< Luc 13 >

1 En ce même temps, quelques-uns vinrent lui annoncer ce qui s’était passé touchant les Galiléens, dont Pilate avait mêlé le sang à leurs sacrifices.
A lokacin, wadansu mutane suka gaya masa game da galilawa wadanda Bilatus ya gauraye jininsu da hadayunsu.
2 Et Jésus répondant, leur dit: Pensez-vous que ces Galiléens fussent plus pécheurs que tous les autres Galiléens, parce qu’ils ont souffert de telles choses?
Sai Yesu ya amsa masu yace “Kuna tsammani wadannan Galilawa sun fi duk sauran Galilawan zunubi ne, da suka sha azaba haka?
3 Non, je vous le dis: mais si vous ne faites pénitence, vous périrez tous de la même manière.
A'a, ina gaya maku. In ba ku tuba ba, dukanku za ku halaka kamarsu.
4 Comme ces dix-huit sur qui tomba la tour de Siloé, et qu’elle tua, croyez-vous qu’ils fussent plus redevables que tous les autres habitants de Jérusalem?
Ko kuwa mutane goma sha takwas din nan da suna Siluwam wadanda hasumiya ta fado a kansu ta kashe su, kuna tsamani sun fi duk sauran mutanen Urushalima laifi ne?
5 Non, je vous le dis: mais si vous ne faites pénitence, vous périrez tous de la même manière.
Ina gaya maku ba haka bane. Amma duk wanda ya ki tuba, dukanku za su hallaka”
6 Il leur disait encore cette parabole: Un homme avait un figuier planté dans sa vigne, et il vint y chercher du fruit, et n’en trouva point.
Yesu ya fada wannan misali, “Wani mutum yana da baure wanda ya shuka a garkar inabinsa sai ya zo neman 'ya'yan itacen amma bai samu ba.
7 Alors il dit au vigneron: Voilà trois ans que je viens chercher du fruit à ce figuier, et je n’en trouve point: coupe-le donc; pourquoi occupe-t-il encore la terre?
Sai mutumin ya ce wa mai kula da garkar, “ka ga, shekara uku kenan nake zuwa neman 'ya'yan wannan baure, amma ban samu ba. A sare shi. Yaya za a bar shi ya tsare wurin a banza?
8 Mais le vigneron répondant, lui dit: Seigneur, laissez-le encore cette année; jusqu’à ce que je creuse tout autour, et que j’y mette du fumier:
Sai mai lura da garkar ya amsa yace, 'Ka dan ba shi lokaci kadan in yi masa kaftu in zuba masa taki.
9 Peut-être qu’il portera ainsi du fruit; sinon vous le couperez.
In yayi 'ya'ya shekara mai zuwa to, amma in bai yi 'ya'ya ba sai a sare shi!”'
10 Or Jésus enseignait dans leur synagogue les jours du sabbat.
Wata rana Yesu yana koyarwa a wata majami' a ran Asabaci.
11 Et voici venir une femme qui avait un esprit d’infirmité depuis dix-huit ans; et elle était courbée et ne pouvait aucunement regarder en haut.
Sai, ga wata mace a wurin shekarunta goma sha takwas tana da mugun ruhu, duk ta tankware, ba ta iya mikewa.
12 Jésus, la voyant, l’appela et lui dit: Femme, vous êtes délivrée de votre infirmité.
Da Yesu ya gan ta, sai ya kira ta ya ce mata, an warkar da ke daga wannan cuta.”
13 Et il lui imposa les mains, et aussitôt elle se redressa, et elle glorifiait Dieu.
Sai Yesu ya dora hannunsa a kanta, nan da nan sai ta mike a tsaye ta fara daukaka Allah.
14 Or le chef de la synagogue prit la parole, s’indignant de ce que Jésus l’eût guérie pendant le sabbat; et il dit au peuple: Il y a six jours pendant lesquels on doit travailler; venez donc ces jours-là vous faire guérir, et non pas le jour du sabbat.
Amma shugaban majami'a yayi fushi domin Yesu yayi warkarwa a ranar Asabaci. Sai shugaban ya amsa yace wa jama'a, “Akwai ranaku shida da ya kamata a yi aiki. Ku zo domin a warkar da ku amma ba ranar Asabaci ba.”
15 Mais le Seigneur, lui répondant, dit: Hypocrites, chacun de vous ne délie-t-il pas son bœuf ou son âne de la crèche le jour du sabbat, pour les mener boire?
Amma Ubangiji ya amsa masa ya ce, “Munafukai! Ashe kowannenku ba ya kwance Jakinsa ko Sa daga turkensa ya kai shi banruwa ran Asabaci?
16 Et cette fille d’Abraham que Satan a liée, voici dix-huit ans, ne fallait-il pas qu’elle fût délivrée de ses liens le jour du sabbat?
Ashe wannan 'yar gidan Ibrahim, wanda shaidan ya daure ta shekara goma sha takwas, wato ba za a iya kwance ta a ranar Asabaci kenan ba?
17 Lorsqu’il parlait ainsi, tous ses adversaires étaient couverts de confusion, et tout le peuple se réjouissait de toutes les choses qu’il faisait avec tant d’éclat.
Da ya fada wadannan abubuwa, dukansu da suka yi adawa da shi suka kunyata, duk taron kuwa suka yi ta farin ciki da abubuwa masu daraja da yayi.
18 Il disait donc: À quoi est semblable le royaume de Dieu, et à quoi le comparerai-je?
Sai Yesu ya ce, “Yaya za a misalta mulkin Allah, kuma da me zan kwatanta shi?
19 Il est semblable à un grain de sénevé qu’un homme prit et jeta dans son jardin; il crût, devint un grand arbre, et les oiseaux du ciel se reposèrent sur ses branches.
Yananan kamar kwayar mastad, wanda wani mutum ya dauka ya jefa ta a lambunsa, ta kuma yi girma ta zama gagarumin itace, har tsuntsaye suka yi shekarsu a rassanta.”
20 Et il dit encore: À quoi comparerai-je le royaume de Dieu?
Ya sake cewa, “Da me zan kwatanta mulkin Allah?
21 Il est semblable à du levain qu’une femme prend et mêle dans trois mesures de farine, jusqu’à ce que tout soit fermenté.
Yana kamar yisti wanda wata mace ta dauka ta cuda da mudu uku na garin alkama don ya kumburar da shi.”
22 Et il allait par les villes et par les villages, enseignant, et faisant son chemin vers Jérusalem.
Yesu ya ziyarci kowanne birni da kauye, a hanyar sa ta zuwa Urushalima yana koyar da su.
23 Or quelqu’un lui demanda: Seigneur, y en a-t-il peu qui soient sauvés? Il leur répondit:
Sai wani ya ce masa, “Ubangiji, wadanda za su sami ceto kadan ne?” Sai ya ce masu,
24 Efforcez-vous d’entrer par la porte étroite; car beaucoup, je vous le dis, chercheront à entrer, et ne le pourront pas.
“Ku yi kokari ku shiga ta matsatsiyar kofa, domin na ce maku, mutane dayawa za su nemi shiga amma ba za su iya shiga ba.
25 Lorsque le père de famille sera entré et aura fermé la porte, vous commencerez par vous tenir dehors et par frapper à la porte, disant: Seigneur, ouvrez-nous; et vous répondant, il vous dira: Je ne sais d’où vous êtes.
In dai maigida ya riga ya tashi ya rufe kofa, sannan za ku tsaya a waje kuna kwankwasa kofar kuna cewa, 'Ubangiji, Ubangiji, bari mu shiga ciki'. Sai ya amsa yace maku, 'Ni ban san ku ba ko daga ina ku ka fito.'
26 Alors vous commencerez à dire: Nous avons mangé et bu devant vous, et vous avez enseigné dans nos places publiques.
Sannan za ku ce, 'Mun ci mun sha a gabanka, ka kuma yi koyarwa a kan titunanmu.'
27 Et il vous dira: Je ne sais d’où vous êtes; retirez-vous de moi, vous tous, ouvriers d’iniquité.
Amma zai amsa ya ce, “Ina gaya maku, ban san ko daga ina ku ka fito ba, ku tafi daga wurina, dukanku masu aikata mugunta!'
28 Là sera le pleur et le grincement de dents, quand vous verrez Abraham, Isaac, Jacob, et tous les prophètes dans le royaume de Dieu, et vous, chassés dehors.
Za a yi kuka da cizon hakora a lokacin da kun ga Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu da dukan annabawa a mulkin Allah amma ku-za a jefar da ku waje.
29 Il en viendra de l’orient, et de l’occident, et de l’aquilon, et du midi, et ils auront place au festin dans le royaume de Dieu.
Za su zo daga gabas, yamma, kudu, da arewa, za su ci a teburin abinci a mulkin Allah.
30 Et ce sont les derniers qui seront les premiers, et ce sont les premiers qui seront les derniers.
Ku san da wannan, na karshe za su zama na farko, na farko kuma za su zama na karshe.”
31 Ce même jour, quelques-uns des pharisiens s’approchèrent, disant: Allez-vous-en, retirez-vous d’ici; car Hérode veut vous faire mourir.
Nan take, wadansu farisiyawa suka zo suka ce masa, “Ka tafi daga nan domin Hirudus yana so ya kashe ka.”
32 Et il leur dit: Allez, et dites à ce renard: Voilà que je chasse les démons et guéris les malades aujourd’hui et demain, et c’est le troisième jour que je dois être consommé.
Yesu ya ce, “Ku tafi ku gaya wa dilan nan cewa, 'Duba, na fitar da aljanu, ina warkarwa yau da gobe, kuma a rana ta uku kuwa zan gama aiki na.'
33 Cependant il faut que je marche aujourd’hui et demain, et le jour suivant; parce qu’il ne peut se faire qu’un prophète périsse hors de Jérusalem.
Ko da kaka, dole ne in ci gaba da tafiyata yau, da gobe, da kuma jibi, don bai dace a kashe annabi nesa da Urushalima ba.
34 Jérusalem, Jérusalem, qui tues les prophètes, et qui lapides ceux qui te sont envoyés, combien de fois ai-je voulu rassembler tes enfants, comme un oiseau rassemble sa couvée sous ses ailes, et tu ne l’as point voulu?
Urushalima, Urushalima masu kisan annabawa, masu jifan wadanda aka aiko gare ku. Sau nawa ne ina so in tattara 'ya'yanki kamar yadda kaza take tattara 'ya'yanta a cikin fukafukanta, amma ba ki so wannan ba.
35 Voici que votre maison vous sera laissée déserte. Je vous le dis, vous ne me verrez plus, jusqu’à ce qu’il arrive que vous disiez: Béni celui qui vient au nom du Seigneur!
Duba, an yashe gidanki. Ina kwa gaya maku ba za ku kara ganina ba sai ran da kuka ce, 'Albarka ta tabbata ga mai zuwa da sunan Ubangiji.'”

< Luc 13 >