< Josué 1 >

1 Or, il arriva après la mort de Moïse, serviteur du Seigneur, que le Seigneur parla à Josué, fils de Nun, serviteur de Moïse, et qu’il lui dit:
Bayan mutuwar Musa bawan Ubangiji, sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa ɗan Nun, mataimakin Musa,
2 Moïse, mon serviteur est mort, lève-toi, passe le Jourdain, toi et tout le peuple avec toi, et va dans la terre que je donnerai moi-même aux enfants d’Israël.
“Bawana Musa ya mutu. Yanzu sai ka tashi tare da mutanen nan duka, ku yi shirin ƙetare kogin Urdun zuwa cikin ƙasar da zan ba su Isra’ilawa.
3 Tout lieu que la plante de votre pied aura foulé, je vous le livrerai, comme j’ai dit à Moïse.
Zan ba ku duk ƙasar da za ku taka, kamar yadda na yi wa Musa alkawari.
4 Depuis le désert et le Liban jusqu’au grand fleuve d’Euphrate, toute la terre des Héthéens, jusqu’à la grande mer contre le couchant du soleil, sera votre limite.
Ƙasar da ta kama daga hamada zuwa Lebanon, zuwa babban Kogin, wato, Kogin Yuferites, da dukan ƙasar Hittiyawa zuwa Bahar Rum, wajen yamma.
5 Nul ne pourra vous résister pendant tous les jours de ta vie: comme j’ai été avec Moïse, ainsi je serai avec toi, je ne te laisserai, ni ne t’abandonnerai.
Ba wanda zai yi tsayayya da kai dukan kwanakin ranka. Yadda na kasance tare da Musa, haka zan kasance tare da kai; ba zan taɓa rabuwa da kai ba; ba zan yashe ka ba.
6 Prends courage et sois fort, car c’est toi qui partageras à ce peuple par le sort la terre, au sujet de laquelle j’ai juré à leurs pères que je la leur livrerais.
“Ka yi ƙarfin hali ka kuma kasance da rashin tsoro, gama kai za ka bi da mutanen nan har su karɓi ƙasar da na yi wa kakanninsu alkawari zan ba su.
7 Prends donc courage, et sois très fort, afin que tu gardes et que tu pratiques toute la loi que t’a prescrite Moïse, mon serviteur: ne t’en détourne ni à droite ni à gauche, afin que tu comprennes tout ce que tu fais.
Ka yi ƙarfin hali ka kuma kasance da rashin tsoro, ka yi lura fa, ka yi biyayya da dokokin da bawana Musa ya ba ka; kada ka kauce ga bin dokokin ko hagu ko dama, domin ka yi nasara a duk, inda za ka je.
8 Que le livre de cette loi ne s’éloigne point de ta bouche; tu le méditeras les jours et les nuits, afin que tu gardes et pratiques tout ce qui y est écrit: alors tu dirigeras ta voie et tu la comprendras.
Kada ka bar Littafin Dokokin nan yă rabu da bakinka, sai dai ka yi ta tunani game da shi dare da rana, don ka lura, ka yi duk abin da aka rubuta a ciki, ta haka ne za ka yi nasara cikin duk abin da za ka yi.
9 Voici que je te l’ordonne, prends courage et sois fort. Ne crains point, et ne t’épouvante point, parce que le Seigneur ton Dieu est avec toi en quelque lieu que tu ailles.
Ba ni na umarce ka ba? Ka yi ƙarfin hali ka kuma kasance da rashin tsoro. Kada ka ji tsoro; kada ka karaya, gama Ubangiji Allahnka zai kasance tare da kai duk inda za ka je.”
10 Et Josué ordonna aux princes du peuple, disant: Passez par le milieu du camp, et commandez au peuple, et dites:
Saboda haka sai Yoshuwa ya umarci shugabannin mutane,
11 Préparez-vous des vivres, parce qu’après trois jours vous passerez le Jourdain, et vous entrerez entrerez pour la posséder, dans la terre que le Seigneur votre Dieu va vous donner.
“Ku ratsa cikin sansani, ku gaya wa mutane, ‘Ku shirya guzurinku. Nan da kwana uku za ku ƙetare Urdun a nan, don ku je ka mallaki ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ta zama taku.’”
12 Aux Rubénites aussi et aux Gadites et à la demi-tribu de Manassé, il dit:
Amma Yoshuwa ya ce wa mutanen Ruben, mutanen Gad da kuma rabin mutanen kabilar Manasse,
13 Souvenez-vous de ce que vous ordonna Moïse, serviteur du Seigneur, disant: Le Seigneur votre Dieu vous a donné le repos et toute cette terre.
“Ku tuna da umarnin da Musa bawan Ubangiji ya yi muku. ‘Ubangiji Allahnku ya ba ku hutawa, ya kuma ba ku wannan ƙasa.’
14 Vos femmes, vos enfants et vos bestiaux demeureront dans la terre que vous a livrée Moïse en deçà du Jourdain; mais vous, passez armés devant vos frères, vous tous forts de la main, et combattez pour eux,
Matanku, da yaranku, da kuma dabbobinku za su kasance a ƙasar da Musa ya ba ku a gabashin Urdun, amma dole mayaƙanku, su yi shirin yaƙi su haye, su yi gaba tare da’yan’uwanku, za ku taimaki’yan’uwanku
15 Jusqu’à ce que le Seigneur donne le repos à vos frères, comme il vous l’a donné à vous-mêmes; et qu’ils possèdent eux aussi la terre que le Seigneur votre Dieu va leur donner: et c’est ainsi que vous retournerez dans la terre de votre possession, et que vous habiterez dans cette terre que vous a donnée Moïse, serviteur de Dieu en deçà du Jourdain contre le levant.
har sai lokacin da Ubangiji ya ba su hutawa, kamar yadda ya yi muku, kuma har sai su ma sun ƙwace ƙasar da Ubangiji Allahnku ya yi alkawari zai ba su. Bayan haka ne za ku koma ku mallaki ƙasarku, wadda Musa bawan Ubangiji ya ba ku a gabashin Urdun.”
16 Et ils répondirent à Josué et dirent: Nous ferons tout ce que tu nous as ordonné; et nous irons partout où tu nous enverras.
Sai suka amsa wa Yoshuwa suka ce, “Duk abin da ka ce mu yi, za mu yi. Duk inda kuma ka aike mu, za mu je.
17 Comme nous avons obéi en toutes choses à Moïse, ainsi nous t’obéirons à toi-même. Seulement que le Seigneur ton Dieu soit avec toi, comme il a été avec Moïse.
Kamar yadda muka yi wa Musa biyayya, haka za mu yi maka biyayya. Ubangiji Allahnka ya kasance tare da Musa.
18 Que celui qui contredira ta parole, et qui n’obéira pas à tous les discours que tu lui prescriras, meure; seulement, toi, fortifie-toi, et agis courageusement.
Duk wanda ya yi wa maganarka tawaye, ya ƙi yă yi biyayya da maganarka, ko da umarnin da ka ba shi, za a kashe shi. Ka dai ƙarfafa ka kuma yi ƙarfi hali!”

< Josué 1 >