< Lévitique 21 >

1 Le Seigneur dit aussi à Moïse: Parle aux prêtres, fils d’Aaron, et tu leur diras: Qu’un prêtre ne se souille point à la mort de ses concitoyens;
Ubangiji ya ce wa Musa, “Yi magana da firistoci,’ya’yan Haruna maza, ka ce musu, ‘Kada firist yă ƙazantar da kansa saboda wani cikin mutanensa da suka mutu,
2 Or, il s’y souillera, à moins qu’il ne s’agisse seulement de ses consanguins et de ses proches, c’est-à-dire, de son père et de sa mère, de son fils et de sa fille, de son frère,
sai dai na danginsa na kusa, kamar mahaifiyarsa ko mahaifinsa, ɗansa ko’yarsa, ɗan’uwansa,
3 Et de sa sœur vierge, qui n’a pas été mariée à un homme;
ko’yar’uwarsa da ba tă riga ta yi aure ba, wadda take dogara gare shi, da yake ba ta da miji, saboda ita zai iya ƙazantar da kansa.
4 Mais il ne se souillera pas non plus pour le prince de son peuple.
Kada yă ƙazantar da kansa saboda mutanen da suke da dangantakar da shi ta wurin aure, ta yin haka zai ƙazantar da kansa.
5 Ils ne raseront point leur tête, ni leur barbe, et dans leur chair ils ne feront point d’incisions.
“‘Kada firistoci su aske kansu ƙwal ko su kwakkwafe gemunsu, ko su tsattsage jikunansu.
6 Ils seront saints pour leur Dieu et ils ne souilleront point son nom; car ils offrent l’holocauste du Seigneur, et les pains de leur Dieu, et c’est pour cela qu’ils seront saints.
Dole su kasance masu tsarki ga Allahnsu, kada kuma su ɓata sunan Allahnsu. Domin sukan miƙa hadayun da aka kawo wa Ubangiji da wuta, abincin Allahnsu, saboda haka sai su kasance da tsarki.
7 Ils n’épouseront point une femme déshonorée et une fille prostituée, ni celle qui a été répudiée par son mari; parce qu’ils sont consacrés à leur Dieu,
“‘Ba za su auri matan da karuwanci ya ɓata su, ko waɗanda mazansu suka sake su ba, gama firistoci masu tsarki ne ga Allahnsu.
8 Et qu’ils offrent les pains de proposition. Qu’ils soient donc saints, parce que je suis saint, moi aussi, le Seigneur qui les sanctifie.
An ɗauke su da tsarki, domin suna miƙa abincin Allahnku. An ɗauka su masu tsarki gama Ni Ubangiji, mai tsarki ne, Ni wanda ya mai da ku masu tsarki.
9 Si la fille d’un prêtre est surprise en fornication et qu’elle ait déshonoré le nom de son père, elle sera complètement brûlée par les flammes.
“‘In’yar firist ta ɓata kanta ta wurin zama karuwa, ta kunyatar da mahaifinta ke nan; dole a ƙone ta da wuta.
10 Le pontife, c’est-à-dire, le grand-prêtre parmi ses frères, sur la tête duquel l’huile de l’onction a été répandue, dont les mains ont été consacrées à son sacerdoce et qui est revêtu des saints vêtements, ne découvrira point sa tête et ne déchirera point ses vêtements:
“‘Babban firist, wanda yake ɗaya cikin’yan’uwansa wanda aka shafe da mai a kansa, wanda kuma aka naɗa don yă sa rigunan firistoci, kada yă bar gashin kansa buzu-buzu, ko ya kyakketa rigunansa.
11 Et il n’entrera absolument auprès d’aucun mort: pour son père même et pour sa mère il ne se souillera point.
Ba zai shiga inda akwai gawa ba. Kada yă ƙazantar da kansa, ko ma ta mahaifinsa ce ko ta mahaifiyarsa.
12 Une sortira point des lieux saints, afin qu’il ne souille pas le sanctuaire du Seigneur, parce que l’huile de la sainte onction de son Dieu est sur lui. Je suis le Seigneur.
An keɓe shi domina, kada yă ƙazantar da kansa, kada kuwa yă ɓata Tentin Sujada ta wurin shiga gidan da gawa take, ko ta mahaifinsa, ko ta mahaifiyarsa ce. Ni ne Ubangiji.
13 C’est une vierge qu’il prendra pour femme;
“‘Dole macen da zai aura ta kasance budurwa.
14 Mais il ne prendra point une veuve, et une femme répudiée, ou déshonorée, ni une prostituée, mais une jeune fille de son peuple.
Ba zai auri matan da mijinta ya mutu, ko macen da mijinta ya rabu da ita, ko macen da ta ɓata kanta ta wurin karuwanci ba, sai dai yă auri budurwa daga cikin mutanensa,
15 Qu’il ne mêle point le sang de sa race avec le vulgaire de sa nation, parce que je suis le Seigneur qui le sanctifie.
don kada yă ƙazantar da’ya’yansa a cikin mutanensa. Ni ne Ubangiji, wanda ya mai da shi mai tsarki.’”
16 Le Seigneur parla encore à Moïse, disant:
Ubangiji ya ce wa Musa,
17 Dis à Aaron: Un homme de ta lignée dans tes familles, qui aura une tache, n’offrira point des pains à son Dieu;
“Faɗa wa Haruna cewa, ‘Don tsararraki masu zuwa, kada ko ɗaya daga cikin zuriyarka, da yake da lahani yă zo kusa domin yă miƙa hadaya ta ci gare ni.
18 Et il ne s’approchera point de son ministère, s’il est aveugle, s’il est boiteux, s’il a le nez petit, ou grand, ou tordu,
Duk mai lahani, ko makaho, ko gurgu, ko mai naƙasa, ko mai wani lahani a jiki;
19 S’il a le pied rompu ou la main,
ko mai karyayyen ƙafa, ko mai karyayyen hannu,
20 S’il est bossu, s’il est chassieux, s’il a une taie sur l’œil, s’il a une gale continue, ou une dartre vive sur le corps, ou une hernie.
ko mai ƙusumbi, ko wada, ko wanda yake da lahani a ido, ko mai cuta mai sa ƙaiƙayi, ko mai kirci, ko wanda aka daƙe, ba zai yi kusa domin yă miƙa hadaya ba.
21 Quiconque de la race d’Aaron, le prêtre, aura une tache, ne s’approchera point pour offrir des hosties au Seigneur, ni des pains à son Dieu:
Ba zuriyar Haruna firist, mai lahanin da zai zo kusa don yă miƙa hadayun da aka yi ga Ubangiji da wuta. Da yake yana da lahani, ba zai zo kusa don yă miƙa abincin Allahnsa ba.
22 Il mangera néanmoins des pains qui sont offerts dans le sanctuaire,
Zai iya cin abinci mafi tsarki na Allahnsa, haka ma abinci mai tsarki;
23 De telle sorte seulement, qu’il n’entre pas au dedans du voile, et qu’il ne s’approche pas de l’autel, parce qu’il a une tache et qu’il ne doit point souiller mon sanctuaire. Je suis le Seigneur qui vous sanctifie.
duk da haka saboda lahaninsa, ba zai yi kusa da labule, ko yă yi kusa da bagade don kada yă ƙazantar da wuri mai tsarkina. Ni ne Ubangiji wanda yake mai da su masu tsarki.’”
24 Moïse dit donc à Aaron, à ses fils et à tout Israël tout ce qui lui avait été commandé.
Sai Musa ya faɗa wannan wa Haruna da’ya’yansa maza da kuma dukan Isra’ilawa.

< Lévitique 21 >