malaléel, qui le fut de Caïnan,
dan Metusela, dan Anuhu, dan Yaret, dan Mahalel, dan Kainana,
38 Qui le fut d’Hénos, qui le fut de Seth, qui le fut d’Adam, qui fut de Dieu.
dan Enosh, dan Shitu, dan Adamu, dan Allah.