< Juges 5 >

1 Or, Debbora et Barac, fils d’Abinoem, chantèrent en ce jour-là, disant:
A wannan rana ce Debora da Barak ɗan Abinowam suka rera wannan waƙa.
2 Vous qui des enfants d’Israël avez volontairement offert vos âmes au péril, bénissez le Seigneur.
“Sa’ad da’ya’yan sarki a Isra’ila suka yi jagora, sa’ad da mutane suka niyya su ba da kansu, suna yabon Ubangiji!
3 Ecoutez, rois; prêtez l’oreille, princes; c’est moi, c’est moi qui chanterai le Seigneur; je célébrerai par des hymnes le Seigneur Dieu d’Israël.
“Ya sarakuna, ku ji! Ku saurara, ku masu mulki! Zan yi waƙa ga Ubangiji, zan yi waƙa; zan yi kaɗe-kaɗe ga Ubangiji, Allah na Isra’ila.
4 Seigneur, lorsque vous sortiez de Séir et que vous passiez par les régions d’Edom, la terre s’émut, et les cieux et les nuées versèrent goutte à goutte leurs eaux.
“Ya Ubangiji, sa’ad da ka bar Seyir, sa’ad da ka yi tafiya daga ƙasar Edom, ƙasa ta girgiza, sammai suka zubo, gizagizai sun zubo da ruwa.
5 Les montagnes s’écoulèrent devant la face du Seigneur, et le Sinaï devant la face du Seigneur Dieu d’Israël.
Duwatsu suka girgizu a gaban Ubangiji, Wannan na Sinai, a gaban Ubangiji, Allah na Isra’ila.
6 Aux jours de Samgar, fils d’Anath, aux jours de Jahel, les sentiers se reposèrent, et ceux qui y entraient, marchèrent par des routes détournées.
“A zamanin Shamgar ɗan Anat, a zamanin Yayel, an yashe dukan hanyoyi; matafiye suka bi hanyoyin da suka yi kona-kona.
7 Les forts manquèrent en Israël, et se reposèrent, jusqu’à ce que se levât Debbora, qu’elle se levât mère en Israël.
Rayuwar ƙauye a Isra’ila ta daina, ta daina sai da ni, Debora, na taso, na taso mahaifiya a Isra’ila.
8 Le Seigneur a choisi de nouvelles guerres, il a renversé lui-même les portes des ennemis; est-ce qu’un bouclier et une lance paraissaient parmi les quarante mille d’Israël?
Sa’ad da suka zaɓi sababbin alloli, sai ga yaƙi a ƙofofin birnin, ba a kuwa ga garkuwa ko māshi a cikin mutum dubu arba’in a Isra’ila ba.
9 Mon cœur aime les princes d’Israël: vous qui volontairement vous êtes offerts au danger, bénissez le Seigneur.
Zuciyata tana tare da’ya’yan sarakunan Isra’ila, tare da masu niyyar ba da kansu da yardan rai cikin mutane. Yabo ya tabbata ga Ubangiji!
10 Vous qui montez sur des ânes brillants, qui siégez dans le jugement et qui marchez dans la voie, parlez.
“Ku da kuke hawan fararen jakuna, kuna zama a sirdin barguna, da ku da kuke tafiya a kan hanya, ku kula
11 Que là où les chars ont été brisés et l’armée des ennemis étouffée on raconte les justices du Seigneur, sa clémence envers les forts d’Israël. Alors le peuple du Seigneur descendit aux portes, et il acquitta principauté.
da muryoyin mawaƙa a wuraren ruwaye. Suna faɗi ayyukan adalcin Ubangiji, ayyukan adalcin mayaƙansa a Isra’ila. “Sa’an nan mutanen Ubangiji suka gangara zuwa ƙofofin birni.
12 Lève-toi, lève-toi, Debbora, lève-toi, lève-toi, et dis un cantique. Lève-toi, Barac, saisis tes captifs, fils d’Abinoem.
‘Ki farka, ki farka, Debora! Ki farka, ki farka, ki tā da waƙa! Ka farka, ya Barak! Ka ta sa kamammunka gaba, ya ɗan Abinowam.’
13 Ils ont été sauvés les débris du peuple, le Seigneur a combattu parmi les forts.
“Sa’an nan waɗanda aka bari suka sauko zuwa wajen shugabanni; mutane na Ubangiji suka zo wurina tare da masu ƙarfi.
14 Un héros sorti d’Ephraïm les a détruits dans Amalec, et après lui un mitre est sorti de Benjamin contre tes peuples, ô Amalec: des princes sont descendus de Machir, et des guerriers de Zabulon, pour conduire l’armée au combat.
Waɗansu suka zo daga Efraim, waɗanda ainihinsu daga Amalek ne; Benyamin yana tare da mutanen da suka bi ka. Daga Makir, shugabannin sojoji suka gangaro, daga Zebulun waɗanda suke riƙe da sandan komanda suka fito.
15 Les chefs d’Issachar ont été avec Debbora, et ont suivi les traces de Barac, qui s’est jeté dans le danger comme dans un précipice et un abîme. Ruben étant divisé contre lui-même, une dispute s’est élevée entre les magnanimes.
’Ya’yan sarautar Issakar suna tare da Debora; I, Issakar yana tare da Barak, yana binsa a guje zuwa kwari. A yankunan Ruben aka kuma bincike zuciya sosai.
16 Pourquoi habites-tu entre deux limites pour entendre les cris aigus des troupeaux? Ruben étant divisé contre lui-même, une dispute s’est élevée entre les magnanimes.
Don me kuka tsaya a wutar sansani don ku ji makiyaya suna kiran garkuna? A yankunan Ruben aka yi bincike zuciya sosai.
17 Galaad se reposait au-delà du Jourdain, et Dan vaquait à ses vaisseaux: Aser habitait sur le rivage de la mer et se tenait dans les ports.
Gileyad ya tsaya gaban Urdun. Kai kuma Dan, don me ka ka yi ta zama a wajen jiragen ruwa? Asher ya ci gaba da kasance a bakin teku ya kasance a wuraren zamansa.
18 Mais Zabulon et Nephthali offraient leurs âmes à la mort dans la région de Méromé.
Mutanen Zebulun sun kasai da rayukansu; haka ma Naftali a bakin dāgā.
19 Des rois sont venus, et ont combattu; les rois de Chanaan ont combattu à Thanach près des eaux de Mageddo, et toutefois, butinant, ils n’ont rien emporté.
“Sarakuna suka zo, suka yi yaƙi; sarakunan Kan’ana sun yi yaƙi a Ta’anak a gefen ruwan Megiddo, amma ba su ɗauki azurfa, ko ganima ba.
20 On a combattu du ciel contre eux; les étoiles, demeurant dans leur rang et dans leur cours, ont combattu contre Sisara.
Daga sama taurari suka yi faɗa, daga bakin tekuna suka yi yaƙi da Sisera.
21 Le torrent de Cison a entraîné leurs cadavres; le torrent de Cadumim, le torrent de Cison: mon âme, foule aux pieds les forts.
Kogin Kishon ya kwashe su, tsohon kogi, kogin Kishon. Ci gaba raina; ka ƙarfafa!
22 La corne des chevaux est tombée, les plus vaillants des ennemis fuyant avec impétuosité et se renversant précipitamment.
Sa’an nan kofatan dawakai suka ƙwaƙula, suna sukuwa, haka dawakansa masu ƙarfi suke tafiya.
23 Maudissez la terre de Méroz, dit l’ange du Seigneur; maudissez ses habitants, parce qu’ils ne sont pas venus au secours du Seigneur, en aide à ses plus vaillants.
Mala’ikan Ubangiji ya ce, ‘Ka la’anci Meroz.’ ‘Ka la’anci mutanensa sosai, domin ba su kawo wa Ubangiji taimako ba, su kawo wa Ubangiji taimako a kan masu ƙarfi ba.’
24 Bénie entre les femmes, Jahel, femme d’Haber, le Cinéen! et qu’elle soit bénie dans son tabernacle.
“Mafi albarka a ciki mata ta zama Yayel matar Heber Bakene, mafi albarka na mata masu zama a alfarma.
25 À Sisara demandant de l’eau, dans la coupe des princes, elle donna du lait, et elle présenta du beurre.
Ya nemi ruwa, ta kuwa ta ba shi madara; a ƙwaryar da ta dace da sarakuna ta kawo masa kindirmo.
26 Elle a mis la main gauche au clou, et la main droite à des marteaux d’ouvriers, et elle a frappé Sisara, cherchant à sa tête un endroit pour la blessure, et lui perçant fortement la tempe.
Hannunta ya ɗauki turken tenti, da hannunta na dama ta ɗauko guduma. Ta bugi Sisera, ta ragargaza kansa, ta ragargaza ta huda kunnensa.
27 Il tomba à ses pieds, défaillit et mourut; il se roulait à ses pieds, et il gisait inanimé et digne de pitié.
A ƙafafunta ya fāɗi, ya fāɗi; a can ya kwanta. A ƙafafunta ya fāɗi, ya fāɗi; a can ya fāɗi, matacce.
28 Regardant par la fenêtre, sa mère poussait des cris perçants, et de sa chambre, elle disait: Pourquoi son char diffère-t-il à revenir? pourquoi les pieds des chevaux de ses quadriges tardent-ils?
“Ta taga mahaifiyar Sisera ta leƙa; a bayan madogarar ƙofa ta yi ta ihu, ‘Me ya sa keken yaƙinsa ta daɗe ba tă dawo ba? Me ya sa dawakan keken yaƙinsa ba su dawo da wuri ba?’
29 Une des femmes de Sisara, plus sage que les autres, répondit à sa belle-mère ces paroles:
Mafi hikima cikin’yan matanta suka amsa mata, tabbatacce, ta ci gaba ta ce wa kanta,
30 Peut-être que maintenant il partage des dépouilles, et que la plus belle des femmes est choisie pour lui; on donne à Sisara des vêtements de diverses couleurs pour butin, et on lui amasse un assortiment varié pour orner son cou.
‘Ba nema suke su raba ganima ba, yarinya guda ko biyu wa kowane mutum, riguna masu launi a matsayin ganima don Sisera, riguna masu ado, riguna masu ado sosai don wuyata, dukan wannan a matsayin ganima?’
31 Ainsi périssent tous vos ennemis. Seigneur! mais que ceux qui vous aiment, brillent, comme le soleil resplendit à son lever. Et le pays se reposa durant quarante ans.
“Ta haka bari dukan abokan gābanka su hallaka, ya Ubangiji! Amma bari waɗanda suke ƙaunarka su zama kamar rana sa’ad da ta fito da ƙarfinta.” Sa’an nan ƙasar ta sami zaman lafiya shekara arba’in.

< Juges 5 >