< Josué 6 >

1 Or, Jéricho était fermée et fortifiée, dans la crainte des enfants d’Israël, et nul n’osait sortir ou entrer.
Ƙofofin Yeriko kuwa a kulle suke ciki da waje saboda Isra’ilawa, ba mai fita babu kuma mai shiga.
2 Et le Seigneur dit à Josué: Voici que j’ai livré en la main Jéricho et son roi et tous ses braves guerriers.
Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Duba, na ba ka nasara a kan Yeriko, duk da sarkinta da mayaƙanta.
3 Faites le tour de la ville, vous tous combattants, une fois par jour. Ainsi ferez-vous pendant six jours.
Da kai da dukan sojoji, ku zaga birnin sau ɗaya kullum. Ku yi haka har kwana shida.
4 Mais, au septième jour, que des prêtres portent sept trompettes dont on fait usage pendant le Jubilé, et qu’ils précèdent l’arche de l’alliance; et sept fois vous ferez le tour de la ville, et les prêtres sonneront des trompettes.
Ka sa firistoci guda bakwai su riƙe ƙahoni raguna su kasance a gaban akwatin alkawari. A rana ta bakwai sai ku zaga birnin sau bakwai, firistocin suna busa ƙahoni.
5 Et lorsque le son de la trompette se fera entendre, d’abord prolongé, puis entrecoupé, et qu’il retentira à vos oreilles, tout le peuple ensemble poussera les plus grands cris, et les murailles de la ville s’écrouleront jusqu’aux fondements, et chacun entrera par l’endroit vis-à-vis duquel il se trouvera.
Sa’ad da kuka ji sun ɗauki dogon lokaci suna busa ƙaho, sai mutane gaba ɗaya su tā da murya su yi ihu da ƙarfi; katangar birnin kuwa za tă rushe, sai sojoji su haura, ko wanne yă nufi inda ya fuskanta kai tsaye.”
6 Josué, fils de Nun, appela donc les prêtres et leur dit: Portez l’arche de l’alliance, et que sept autres prêtres portent sept trompettes du jubilé, et qu’ils marchent devant l’arche du Seigneur.
Yoshuwa ɗan Nun kuwa ya kira firistoci ya ce musu, “Ku ɗauki akwatin alkawari, ku sa firistoci guda bakwai su riƙe ƙahoni su kasance a gabansa.”
7 Au peuple aussi il dit: Allez, et faites le tour de la ville, armés, précédant l’arche du Seigneur.
Sai ya umarci jama’a ya ce, “Mu je zuwa! Ku zaga birnin, masu tsaro da makamai su shiga gaban akwatin alkawarin Ubangiji.”
8 Or, lorsque Josué eut achevé ces paroles, et que les sept prêtres sonnaient des sept trompettes devant l’arche de l’alliance du Seigneur,
Da Yoshuwa ya gama yin wa mutane magana, sai firistoci guda bakwai waɗanda suke riƙe da ƙahoni guda bakwai a gaban Ubangiji suka sha gaba suna busa ƙahoninsu, akwatin alkawari kuwa yana biye da su.
9 Et que toute la troupe armée précédait, le reste du peuple suivait l’arche, et tout retentissait du son des trompettes.
Masu tsaro da makamai kuma suna gaban firistoci waɗanda suke busa ƙahoni, masu tsaro daga baya kuma suna bin akwatin alkawari, ana ta busa ƙahoni.
10 Or, Josué avait commandé au peuple, disant: Vous ne crierez point, et votre voix ne sera point entendue, et aucun mot ne sortira de votre bouche, jusqu’à ce que vienne le jour auquel je vous dirai: Criez et vociférez.
Amma Yoshuwa ya umarci mutane ya ce, “Kada ku yi kururuwar yaƙi, kada ku tā da murya, kada ku ce kome, sai ranar da na ce ku yi ihu, a sa’an nan ne sai ku yi ihu!”
11 L’arche du Seigneur fit donc une fois le tour de la ville pendant le jour, et, revenue au camp, elle y demeura.
Sai ya sa aka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji aka kewaye birnin da shi sau ɗaya, sa’an nan mutane suka dawo masauƙinsu suka kwana a can.
12 Mais Josué s’étant levé durant la nuit, les prêtres portèrent l’arche du Seigneur,
Kashegari, Yoshuwa ya tashi da sassafe, firistoci kuma suka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji.
13 Et sept d’entre eux, les sept trompettes dont on fait usage dans le jubilé; et ils précédaient l’arche du Seigneur, marchant et sonnant des trompettes, et le peuple armé allait devant eux, et le reste du peuple suivait l’arche et sonnait des trompettes.
Firistoci guda bakwai waɗanda suke riƙe da ƙahoni guda bakwai suka shiga gaba, suna takawa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji suna kuma busa ƙahoni, masu tsaro ɗauke da makamai suna gabansu, sai masu tsaro da suke baya suna biye da akwatin alkawarin Ubangiji.
14 Et le second jour ils firent le tour de la ville une fois, puis ils revinrent dans le camp. Ainsi firent-ils pendant six jours.
A rana ta biyu suka sāke zaga birnin sau ɗaya, suka kuma koma masauƙinsu. Haka suka yi har kwana shida.
15 Mais le septième jour, se levant dès l’aurore, ils firent le tour de la ville, comme il leur avait été ordonné, sept fois.
A rana ta bakwai, suka tashi da sassafe suka zaga birnin sau bakwai yadda suka saba. A wannan rana kaɗai ne suka zaga birnin sau bakwai.
16 Et lorsqu’au septième tour, les prêtres sonnaient de la trompette, Josué dit à tout Israël: Poussez de grands cris; car le Seigneur vous a livré la ville.
A zagawa ta bakwai, da firistoci suka busa ƙahoni, sai Yoshuwa ya ba sojojin umarni ya ce, “Ku yi ihu, gama Ubangiji ya ba ku birnin!
17 Et que cette ville soit anathème, et que tout ce qui s’y trouve, soit consacré au Seigneur; que la seule Rahab, la femme de mauvaise vie, vive avec tous ceux qui sont à elle dans sa maison; car elle a caché les messagers que nous avons envoyés.
Birnin da dukan abin da yake cikinta za a miƙa su ga Ubangiji. Rahab karuwan nan kaɗai ce, da dukan waɗanda suke tare da ita a gidanta za a bari da rai domin ta ɓoye’yan leƙen asirin ƙasa da muka aika.
18 Mais vous, prenez garde que vous ne touchiez à aucune des choses qui vous ont été défendues, que vous ne soyez coupables de prévarication, et que tout le camp d’Israël ne soit sous le péché, et n’éprouve de la disgrâce.
Amma, ba za ku ɗauki wani abin da za a hallaka ba, idan kuka yi haka, za ku jawo masifa da hallaka a kan mutanen Isra’ila a inda kuka sauka.
19 Ainsi, que tout ce qu’il y aura d’or et d’argent, et de vases d’airain et de fer, soit consacré au Seigneur et déposé dans ses trésors.
Dukan azurfa da zinariya, da kwanonin tagulla da na ƙarfe, keɓaɓɓu ne ga Ubangiji, dole a sa su cikin ma’ajin Ubangiji.”
20 Tout le peuple donc poussant de grands cris, et les trompettes sonnant, quand la voix et le son eurent retenti aux oreilles de la multitude, les murs soudain s’écroulèrent, chacun monta par le lieu qui était vis-à-vis de lui, et ils prirent la ville.
Da aka busa ƙahoni, sojoji suka yi ihu, da jin ƙarar ƙahoni, mutane suka kuma yi ihu, sai katangar ta rushe; dukan mutanen kuwa suka shiga birnin kai tsaye, suka yi nasara a kanta.
21 Et ils tuèrent tout ce qui s’y trouvait, depuis l’homme jusqu’à la femme, depuis l’enfant jusqu’au vieillard. Les bœufs aussi, et les brebis et les ânes, ils les frappèrent du tranchant du glaive.
Suka miƙa wa Ubangiji birnin, suka hallaka kowane abu mai ran da yake cikin birnin da takobi, maza da mata, yara da tsofaffi, shanu, tumaki da jakuna.
22 Mais Josué dit aux deux hommes qui avaient été envoyés comme espions: Entrez dans la maison de la femme de mauvaise vie, et faites-la sortir, ainsi que tout ce qui est à elle, comme vous lui avez assuré par serment.
Yoshuwa ya ce wa mutanen nan biyu waɗanda suka je leƙen asirin ƙasar, “Ku shiga gidan karuwan nan ku fitar da ita da duk waɗanda suke nata bisa ga alkawarin da kuka yi mata.”
23 Et les deux jeunes hommes étant entrés, firent sortir Rahab, son père et sa mère, ses frères aussi, tout ce qui leur appartenait et toute sa parenté, et les firent demeurer hors du camp d’Israël.
Sai samarin waɗanda suka je leƙen asirin suka shiga suka fitar da Rahab, mahaifinta da mahaifiyarta, da’yan’uwanta da duk abin da yake nata. Suka fitar da iyalinta gaba ɗaya suka sa su a wani wuri, ba a cikin masauƙin Isra’ilawa ba.
24 Mais la ville et tout ce qui s’y trouvait, ils les brûlèrent, excepté l’or, l’argent, les vases d’airain et de fer, qu’ils consacrèrent pour le trésor du Seigneur.
Sa’an nan suka ƙona birnin tare da dukan abin da yake ciki tatas, amma suka sa azurfa da zinariya da kayan tagulla da na ƙarfe a cikin ma’aji na haikalin Ubangiji.
25 Quant à Rahab, la femme de mauvaise vie, à la maison de son père et à tout ce qu’elle avait, Josué leur conserva la vie, et ils ont habité au milieu d’Israël jusqu’au présent jour, parce qu’elle cacha les messagers qu’il avait envoyés pour explorer Jéricho. En ce temps-là, Josué fit une imprécation, disant:
Amma Yoshuwa ya bar Rahab karuwan nan bai kashe ta ba, ita da iyalinta da duk abin da yake nata, domin ita ta ɓoye mutanen da Yoshuwa ya aika Yeriko don su leƙo asirin ƙasar kuma ta zauna tare da Isra’ilawa har wa yau.
26 Maudit devant le Seigneur; l’homme qui relèvera et rebâtira la ville de Jéricho! Que ce soit sur son premier-né qu’il en jette les fondements, et que ce soit sur le dernier de ses enfants qu’il en pose les portes.
A lokacin nan Yoshuwa ya yi wannan alkawari cewa, “Ubangiji zai tsine wa mutumin da zai yi ƙoƙarin sāke gina birnin nan, Yeriko. “A bakin ran ɗan farinsa zai kafa harsashin birnin; a bakin ran ɗan autansa kuma zai sa ƙofofin birnin.”
27 Le Seigneur fut donc avec Josué, et son nom se répandit sur toute la terre.
Ubangiji ya kasance tare da Yoshuwa, aka kuma san da shi a duk fāɗin ƙasar.

< Josué 6 >