< Luc 3 >

1 L’an quinzième du règne de César Tibère, Ponce Pilate étant gouverneur de la Judée, Hérode, tétrarque de Galilée, Philippe, son frère, tétrarque d’Iturée et du pays de Trachonite, et Lysanias tétrarque d’Abylène;
A shekara ta goma sha biyar ta mulkin Kaisar Tiberiyus, a lokacin Buntus Bilatus ne gwamnar Yahudiya, Hiridus kuma yana sarautar Galili, ɗan’uwansa Filibus yana sarautar Ituriya da Tarakunitis, Lisaniyas kuma yana sarautar Abiline.
2 Sous les grands prêtres Anne et Caïphe, la parole du Seigneur se fit entendre à Jean, fils de Zacharie, dans le désert.
A lokacin ne Annas da Kayifas suke manyan firistoci. Sai maganar Allah ta zo wa Yohanna, ɗan Zakariya a hamada.
3 Et il vint dans toute la région du Jourdain, prêchant le baptême de pénitence pour la rémission des péchés.
Ya zaga dukan ƙasar da take kewaye da Urdun, yana wa’azin baftismar tuba don gafarar zunubai.
4 Ainsi qu’il est écrit au livre des paroles du prophète Isaïe: Voix de quelqu’un qui crie dans le désert: Préparez la voie du Seigneur, faites droits ses sentiers:
Kamar yadda yake a rubuce a littafin annabi Ishaya. “Muryar mai kira a hamada, ‘Ku shirya wa Ubangiji hanya, ku miƙe hanyoyi dominsa.
5 Toute vallée sera comblée, et toute montagne et toute colline seront abaissées, les chemins tortueux deviendront droits, et les raboteux, unis;
Za a cike kowane kwari, a farfashe kowane dutse da kowane tudu. Za a miƙe hanyoyin da suka karkace, a gyaggyara hanyoyi masu gargaɗa su zama sumul.
6 Et toute chair verra le salut de Dieu.
Dukan’yan Adam kuwa za su ga ceton Allah!’”
7 Ainsi il disait à ceux qui accouraient en foule pour être baptisés par lui: Race de vipères, qui vous a montré à fuir la colère à venir?
Yohanna ya ce wa taron da suke zuwa domin yă yi musu baftisma, “Ku macizai! Wa ya gargaɗe ku, ku guje wa fushin nan mai zuwa?
8 Faites donc de dignes fruits de pénitence, et ne commencez pas par dire: Nous avons pour père Abraham. Car je vous dis que de ces pierres mêmes Dieu peut susciter des enfants à Abraham.
Ku yi ayyukan da suka dace da tuba. Kada ma ku yi tunani za ku iya ce wa kanku, ‘Ai, muna da mahaifinmu Ibrahim.’ Ina gaya muku cewa daga cikin duwatsun nan Allah zai iya tā da’ya’ya wa Ibrahim.
9 Déjà la cognée a été mise à la racine des arbres. Tout arbre donc qui ne produit pas de bon fruit sera coupé et jeté au feu.
An riga an sa bakin gatari a gindin itatuwa, kuma duk itacen da bai ba da’ya’ya masu kyau ba, za a sare shi a jefa cikin wuta.”
10 Et la foule l’interrogeait, disant: Que ferons-nous donc?
Sai taron suka tambaye shi, suka ce “Me za mu yi ke nan?”
11 Et répondant, il leur disait: Que celui qui a deux tuniques en donne une à celui qui n’en a point, et que celui qui a de quoi manger fasse de même.
Ya amsa ya ce, “Ya kamata, mutumin da yake da riguna biyu, yă raba da wanda ba shi da riga, mai abinci kuma yă yi haka.”
12 Des publicains vinrent aussi pour être baptisés, et lui demandèrent: Maître, que ferons-nous?
Masu karɓar haraji ma suka zo, domin a yi musu baftisma. Suka yi tambaya, suka ce “Malam, me ya kamata mu yi?”
13 Et il leur répondit: Ne faites rien de plus que ce qui vous a été prescrit.
Ya ce musu, “Kada ku karɓa fiye da abin da aka ce a karɓa.”
14 Et des soldats aussi l’interrogeaient, disant: Et nous, que ferons-nous? Et il leur dit: N’usez de violence ni de fraude envers personne, et contentez-vous de votre paye.
Sai waɗansu sojoji suka tambaye shi, “Mu fa? Me ya kamata mu yi?” Sai ya amsa ya ce, “Kada ku ƙwace kuɗin mutane, kada kuma ku yi shaidar ƙarya. Ku yi haƙuri da abin da ake biyanku.”
15 Or le peuple croyait et tous pensaient en leurs cœurs que Jean pourrait bien être le Christ.
Mutane suka zuba ido, suna kuma tunani a zuciyarsu, ko Yohanna ne Kiristi wanda ake sauraron zuwansa.
16 Jean répondit, disant à tous: Pour moi, je vous baptise dans l’eau; mais viendra un plus puissant que moi, de la chaussure de qui je ne suis pas digne de délier la courroie: lui vous baptisera dans l’Esprit-Saint et le feu;
Yohanna ya amsa musu duka ya ce, “Ina muku baftisma da ruwa. Amma wani wanda ya fi ni iko yana zuwa, ban ma isa in kunce igiyar takalmansa ba. Shi zai yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki da wuta kuma.
17 Son van est en sa main, et il nettoiera son aire, puis il rassemblera le froment dans son grenier, et brûlera la paille dans un feu qui ne peut s’éteindre.
Matankaɗinsa yana a hannunsa don yă tankaɗe sussukarsa ya kuma tattara alkama cikin rumbunsa, amma zai ƙone yayin da wutar da ba a iya kashewa.”
18 C’est ainsi qu’en lui apprenant beaucoup d’autres choses, il évangélisait le peuple.
Da kalmomi masu yawa Yohanna ya yi wa mutane gargaɗi, ya kuma yi musu wa’azin bishara.
19 Mais comme il reprenait Hérode le tétrarque, au sujet d’Hérodiade, femme de son frère, et à cause de tous les maux qu’il avait faits,
Amma da Yohanna ya tsawata wa Hiridus mai mulki saboda Hiridiyas, matar ɗan’uwansa, da kuma dukan sauran mugayen abubuwan da ya yi,
20 Hérode ajouta encore celui-ci à tous les autres, il fit mettre Jean en prison.
Hiridus dai ya ƙara ɓata al’amarin. Ya sa a kulle Yohanna a kurkuku.
21 Or il arriva que, comme tout le peuple recevait le baptême, et que Jésus ayant été baptisé, priait, le ciel s’ouvrit;
Sa’ad da ake wa dukan mutane baftisma, sai aka yi wa Yesu shi ma. Da yana cikin addu’a, sai sama ya buɗe,
22 Et l’Esprit-Saint descendit sur lui sous la forme sensible d’une colombe; et une voix vint du ciel: Vous êtes mon fils bien-aimé; c’est en vous que j’ai mis mes complaisances.
Ruhu Mai Tsarki kuma ya sauko masa a wata siffa, kamar kurciya. Sai murya ta fito daga sama, ta ce, “Kai ne Ɗana, wanda nake ƙauna, kai ne kuma kana faranta mini zuciya ƙwarai.”
23 Or Jésus avait, quand il commença son ministère, environ trente ans, étant, comme l’on croyait, fils de Joseph, qui le fut d’Héli, qui le fut de Mathat.
To, Yesu kansa yana da shekaru kusan talatin da haihuwa sa’ad da ya fara aikinsa. An ɗauka shi ɗan Yusuf ne, ɗan Heli,
24 Qui le fut de Lévi, qui le fut de Melchi, qui le fut de Janné, qui le fut de Joseph,
ɗan Mattat, ɗan Lawi, ɗan Melki, ɗan Yannai, ɗan Yusuf,
25 Qui le fut de Mathathias, qui le fut d’Amos, qui le fut de Nahum, qui le fut de Hesli, qui le fut de Naggé,
ɗan Mattatiyas, ɗan Amos, ɗan Nahum, ɗan Esli, ɗan Naggai,
26 Qui le fut de Mahath, qui le fut de Mathathias, qui le fut de Séméi, qui le fut de Joseph, qui le fut de Juda,
ɗan Ma’at, ɗan Mattatiyas, ɗan Semeyin, ɗan Yosek, ɗan Yoda,
27 Qui le fut de Joanna, qui le fut de Réza, qui le fut de Zorobabel, qui le fut de Salathiel, qui le fut de Néri,
ɗan Yowanan, ɗan Resa, ɗan Zerubbabel, ɗan Sheyaltiyel, ɗan Neri,
28 Qui le fut de Melchi, qui le fut d’Addi, qui le fut de Cosan, qui le fut d’Elmadan, qui le fut de Her,
ɗan Melki, ɗan Addi, ɗan Kosam, ɗan Elmadam, ɗan Er,
29 Qui le fut de Jésu, qui le fut d’Eliézer, qui le fut de Jorim, qui le fut de Mathat, qui le fut de Lévi,
ɗan Yoshuwa, ɗan Eliyezer, ɗan Yorim, ɗan Mattat, ɗan Lawi,
30 Qui le fut de Siméon, qui le fut de Juda, qui le fut de Joseph, qui le fut de Jona, qui le fut d’Eliakim,
ɗan Simeyon, ɗan Yahuda, ɗan Yusuf, ɗan Yonam, ɗan Eliyakim,
31 Qui le fut de Méléa, qui le fut de Menna, qui le fut de Mathatha, qui le fut de Nathan, qui le fut de David,
ɗan Meleya, ɗan Menna, ɗan Mattata, ɗan Natan, ɗan Dawuda,
32 Qui le fut de Jessé, qui le fut d’Obed, qui le fut de Booz, qui le fut de Salmon, qui le fut de Naasson,
ɗan Yesse, ɗan Obed, ɗan Bowaz, ɗan Salmon, ɗan Nashon,
33 Qui le fut d’Aminadab, qui le fut d’Aram, qui le fut d’Esron, qui le fut de Pharès, qui le fut de Juda,
ɗan Amminadab, ɗan Ram, ɗan Hezron, ɗan Ferez, ɗan Yahuda,
34 Qui le fut de Jacob, qui le fut d’Isaac, qui le fut d’Abraham, qui le fut de Tharé, qui le fut de Nachor,
ɗan Yaƙub, ɗan Ishaku, ɗan Ibrahim, ɗan Tera, ɗan Nahor,
35 Qui le fut de Sarug, qui le fut de Ragaü, qui le fut de Phaleg, qui le fut d’Héber, qui le fut de Salé,
ɗan Serug, ɗan Reyu, ɗan Feleg, ɗan Eber, ɗan Sala,
36 Qui le fut de Caïnan, qui le fut d’Arphaxad, qui le fut de Sem, qui le fut de Noé, qui le fut de Lamech,
ɗan Kainan, ɗan Arfakshad, ɗan Shem, ɗan Nuhu, ɗan Lamek,
37 Qui le fut de Mathusalé, qui le fut d’Hénoch, qui le fut de Jared, qui le fut de Malaléel, qui le fut de Caïnan,
ɗan Metusela, ɗan Enok, ɗan Yared, ɗan Mahalalel, ɗan Kainan,
38 Qui le fut d’Hénos, qui le fut de Seth, qui le fut d’Adam, qui fut de Dieu.
ɗan Enosh, ɗan Shitu, ɗan Adamu, ɗan Allah.

< Luc 3 >