< Juges 10 >
1 Après Abimélech, parut comme chef en Israël, Thola, fils de Phua, oncle paternel d’Abimélech, homme de la tribu d’Issachar, qui habita à Samir de la montagne d’Ephraïm;
Bayan zamanin Abimelek, sai Tola ɗan Fuwa ɗan Dodo daga Issakar ya tashi don yă ceci Isra’ila. Yana zama a Shamir a ƙasar tudu ta Efraim.
2 Et il jugea Israël pendant vingt-trois ans; et il mourut, et fut enseveli dans Samir.
Ya shugabanci Isra’ila shekara ashirin da uku sa’an nan ya mutu, aka kuma binne shi a Shamir.
3 À Thola succéda Jaïr Galaadite qui jugea Israël pendant vingt-deux ans,
Bayansa kuma sai Yayir daga Gileyad, wanda ya shugabanci Isra’ila shekara ashirin da biyu.
4 Ayant trente fils, qui montaient sur trente poulains d’ânesses, et étaient princes de trente villes dans la terre de Galaad, qui ont été appelées de son nom, Havoth-Jaïr, c’est-à-dire villes de Jaïr, jusqu’au présent jour,
Yana’ya’ya talatin, waɗanda suke hawan jakuna talatin. Sun shugabanci birane talatin a Gileyad, har wa yau ana ce da biranen Hawwot Yayir.
5 Jaïr mourut ensuite, et il fut enseveli dans un lieu dont le nom est Camon.
Sa’ad da Yayir ya mutu, sai aka binne shi a Kamon.
6 Mais les enfants d’Israël ajoutant aux anciens péchés des nouveaux, firent le mal en la présence du Seigneur, et servirent des idoles, les Baalim, les Astaroth, les dieux de Syrie, de Sidon, de Moab, des enfants d’Ammon et des Philistins; et ils abandonnèrent le Seigneur, et ne l’adorèrent point.
Isra’ilawa suka sāke yin mugayen ayyuka a gaban Ubangiji. Suka shiga bautar Ba’al da Ashtarot, da kuma allolin Aram, allolin Sidon, allolin Mowab, Ammonawa da kuma allolin Filistiyawa. Kuma domin Isra’ilawa sun bar Ubangiji ba su ƙara bauta masa ba,
7 Le Seigneur irrité contre eux, les livra aux mains des Philistins et des enfants d’Ammon.
sai ya fusata da su. Ya sayar da su ga hannun Filistiyawa da Ammonawa,
8 Et tous ceux qui habitaient au-delà du Jourdain, dans la terre de l’Amorrhéen, qui est en Galaad, furent affligés et violemment opprimés pendant dix-huit ans;
waɗanda suka fatattake su a shekarar suka kuma ragargaza su. Shekara goma sha takwas suka yi ta danne dukan Isra’ilawan da suke gabashin Urdun a Gileyad, ƙasar Amoriyawa.
9 En sorte que les enfants d’Ammon, passant le Jourdain, ravageaient Juda, Benjamin et Ephraïm: ainsi, Israël fut extrêmement affligé,
Ammonawa su ma suka haye Urdun domin su yi yaƙi da Yahuda, Benyamin da kuma gidan Efraim; Isra’ila kuwa suka kasance cikin wahala ƙwarai da gaske.
10 C’est pourquoi criant ait Seigneur, ils dirent: Nous avons péché contre vous, parce que, nous avons abandonné le Seigneur notre Dieu, et nous avons servi les Baalim,
Sa’an nan Isra’ilawa suka yi kuka ga Ubangiji, suka ce, “Mun yi maka zunubi, mun bar Allahnmu muka shiga bautar Ba’al.”
11 Le Seigneur leur répondit: N’est-ce pas que les Egyptiens, les Amorrhéens, les enfants d’Ammon, les Philistins,
Ubangiji ya ce, “Sa’ad da Masarawa, Amoriyawa, Ammonawa, Filistiyawa,
12 Les Sidoniens aussi, et Amalec et Chanaan vous ont opprimés, que vous avez crié vers moi, et que je vous ai délivrés de leur main?
Sidoniyawa, Amalekawa da kuma mutanen Mawon suka wulaƙanta ku kuka kuwa yi mini kuka, ban cece ku daga hannunsu ba?
13 Et cependant vous m’avez abandonné, et vous avez adoré des dieux étrangers: c’est pourquoi je ne recommencerai plus à vous délivrer.
Amma kuka bar ni kuka bauta wa waɗansu alloli, saboda haka ni ma ba zan ƙara cece ku ba.
14 Allez, et invoquez les dieux que vous avez choisis; qu’ils vous délivrent eux-mêmes dans le temps de l’angoisse.
Ku tafi ku yi wa allolin da kuka zaɓa. Bari su cece ku sa’ad da kuke cikin wahala!”
15 Et les enfants d’Israël dirent au Seigneur: Nous avons péché, faites-nous vous-même, en retour, tout ce qu’il vous plaira; seulement pour cette heure délivrez-nous.
Amma Isra’ilawa suka ce wa Ubangiji, “Mu dai mun yi zunubi. Ka yi da mu abin da ka ga dama, amma muna roƙonka ka cece mu a yanzu.”
16 Disant cela, ils jetèrent hors de leur territoire les idoles des dieux étrangers, et ils servirent le Seigneur Dieu, qui fut sensible à leurs misères.
Sa’an nan suka zubar da allolin nan daga cikinsu suka bauta wa Ubangiji. Ubangiji kuwa bai ƙara daure da azabar da Isra’ila suke sha ba.
17 C’est pourquoi les enfants d’Ammon, jetant de grands cris, plantèrent leurs tentes en Galaad; et les enfants d’Israël, s’étant réunis contre eux, campèrent à Maspha.
Sa’ad da aka kira Ammonawa su yi ɗamarar yaƙi, sai su kuma kafa sansani a Gileyad, Isra’ilawa kuwa suka tattaru suka kafa sansani Mizfa.
18 Et les princes de Galaad se dirent les uns aux autres: Le premier d’entre nous qui commencera à combattre contre les enfants d’Ammon, sera le chef du peuple de Galaad.
Shugabannin mutanen Gileyad suka cewa juna, “Duk wanda zai fara fāɗa wa Ammonawa shi zai zama shugaban duk waɗanda suke zama a Gileyad.”