< Juges 6 >
1 Mais les enfants d’Israël firent le mal en la présence du Seigneur, qui les livra à la main de Madian pendant sept ans,
Isra’ilawa suka sāke yin mugayen ayyuka a gaban Ubangiji, sai ya ba da su ga Midiyawa shekara bakwai.
2 Et ils furent très opprimés par eux. Ils se firent des antres et des cavernes dans les montagnes, et des lieux très fortifiés pour se défendre.
Da Midiyawa suka matsa musu sosai, sai Isra’ilawa suka yi wa kansu mafakai a rammukan duwatsu, kogona da kuma mafaka.
3 Lorsqu’Israël avait semé, montaient Madian et Amalec et tous les autres peuples des nations orientales;
Duk lokacin da Isra’ilawa suka yi shuka sai Midiyawa da Amalekawa da waɗansu mutane daga gabashi sukan kai musu hari.
4 Et plantant chez eux leurs tentes, comme ils étaient au milieu des moissons, ils ravageaient tout jusqu’à Gaza; et ils ne laissaient absolument rien en Israël, de tout ce qui était nécessaire à la vie, ni brebis, ni bœufs, ni ânes.
Sukan yi sansani a ƙasar sun lalatar da hatsi har zuwa Gaza kuma ba sa barin wani abu mai rai wa Isra’ila, ko tumaki ko shanu ko jakuna.
5 Car ils venaient eux-mêmes et tous leurs troupeaux avec leurs tabernacles; et comme des sauterelles, cette multitude innombrable d’hommes et de chameaux remplissait tout, ravageant tout ce qu’elle touchait.
Sukan zo da dabbobinsu da tentinsu kamar tarin fāri. Yana da wuya a ƙidaya yawan mutanen da kuma raƙumansu; sukan mamaye ƙasar don su lalatar da ita.
6 Israël fut donc très humilié en présence de Madian.
Midiyawa suka talauce Isra’ilawa ƙwarai, har ya sa suka yi kuka ga Ubangiji don taimako.
7 Et il cria au Seigneur, demandant secours contre les Madianites.
Sa’ad da Isra’ilawa suka yi kuka ga Ubangiji saboda Midiyawa,
8 Le Seigneur leur envoya un homme, prophète, qui leur dit: Voici ce que dit le Seigneur Dieu d’Israël: C’est moi qui vous ai fait monter de l’Égypte, et qui vous ai retirés de la maison de servitude;
sai ya aika musu da annabi, wanda ya ce, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce na fitar da ku daga Masar, daga ƙasar bauta.
9 Je vous ai délivrés de la main des Egyptiens, et de tous les ennemis qui vous affligeaient; je les ai chassés à votre entrée, et je vous ai livré leur terre.
Na ƙwace ku daga ikon Masarawa da kuma daga dukan hannuwan masu danniya. Na kore su a gabanku na kuma ba ku ƙasarsu.
10 Et j’ai dit: Je suis le Seigneur votre Dieu, ne craignez point les dieux des Amorrhéens dans la terre desquels vous habitez. Et vous n’avez pas voulu écouter ma voix.
Na ce muku, ‘Ni ne Ubangiji Allahnku; kada ku bauta allolin Amoriyawa, waɗanda kuke zama a ƙasarsu.’ Amma ba ku saurare ni ba.”
11 Or, vint l’ange du Seigneur et il s’assit sous le chêne qui était à Ephra et qui appartenait à Joas, père de la famille d’Ezri. Et comme Gédéon, son fils, battait et vannait du blé dans le pressoir pour échapper à Madian,
Sai mala’ikan Ubangiji ya zo ya zauna a ƙarƙashin itacen oak a Ofra na Yowash mutumin Abiyezer, inda ɗansa Gideyon yake sussukar alkama a wurin matsin inabi don yă ɓoye daga Midiyawa.
12 L’ange du Seigneur apparut et lui dit: Le Seigneur est avec toi, ô le plus fort des hommes!
Sa’ad da mala’ikan Ubangiji ya bayyana wa Gideyon, sai ya ce masa, “Ubangiji yana tare da kai, jarumi.”
13 Et Gédéon lui répondit: Je vous conjure, mon seigneur, si le Seigneur est avec nous, pourquoi tout cela a-t-il fondu sur nous? Où sont ses merveilles que nous ont racontées nos pères? car ils ont dit: Le Seigneur nous a retirés de l’Égypte. Mais maintenant le Seigneur nous a abandonnés, et nous a livrés à la main de Madian.
Gideyon ya ce, “Ranka yă daɗe, in Ubangiji yana tare da mu, me ya sa waɗannan abubuwa suka faru da mu? Ina dukan abubuwan al’ajabinsa waɗanda kakanninmu suka gaya mana game su sa’ad da suka ce, ‘Ashe, ba Ubangiji ne ya fitar da mu daga Masar ba?’ Amma yanzu Ubangiji ya rabu da mu ya kuma sa mu hannun Midiyawa.”
14 Et le Seigneur le regarda et dit: Va avec cette tienne force, et tu délivreras Israël de la main de Madian. Sache que je t’ai envoyé.
Sai Ubangiji ya juya wajensa ya ce, “Ka je da ƙarfin da kake da shi ka ceci Isra’ila daga hannun Midiyawa. Ba Ni ne nake aikan ka ba?”
15 Gédéon répondant, dit: Je vous conjure, mon seigneur, comment délivrerai-je Israël? Voilà que ma famille est la dernière en Manassé, et que moi je suis le plus petit dans la maison de mon père.
Gideyon ya ce, “Amma Ubangiji, yaya zan iya ceci Isra’ila? Kabilata ce marar ƙarfi duka a Manasse, kuma ni ne ƙarami a iyalina.”
16 Et le Seigneur lui dit: Moi-même, je serai avec toi, et tu battras Madian comme un seul homme.
Ubangiji ya ce, “Zan kasance tare da kai, za ka kuwa fatattake dukan Midiyawa gaba ɗaya.”
17 Alors Gédéon: Si j’ai, dit-il, trouvé grâce devant vous, donnez-moi un signe que c’est vous qui me parlez.
Gideyon ya ce, “In lalle na sami tagomashi a gabanka, to, ka ba ni wata alamar da ta nuna lalle kai kake magana da ni.
18 Et ne vous retirez point d’ici, jusqu’à ce que je retourne vers vous, portant mon sacrifice, et vous l’offrant. L’ange lui répondit: Oui, j’attendrai ton retour.
Ina roƙonka ka dakata har in komo in kawo maka hadayata in ajiye a gabanka.” Sai Ubangiji ya ce, “Zan jira har ka dawo.”
19 C’est pourquoi Gédéon entra chez lui, et fit cuire un chevreau et des pains azymes d’une mesure de farine, • et plaçant la chair dans la corbeille, et le jus de la chair dans la marmite, il porta le tout sous le chêne, et le lui offrit.
Sai Gideyon ya shiga ciki, ya gyara’yar akuya ya dafa, da garin efa ya yi burodi marar yisti. Da ya sa naman a kwando, romon kuma a tukunya, sai ya fito da su waje ya miƙa masa su a ƙarƙashin itacen oak.
20 L’ange du Seigneur lui dit: Prends la chair et les pains azymes, et pose-les sur cette pierre, et verse le jus dessus. Lorsqu’il eut fait ainsi,
Mala’ikan Allah ya ce masa, “Ka ɗauko naman da burodi marar yisti ka sa su a kan wannan dutse, ka zuba romon a kai.” Gideyon kuwa ya yi haka.
21 L’ange du Seigneur étendit le bout de la verge qu’il tenait à la main, et il toucha la chair et les pains azymes: et le feu monta de la pierre, et consuma la chair et les pains azymes; mais l’ange du Seigneur disparut de devant ses yeux.
Da kan sandan da yake a hannunsa, mala’ikan Ubangiji ya taɓa naman da burodi marar yistin. Sai wuta ta fito daga dutsen ta cinye naman da burodin. Mala’ikan kuwa ya ɓace.
22 Et Gédéon, voyant que c’était l’ange du Seigneur, dit: Hélas! Seigneur mon Dieu, j’ai vu l’ange du Seigneur face à face.
Sa’ad da Gideyon ya gane mala’ikan Ubangiji ne, sai ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka! Na ga mala’ikan Ubangiji ido da ido.”
23 Et le Seigneur lui répondit: Paix avec toi! ne crains point, tu ne mourras pas.
Amma Ubangiji ya ce masa, “Salama! Kada ka ji tsoro, ba za ka mutu ba.”
24 Gédéon bâtit donc là un autel au Seigneur et il l’appela Paix du Seigneur, jusqu’au présent jour. Et lorsqu’il était encore à Ephra, qui est à la famille d’Ezri,
Saboda haka Gideyon ya gina wa Ubangiji bagade a can, ya kuma kira shi, Ubangiji Salama ne. Har wa yau bagaden yana a Ofra ta mutanen Abiyezer.
25 Le Seigneur lui dit en cette nuit-là: Prends le taureau de ton père et un autre taureau de sept ans, et tu détruiras l’autel de Baal, qui est à ton père; et le bois qui est autour de l’autel, coupe-le.
A wannan dare Ubangiji ya ce masa, “Ka ɗauki bijimi na biyu daga garken mahaifinka, wannan mai shekara bakwai. Ka rushe bagaden mahaifinka na Ba’al ka sare ginshiƙin Ashera kusa da ita.
26 Tu bâtiras aussi un autel au Seigneur ton Dieu sur le sommet de cette pierre, sur laquelle tu as déjà posé le sacrifice; et tu prendras avec toi le second taureau, et tu offriras un holocauste sur un amas d’arbres que tu auras coupés de ce bois.
Sa’an nan ka gina bagade irin da ya dace wa Ubangiji Allahnka a kan wannan tudu. Ka yi amfani da itacen katakon ginshiƙin Ashera da ka sare, ka miƙa bijiman nan biyu hadaya ta ƙonawa.”
27 Gédéon ayant donc pris dix hommes de ses serviteurs, fit comme lui avait ordonné le Seigneur. Mais craignant la maison de son père et les hommes de cette ville-là, il ne voulut pas le faire pendant le jour, mais il accomplit toutes choses de nuit.
Saboda haka Gideyon ya ɗebi bayinsa bakwai ya yi yadda Ubangiji ya ce masa. Amma saboda yana tsoron iyalinsa da mutanen gari, ya yi haka da dare a maimako da rana.
28 Et lorsque les hommes de cette ville se furent levés au matin, ils virent l’autel de Baal détruit, le bois coupé, et le second taureau mis sur l’autel qui venait d’être bâti.
Da safe sa’ad da mutanen garin suka tashi, sai suka tarar an rushe bagaden Ba’al, tare da ginshiƙin Ashera da yake kusa da shi, duk an sare, bijimi na biyu kuma aka miƙa hadaya a kan sabon bagaden!
29 Alors ils se dirent les uns aux autres: Qui a fait cela? Et comme ils cherchaient partout l’auteur du fait, on leur dit: C’est Gédéon, fils de Joas, qui a fait toutes ces choses.
Sai suka tambayi junansu, “Wa ya yi wannan?” Sa’ad da suka bincika a hankali, sai aka faɗa musu, “Gideyon ɗan Yowash ne ya yi haka.”
30 Et ils dirent à Joas: Fais venir ton fils ici, afin qu’il meure, parce qu’il a détruit l’autel de Baal, et qu’il a coupé le bois.
Mutanen garin suka ce wa Yowash, “Ka kawo mana ɗanka. Dole yă mutu, domin ya rushe bagaden Ba’al, ya sare ginshiƙin Asheran da yake tsaye kusa da shi.”
31 Joas leur répondit: Est-ce que vous êtes les vengeurs de Baal, pour que vous combattiez pour lui? Que celui qui est son ennemi, meure avant que la lumière de demain ne vienne. S’il est dieu, qu’il se venge lui-même de celui qui a démoli son autel.
Amma Yowash ya ce wa taron da suka tayar masa, “Za ku yi hamayya domin Ba’al ne? Kuna ƙoƙari ku cece shi ne? Duk wanda ya yi faɗa saboda shi za a kashe shi kafin safe. In lalle Ba’al allah ne, zai kāre kansa sa’ad da wani ya rushe bagadensa.”
32 Depuis ce jour Gédéon fut appelé Jérobaal, parce que Joas avait dit: Que Baal se venge de celui qui a démoli son autel.
Saboda haka a ranar suka kira Gideyon, “Yerub-Ba’al,” suna cewa, “Bari Ba’al ya yi hamayya da shi,” domin ya rushe bagaden Ba’al.
33 Ainsi, tout Madian, Amalec et les peuples orientaux se réunirent, et passant le Jourdain, ils campèrent dans la vallée de Jezraël.
To, dukan Midiyawa, Amalekawa da sauran mutanen gabashi suka haɗa ƙarfi suka ƙetare Urdun suka kafa sansani a Kwarin Yezireyel.
34 Mais l’esprit du Seigneur remplit Gédéon, qui sonnant de la trompette, convoqua la maison d’Abiézer, afin qu’elle le suivît.
Sa’an nan Ruhun Ubangiji ya sauko wa Gideyon, ya kuma busa ƙaho, ya kira mutanen Abiyezer su bi shi.
35 Et il envoya des messagers à tout Manassé, qui, lui aussi, le suivit; et il envoya d’autres messagers à Aser, à Zabulon et à Nephthali qui vinrent à sa rencontre.
Ya aika manzanni ko’ina a Manasse, yana kiransu su kintsa, haka ma Asher, Zebulun da Naftali, ta haka su ma suka haura su sadu da su.
36 Alors Gédéon dit à Dieu: Si vous sauvez par ma main Israël, comme vous avez dit,
Gideyon ya cewa Allah, “In za ka ceci Isra’ila ta hannuna yadda ka yi alkawari,
37 Je mettrai cette toison dans l’aire: s’il y a de la rosée sur la toison seule, et sur toute la terre de la sécheresse, je saurai que c’est par ma main, comme vous avez dit, que vous délivrerez Israël.
to, zan shimfiɗa ulu a masussuka, inda safe akwai raɓa a kan ulun kaɗai, ƙasa kuwa a bushe, to, zan san cewa za ka ceci Isra’ila ta hannuna, yadda ka ce.”
38 Et il fut fait ainsi. Et se levant de nuit, et pressant la toison, il remplit une conque de rosée.
Abin da faru ke nan. Gideyon ya tashi da sassafe kashegari, ya matse ulun ya kakkaɓe raɓar, ruwan ya cika ƙwarya.
39 Et Gédéon dit de nouveau à Dieu: Que votre fureur ne s’irrite point contre moi, si je fais encore une fois une tentative, en demandant un signe dans la toison. Je demande que la toison seule soit sèche, et que toute la terre soit mouillée de rosée.
Sa’an nan Gideyon ya ce wa Allah, “Kada ka yi fushi da ni. Bari in ƙara yin wani gwaji kuma da ulun. A wannan lokaci ka sa ulun yă bushe, ƙasar kuma ta rufu da raɓa.”
40 Et Dieu fit en cette nuit-là comme il avait demandé: et il y eut de la sécheresse sur la toison seule, et de la rosée sur toute la terre.
A wannan dare Allah ya yi haka. Ulun ne kaɗai yake a bushe, amma dukan ƙasar ta jiƙe da raɓa.