< Luc 20 >

1 Or il arriva qu’un de ces jours-là, comme il enseignait le peuple dans le temple, et qu’il annonçait l’Evangile, les princes des prêtres et les scribes y vinrent avec les anciens,
Wata rana da Yesu yana koyar da mutane, yana musu wa’azin bishara a filin haikalin, sai manyan firistoci da malaman dokoki, tare da dattawan suka zo wurinsa.
2 Et lui adressèrent la parole en disant: Dis-nous par quelle autorité tu fais ces choses? ou: Qui est celui qui t’a donné ce pouvoir?
Suka ce masa, “Gaya mana, da wane iko kake yin waɗannan abubuwa. Wa ya ba ka wannan ikon?”
3 Et Jésus répondant, leur dit: Je vous interrogerai, moi aussi, mais sur une seule chose. Répondez-moi.
Ya amsa ya ce, “Ni ma zan yi muku wata tambaya. Ku faɗa mini,
4 Le baptême de Jean était-il du ciel ou des hommes?
baftismar Yohanna, daga sama ne ta fito, ko kuwa daga wurin mutane ne?”
5 Mais ils pensaient en eux-mêmes, disant: Si nous répondons: Du ciel, il dira: Pourquoi donc n’y avez-vous point cru?
Sai suka yi shawara da junansu, suka ce, “In muka ce, ‘Daga sama ne,’ zai tambaya, ‘To, don me ba ku gaskata shi ba?’
6 Et si nous répondons: Des hommes, tout le peuple nous lapidera, car ils tiennent pour certain que Jean était prophète.
Amma in kuma muka ce, ‘Daga mutane ne,’ dukan mutanen za su jajjefe mu da duwatsu, domin sun tabbata cewa, Yohanna annabi ne.”
7 Ils répondirent donc qu’ils ne savaient d’où il était.
Don haka, sai suka amsa cewa, “Ba mu san inda ta fito ba.”
8 Et Jésus leur dit: Ni moi, je ne vous dis pas non plus par quelle autorité je fais ces choses.
Yesu ya ce, “To, ni ma ba zan gaya muku, ko da wane iko ne, nake yin waɗannan abubuwa ba.”
9 Alors il se mit à dire au peuple cette parabole: Un homme planta une vigne, et la loua à des vignerons, et lui-même fut longtemps en voyage.
Sai ya ci gaba da gaya wa mutanen wannan misali ya ce, “Wani mutum ya yi gonar inabi, sai ya ba da hayarta ga waɗansu manoma, sa’an nan ya yi wata doguwar tafiya.
10 Et dans la saison, il envoya un de ses serviteurs aux vignerons, pour qu’ils lui donnassent du fruit de la vigne. Mais eux, après l’avoir déchiré de coups, le renvoyèrent les mains vides.
A lokacin girbi, sai ya aiki bawa zuwa wurin masu hayan, don su ba shi daga cikin’ya’yan inabin. Amma’yan hayan suka yi wa bawan nan dūka, suka kore shi hannu wofi.
11 Il envoya encore un autre serviteur. Mais eux, l’ayant aussi déchiré de coups et chargé d’outrages, ils le renvoyèrent les mains vides.
Ya sāke aikan wani bawa, shi ma suka yi masa dūka, suka kunyata shi, suka kuma kore shi hannu wofi.
12 Enfin il en envoya un troisième; les vignerons le blessèrent aussi et le jetèrent dehors.
Har yanzu, ya sāke aikan na uku, amma suka ji masa rauni, suka jefar da shi waje.
13 Alors le maître de la vigne dit: Que ferai-je? J’enverrai mon fils bien-aimé; peut être que lorsqu’ils le verront, ils le respecteront.
“Sai mai gonar inabin ya ce, ‘Me zan yi? Zan aiki ɗana da nake ƙauna, wataƙila za su girmama shi.’
14 Mais les vignerons l’ayant vu, pensèrent en eux-mêmes, disant: Celui-ci est l’héritier, tuons-le, afin que nôtre devienne l’héritage.
“Amma da’yan hayan suka gan shi, sai suka tattauna zancen, suka ce, ‘Wannan shi ne magājin, mu kashe shi sa’an nan gādon zai zama namu!’
15 Et l’ayant jeté hors de la vigne, ils le tuèrent. Que leur fera donc le maître de la vigne?
Sai suka fitar da shi waje, suka kashe shi. “To, me mai gonar inabin zai yi da su?
16 Il viendra, et perdra ces vignerons, et donnera la vigne à d’autres. Ce qu’ayant entendu, ils lui dirent: À Dieu ne plaise!
Zai zo ya karkashe masu hayan nan, ya ba wa waɗansu gonar inabin.” Da mutanen suka ji wannan, sai suka ce, “Allah ya sawwaƙa!”
17 Mais Jésus les regardant dit: Qu’est-ce donc que ce qui est écrit: La pierre qu’ont rejetée ceux qui bâtissaient est devenue un sommet d’angle?
Yesu ya zura musu ido ya ce, “To, mene ne ma’anar abin da aka rubuta cewa, “‘Dutsen da magina suka ƙi, shi ne kuwa ya zama dutsen kan ginin’
18 Quiconque tombera sur cette pierre sera brisé, et celui sur qui elle tombera, elle le réduira en poudre.
Duk wanda ya fāɗi a kan dutsen nan, zai kakkarye. Kuma in dutsen nan ya fāɗi a kan wani, zai murƙushe shi.”
19 Et les princes des prêtres et les scribes cherchaient à mettre la main sur lui en cette heure-là, mais ils craignirent le peuple; ils avaient compris que c’étaient à eux qu’il avait appliqué cette parabole.
Malaman dokoki da manyan firistoci, suka nemi hanyar kama shi nan da nan, domin sun san cewa, ya yi wannan misali a kansu ne, amma suna jin tsoron mutane.
20 Et, l’épiant, ils envoyèrent des gens qui feignaient d’être justes, pour lui tendre des embûches et le surprendre dans ses paroles, afin de le livrer au magistrat et au pouvoir du gouverneur.
Sai suka sa masa ido, suka aiki’yan leƙen asiri, waɗanda suka nuna kamar su masu gaskiya ne, suna nufin su kama shi game da abin da zai faɗa, domin su ba da shi ga gwamna mai mulki, da mai iko.
21 Ainsi ils l’interrogèrent disant: Maître, nous savons que vous parlez et enseignez avec droiture; que vous ne faites acception de personne, mais que vous enseignez la voix de Dieu dans la vérité:
Sai’yan leƙen asirin suka tambaye shi, suka ce, “Malam, mun sani kana faɗin, kuma kana koyar da abin da yake daidai, ba ka kuma nuna bambanci, amma kana koyar da hanyar Allah bisa ga gaskiya.
22 Nous est-il permis de payer le tribut à César, ou non?
Daidai ne mu biya haraji ga Kaisar, ko babu?”
23 Considérant leur ruse, il leur dit: Pourquoi me tentez-vous?
Ya gane makircinsu, sai ya ce musu,
24 Montrez-moi un denier. De qui porte-t-il l’image et l’inscription? Ils lui répondirent: De César.
“Nuna mini dinari. Hoton wane ne, kuma rubutun wane ne a kai?” Suka amsa, “Na Kaisar.”
25 Et il leur dit: Rendez donc à César ce qui est à César, et à Dieu ce qui est à Dieu.
Sai ya ce musu, “Ku ba wa Kaisar abin da yake na Kaisar, ku kuma ba wa Allah abin da yake na Allah.”
26 Et ils ne purent reprendre aucune de ses paroles devant le peuple; mais ils admirèrent sa réponse, et se turent.
Ba su iya kama shi a kan abin da ya faɗa a fili ba. Amsarsa ya ba su mamaki, shi ya sa suka yi shiru.
27 Quelques-uns des sadducéens, qui nient qu’il y ait une résurrection, s’approchèrent alors et l’interrogèrent;
Waɗansu Sadukiyawa da suke cewa, ba tashin matattu, suka zo wurin Yesu da tambaya cewa,
28 Disant: Maître, Moïse a écrit pour nous: Si le frère de quelqu’un meurt, ayant une femme, mais étant sans enfants, que son frère prenne sa femme et suscite une postérité à son frère.
“Malam, Musa ya rubuta mana cewa, ‘In ɗan’uwan wani mutum ya mutu, ya bar mata amma ba’ya’ya, dole mutumin ya aure gwauruwar, ya samo wa ɗan’uwansa’ya’ya.’
29 Or il y avait sept frères; et le premier prit une femme, et mourut sans enfants.
To, an yi waɗansu’yan’uwa bakwai. Na fari ya auri wata mace, ya mutu ba’ya’ya.
30 Le suivant prit la femme, et mourut lui-même sans enfants.
Na biyun,
31 Et le troisième la prit; et pareillement tous les sept, et ils n’ont point laissé de postérité, et ils sont morts.
da na ukun suka aure ta. Haka nan dukansu bakwai suka mutu babu’ya’ya.
32 Enfin, après eux tous, est morte aussi la femme.
A ƙarshe, ita macen ma ta mutu.
33 À la résurrection donc, duquel sera-t-elle femme, puisque les sept l’ont eue pour femme?
Shin, a tashin matattu, matar wa za tă zama? Tun da su bakwan nan, sun aure ta.”
34 Jésus leur dit: Les fils de ce siècle se marient et sont donnés en mariage; (aiōn g165)
Yesu ya amsa ya ce, “Mutanen zamanin nan suna aure, suna kuma ba da aure, (aiōn g165)
35 Mais ceux qui seront trouvés dignes du siècle à venir et de la résurrection des morts, ne se marieront point et n’épouseront point de femmes; (aiōn g165)
amma su waɗanda aka ga sun cancantar kasancewa a zamanin can, da kuma na tashin matattu, ba za su yi aure, ko su ba da aure ba. (aiōn g165)
36 Car ils ne pourront plus mourir; parce qu’ils sont égaux aux anges, et fils de Dieu, étant fils de la résurrection.
Kuma ba za su sāke mutuwa ba, gama su kamar mala’iku ne. Su’ya’yan Allah ne, tun da su’ya’yan tashin matattu ne.
37 Or que les morts ressuscitent, Moïse le montre à l’endroit du buisson, quand il appelle le Seigneur, le Dieu d’Abraham, le Dieu d’Isaac et le Dieu de Jacob.
Amma bisa ga labari na bishiya nan, mai cin wuta da Musa ya gani a jeji, ko Musa ma, ya nuna cewa, matattu suna tashi. Gama ya kira Ubangiji, ‘Allah na Ibrahim, da Allah na Ishaku, da kuma Allah na Yaƙub.’
38 Or Dieu n’est point le Dieu des morts, mais des vivants; car tous vivent pour lui.
Shi ba Allah na matattu ba ne, amma na masu rai ne, gama a gare shi, duka na da rai.”
39 Quelques-uns des scribes, prenant la parole, lui dirent: Maître, vous avez bien dit.
Sai waɗansu malaman dokoki suka amsa suka ce, “Ka faɗi daidai, malam!”
40 Et on n’osait plus lui faire aucune question.
Kuma ba wanda ya sami ƙarfin halin yin masa waɗansu tambayoyi.
41 Mais il leur demanda: Comment dit-on que le Christ est fils de David?
Sai Yesu ya ce musu, “Yaya suke cewa, ‘Kiristi ɗan Dawuda ne?’
42 Puisque David lui-même dit dans le livre des Psaumes: Le Seigneur a dit à mon Seigneur: Asseyez-vous à ma droite,
Dawuda da kansa ya faɗa a cikin Zabura, “‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana,
43 Jusqu’à ce que je fasse de vos ennemis l’escabeau de vos pieds.
sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.”’
44 Ainsi David l’appelle son Seigneur; comment donc est-il son fils?
Dawuda ya kira shi ‘Ubangiji.’ Ta, yaya zai zama ɗansa?”
45 Or tout le peuple l’écoutant, il dit à ses disciples:
Yayinda dukan mutane suna cikin sauraronsa, sai Yesu ya ce wa almajiransa,
46 Gardez-vous des scribes, qui se plaisent à se promener avec de longues robes, aiment les salutations dans les places publiques, les premiers sièges dans les synagogues, et les premières places dans les festins;
“Ku yi hankali da malaman dokoki. Sukan so sa manyan riguna suna zaga, suna sha’awan karɓan gaisuwa a wuraren kasuwanci, da kuma wuraren zama mafi daraja a majami’u, da wuraren bangirma a bukukkuwa.
47 Qui dévorent les maisons des veuves sous prétexte de longues prières. Ceux-ci subiront une condamnation plus rigoureuse.
Suna mamaye gidajen gwauraye, kuma don burga, suna dogayen addu’o’i. Ga irin waɗannan mutane, za a yi musu hukunci mai tsanani sosai.”

< Luc 20 >