< Lévitique 10 >
1 Alors Nadab et Abiu ayant pris les encensoirs, mirent du feu et de l’encens dessus, offrant devant le Seigneur un feu étranger; ce qui ne leur avait pas été ordonné.
’Ya’yan Haruna maza, Nadab da Abihu suka ɗauki farantansu, suka sa wuta a ciki, suka zuba turare a kai; suka kuma miƙa haramtacciyar wuta a gaban Ubangiji, ba irin wadda Ubangiji ya umarta ba.
2 Et un feu sorti du Seigneur les dévora, et ils moururent devant le Seigneur.
Sai wuta ta fito daga Ubangiji ta cinye su, suka kuma mutu a gaban Ubangiji.
3 Et Moïse dit à Aaron: Voilà ce qu’a dit le Seigneur: Je serai sanctifié dans ceux qui m’approchent, et je serai glorifié devant tout le peuple. Ce qu’entendant, Aaron se tut.
Sai Musa ya ce Haruna, “Ga abin da Ubangiji yake nufi sa’ad da ya ce, “‘A cikin waɗanda suka kusace ni za a tabbata ni mai tsarki ne; a fuskar dukan mutane za a kuwa girmama ni.’” Haruna ya yi shiru.
4 Or, Moïse ayant appelé Misaël et Elisaphan fils d’Oziel, oncle d’Aaron, leur dit: Allez et prenez vos frères de devant le sanctuaire, et emportez-les hors du camp.
Sai Musa ya kira Mishayel da Elzafan,’ya’yan Uzziyel kawun Haruna, ya ce musu, “Ku zo nan; ku ɗauki’yan’uwanku waje da sansani, daga gaban wuri mai tsarki.”
5 Et aussitôt allant, il les prient, comme ils gisaient, vêtus de leurs tuniques de lin, et ils les jetèrent dehors, comme il leur avait été commandé.
Sai suka zo suka ɗauke su, suna nan cikin taguwoyinsu, zuwa waje da sansani yadda Musa ya umarta.
6 Alors Moïse dit à Aaron, et à Eléazar et à Ithamar ses fils: Ne découvrez pas vos têtes, et ne déchirez pas vos vêtements, de peur que vous ne mouriez, et que l’indignation ne s’élève contre toute l’assemblée. Que vos frères et toute la maison d’Israël pleurent l’incendie que le Seigneur a suscité;
Sa’an nan Musa ya ce wa Haruna da Eleyazar da Itamar’ya’yansa maza, “Kada ku bar gashin kanku barkatai, kada kuma ku yage tufafinku, don kada ku mutu. Yin haka zai jawo fushin Ubangiji a kan dukan jama’a. Amma dangoginku, wato, dukan Isra’ilawa, suna iya kuka saboda waɗanda Ubangiji ya hallaka da wuta.
7 Mais vous, vous ne sortirez peint de la porte du tabernacle; autrement vous périrez; car l’huile de la sainte onction est sur vous. Ceux-ci firent tout selon l’ordre de Moïse.
Kada ku bar ƙofar Tentin Sujada ko kuwa ku mutu, domin man Shafan Ubangiji yana kanku.” Saboda haka suka yi kamar yadda Musa ya faɗa.
8 Le Seigneur dit aussi à Aaron:
Sa’an nan Ubangiji ya yi magana da Haruna ya ce,
9 Vous ne boirez point de vin et de tout ce qui peut enivrer, toi et tes fils, quand vous entrerez dans le tabernacle de témoignage, de peur que vous ne mouriez; parce que c’est un précepte perpétuel pour vos générations,
“Kai da’ya’yanka maza, ba za ku sha ruwan inabi ko wani abu mai sa jiri ba a duk sa’ad da za ku shiga cikin Tentin Sujada, in ba haka ba za ku mutu. Wannan dawwammamiyar farilla ce wa tsararraki masu zuwa.
10 Et afin que vous ayez la science de discerner entre le saint et le profane, entre ce qui est souillé et ce qui est pur,
Dole ku bambanta tsakanin mai tsarki da marar tsarki, tsakanin marar tsabta da mai tsabta,
11 Et que vous enseigniez aux enfants d’Israël tout ce qui concerne mes lois que le Seigneur a proclamées par l’entremise de Moïse.
za ku kuma koyar da Isra’ilawa dukan farillan da Ubangiji ya ba su ta wurin Musa.”
12 Moïse dit alors à Aaron, à Eléazar et à Ithamar, ses fils qui lui étaient restés: Prenez le sacrifice qui est resté de l’oblation du Seigneur, et mangez-le sans levain près de l’autel, parce que c’est une chose très sainte.
Musa ya ce wa Haruna da Eleyazar da Itamar’ya’yansa maza da suka ragu, “Ku ɗauki ragowar hadaya ta gari wadda aka yi hadaya ta ƙonawa da ita ga Ubangiji ku ci ba tare da yisti ba, a gefen bagaden, gama tsattsarka ne.
13 Or, vous le mangerez dans un lieu saint, parce qu’il vous a été donné, à toi et à tes fils, des oblations du Seigneur, comme il m’a été ordonné.
Ku ci shi a tsattsarkan wuri, gama rabonka ne da na’ya’yanka daga cikin hadayun da akan ƙone da wuta ga Ubangiji; gama haka aka umarce ni.
14 La poitrine aussi qui a été offerte, et l’épaule qui a été séparée, vous les mangerez dans un lieu très pur, toi et tes fils et tes filles avec toi; car c’est pour toi et pour tes enfants qu’elles ont été réservées, des hosties salutaires des enfants d’Israël;
Amma kai da’ya’yanka maza da mata za su iya ci ƙirjin da aka kaɗa, da kuma cinyar da aka miƙa. Ku ci su a wuri mai tsabta; an ba da su gare ku da kuma’ya’yanku a matsayin rabo daga hadaya ta salama ta Isra’ilawa.
15 Parce qu’ils ont élevé devant le Seigneur l’épaule, la poitrine et les graisses qui sont brûlées sur l’autel, et qu’elles t’appartiennent à toi et à tes fils par une loi perpétuelle, comme a ordonné le Seigneur.
Cinyar da aka miƙa da kuma ƙirjin da aka kaɗa, dole a kawo su tare da ɓangarori kitsen hadayun da aka yi ta wuri wuta, don a kaɗa a gaban Ubangiji a matsayin hadaya ta kaɗawa. Wannan zai zama na kullayaumi gare ka da’ya’yanka, yadda Ubangiji ya umarta.”
16 Cependant, comme Moïse cherchait le bouc qui avait été offert pour le péché, il le trouva entièrement brûlé; or, irrité contre Eléazar et Ithamar, fils d’Aaron, qui lui étaient restés, il dit:
Sa’ad da Musa ya nemi sani game da akuyar hadaya don zunubi, ya kuwa gane cewa an ƙone shi, sai ya yi fushi da Eleyazar da kuma Itamar,’ya’yan Haruna maza da suka ragu, ya kuma yi tambaya,
17 Pourquoi n’avez-vous pas mangé dans le lieu saint l’hostie pour le péché, qui est très sainte, et qui vous a été donnée, afin que vous portiez l’iniquité de la multitude, et que vous priiez pour elle en la présence du Seigneur,
“Me ya sa ba ku ci hadaya don zunubi a cikin wuri mai tsarki ba? Mafi tsaki ne; an ba ku ne don a ɗauke laifin jama’a ta wurin yin kafara saboda su a gaban Ubangiji.
18 Surtout puisqu’on n’a pas porté de son sang dans les lieux saints, et que vous auriez dû la manger dans le sanctuaire comme il m’a été ordonné?
Da yake ba a kai jininsa cikin wuri mai tsarki ba, ya kamata ku ci akuyar a wuri mai tsarki, kamar yadda na umarta.”
19 Aaron répondit: La victime pour le péché a été offerte aujourd’hui, et l’holocauste devant le Seigneur; mais pour moi, il m’est arrivé ce que tu vois. Comment aurais-je pu la manger, ou plaire au Seigneur dans les cérémonies, avec un esprit profondément affligé?
Sai Haruna ya amsa wa Musa, “Yau sun miƙa hadayarsu don zunubi da kuma hadayarsu ta ƙonawa a gaban Ubangiji, ga kuma irin waɗannan abubuwa da suka same ni, da a ce na ci hadaya don zunubi yau, da zai yi kyau ke nan a gaban Ubangiji?”
20 Ce qu’ayant entendu Moïse, il reçut son excuse.
Da Musa ya ji haka, sai ya gamsu.