< Luc 15 >

1 Or les publicains et les pécheurs s’approchaient de Jésus pour l’entendre.
To sai duk masu karbar haraji da masu zunubi suna ta zuwa wurin Yesu suna sauraronsa.
2 Et les pharisiens et les scribes murmuraient, disant: Celui-ci accueille les pécheurs et mange avec eux.
Dukan Farisawa da Marubuta suna ta gunaguni da junansu, cewa, “Wannan mutum yana karbar masu zunubi, har ma tare suke cin abinci.”
3 Et il leur proposa cette parabole, disant:
Yesu ya fadi wannan misali, ya ce,
4 Quel est celui d’entre vous qui a cent brebis, et qui, s’il en perd une, ne laisse les quatre vingt-dix-neuf autres dans le désert, et ne va après celle qui est perdue, jusqu’à ce qu’il la trouve?
“Idan waninku yana da tumaki dari, sai dayarsu ta bace, wato ba zai bar tasa'in da taran nan a makiyaya, ya bi sawun wadda ta bata gudan nan har sai ya same shi ba?
5 Et lorsqu’il l’a trouvée, il la met sur ses épaules, plein de joie;
Idan kuwa ya same ta, sai ya dauke ta a kafadarsa yana farin ciki.
6 Et, venant à sa maison, il appelle ses amis et ses voisins, leur disant: Réjouissez-vous avec moi, parce que j’ai trouvé ma brebis qui était perdue.
In ya dawo gida, sai ya kira abokansa da makwabta, yace masu, 'Ku taya ni murna don na samo tunkiyata da ta bata.'
7 Je vous dis de même qu’il y aura plus de joie dans le ciel pour un pécheur faisant pénitence, que pour quatre-vingt-dix-neuf justes qui n’ont pas besoin de pénitence.
Ina gaya maku, haka kuma za a yi farin ciki a sama, a kan mai zunubi guda da ya tuba, fiye da kan masu adalci tassa'in da tara wadanda ba su bukatar tuba.
8 Ou, quelle est la femme qui, ayant dix drachmes, si elle en perd une, n’allume sa lampe, ne balaye sa maison, et ne cherche soigneusement jusqu’à ce qu’elle la trouve?
Ko kuwa wacce mace ce, in tana da kudi azurfa guda goma, in ta batar da daya, ba za ta kunna fitila ta share gidan, ta yi ta neman shi har sai ta same shi ba?
9 Et lorsqu’elle l’a trouvée, elle appelle ses amies et ses voisines, disant: Réjouissez-vous avec moi, parce que j’ai trouvé la drachme que j’avais perdue.
In kuwa ta same shi sai ta tara kawayenta da makwabtanta, ta ce, 'Ku taya ni farin ciki don na sami kudin nan nawa da ya bace.'
10 Ainsi, je vous le dis, sera la joie parmi les anges de Dieu pour un pécheur faisant pénitence.
Haka nake gaya maku, abin farin ciki ne ga mala'ikun Allah idan mai zunubi guda ya tuba.”
11 Et il ajouta: Un homme avait deux fus.
Sai Yesu ya ce, “Akwai wani mutum mai 'ya'ya biyu maza,
12 Or le plus jeune des deux dit à son père: Mon père, donnez-moi la portion de votre bien qui doit me revenir. Et le père leur partagea son bien.
sai karamin ya ce wa mahaifinsa, 'Baba, bani rabona daga cikin dukiyarka.' Sai mahaifinsa ya raba masu dukiyarsa tsakaninsu.
13 Peu de jours après, le plus jeune fils ayant rassemblé tout ce qu’il avait, partit pour une région étrangère et lointaine, et il y dissipa son bien, en vivant dans la débauche.
Bayan 'yan kwanaki kadan, sai karamin dan ya tattara duk mallakarsa, ya kama hanya zuwa wata kasa mai nisa. A can ya batas da kudinsa, yana sayan abubuwan da ba ya bukata, ya kuma batas da kudinsa a wajen masha'a.
14 Après qu’il eut tout consumé, il survint une grande famine dans ce pays, et il commença à se trouver dans l’indigence,
Bayan da ya batas da duk abin da ya ke da shi, sai aka yi babbar yunwa a kasar, sai ya shiga fatara.
15 Il alla donc, et il s’attacha à un habitant de ce pays. Or celui-ci l’envoya à sa maison des champs pour paître les pourceaux.
Ya je ya mika kansa domin aiki ga wani dan kasar, sai ya aike shi cikin gonakinsa domin ya rika ba aladu abinci.
16 Il désirait se rassasier des cosses que mangeaient les pourceaux, mais personne ne lui en donnait.
Har yayi marmarin ya ci daga cikin barbashin da aladu suke ci, domin babu wanda yake ba shi wani abu ya ci.
17 Rentrant alors en lui-même, il dit: Combien de mercenaires, dans la maison de mon père, ont du pain en abondance, et moi ici je meurs de faim!
Amma da hankalinsa ya dawo, ya ce, 'Barorin mahaifina su nawa ne da suke da abinci isasshe, amma ina nan a nan, ina mutuwa sabili da yunwa!
18 Je me lèverai, et j’irai à mon père, et je lui dirai: Mon père, j’ai péché contre le ciel et à vos yeux;
Zan tashi, in tafi gun mahaifina, in ce masa, “Baba, na yi wa sama zunubi, na kuma saba maka.
19 Je ne suis plus digne d’être appelé votre fils; traitez-moi comme l’un de vos mercenaires.
Ban cancanci a kara kira na danka ba; ka mai da ni kamar daya daga cikin barorinka.'”
20 Et se levant, il vint à son père. Comme il était encore loin, son père l’aperçut, s’attendrit, et accourant, tomba sur son cou et le baisa.
Sai ya tashi, ya taho wurin mahaifinsa. Amma tun yana daga nesa, sai mahaifinsa ya hango shi tausayi ya kama shi, ya ruga a guje, ya rungume shi, ya yi ta sumbatar sa.
21 Et le fils lui dit: Mon père, j’ai péché contre le ciel et à vos yeux, je ne suis plus digne d’être appelé votre fils.
Dan kuma ya ce masa, 'Baba, na yi wa sama zunubi, na kuma saba maka. Ban isa a kara kira na danka ba.'
22 Mais le père dit à ses serviteurs: Apportez vite sa robe première, et l’en revêtez; mettez un anneau à sa main et une chaussure à ses pieds;
Amma mahaifinsa ya ce wa bayinsa, 'Ku yi hamzari ku kawo riga mafi kyau, ku yafa masa. Ku sa masa zobe a hanunsa da takalma a kafafunsa.
23 Amenez aussi le veau gras, et tuez-le; mangeons et réjouissons-nous:
Sa'annan a kawo kiwataccen marakin nan, a yanka. Mu yi buki!
24 Car mon fils que voici était mort, et il revit; il était perdu, et il est retrouvé. Et ils commencèrent à faire grande chère.
Gama da na ya mutu a da, amma yanzu yana a raye. Ya bata a da, amma a yanzu an same shi.' Sai suka fara liyafa.
25 Cependant son fils aîné était dans les champs; et comme il revenait et approchait de la maison, il entendit une symphonie et des danses.
A wannan lokacin, babban dansa yana gona. Da ya kai kusa da gida, ya ji ana kade-kade da raye-raye.
26 Il appela donc un de ses serviteurs, et lui demanda ce que c’était.
Sai ya kira wani bawan gidan, ya tambayi manufar wadannan abubuwa.
27 Le serviteur lui répondit: Votre frère est revenu, et votre père a tué le veau gras, parce qu’il a recouvré son fils sain et sauf.
Bawan ya ce masa, 'Dan'uwanka ne ya dawo gida, mahaifinka kuma ya yanka kiwataccen marakin nan, saboda ya dawo gida lafiya.'
28 Il s’indigna, et il ne voulait pas entrer. Son père donc étant sorti, se mit à le prier.
Amma dan'uwan ya yi fushi, ya ki ya shiga ciki, mahaifinsa kuwa ya fito, ya roke shi.
29 Mais lui, répondant, dit à son père: Voilà tant d’années que je vous sers, et jamais je n’ai manqué à vos commandements, et jamais vous ne m’avez donné un chevreau pour faire bonne chère avec mes amis;
Amma babban dan ya amsa wa ubansa ya ce, 'Duba, duk yawan shekarun nan da nake bauta maka, ban taba karya umarnin ka ba, duk da haka ba ka taba bani ko dan taure da zan yi shagali tare da abokaina ba,
30 Mais après que cet autre fils, qui a dévoré son bien avec des femmes perdues, est revenu, vous avez tué pour lui le veau gras.
amma da dan nan naka ya zo wanda ya fallasar da dukiyarka a kan karuwai, ka yanka masa kiwataccen marakin nan.
31 Alors le père lui dit: Mon fils, toi, tu es toujours avec moi, et tout ce qui est à moi est à toi;
Sai mahaifin ya ce masa, 'Dana, ai kullum kana tare da ni, duk abin da yake nawa naka ne.
32 Mais il fallait faire un festin et se réjouir, parce que ton frère était mort, et il revit; il était perdu, et il est retrouvé.
Amma, daidai ne a yi murna da farinciki, don dan'uwan nan naka da ya mutu, amma yanzu yana da rai, da ya bata, amma yanzu an same shi.'”

< Luc 15 >