< Jonas 2 >

1 Et Jonas pria le Seigneur son Dieu du ventre du poisson.
Daga ciki cikin kifi, Yunana ya yi addu’a ga Ubangiji Allahnsa.
2 Et il dit: [J’ai crié vers le Seigneur du milieu de ma tribulation, et il m’a exaucé; du sein de l’enfer j’ai crié, et vous avez entendu ma voix. (Sheol h7585)
Ya ce, “A cikin damuwata na yi kira ga Ubangiji, ya kuwa amsa mini. Daga cikin zurfi kabari na yi kiran neman taimako, ka kuwa saurari kukata. (Sheol h7585)
3 Et vous m’avez jeté dans le profond d’un gouffre, dans le cœur d’une mer, et des eaux m’ont environné; toutes vos vagues et vos flots ont passé sur moi.
Cikin tashin hankali, ka jefa ni cikin zurfafa, a tsakiyar teku, ka kuma jujjuya ni a cikin ruwa; dukan raƙuman ruwanka da ambaliyarka sun bi ta kaina.
4 Et moi j’ai dit: Je suis rejeté de la présence de vos yeux, mais je verrai encore votre temple saint.
Sai na ce, ‘An kore ni daga fuskarka; duk da haka zan sāke duba wajen haikalinka mai tsarki.’
5 Des eaux m’ont environne jusqu’à l’âme, un abîme m’a enveloppé, une mer a couvert ma tête.
Ruwayen da suke kewaye da ni sun yi mini barazana, zurfi kuma ya kewaye ni, ciyayin ruwa suna nannaɗe kewaye da ni.
6 Je suis descendu jusqu’aux fondements des montagnes; les barrières de la terre étaient fermées sur moi pour toujours; mais vous préserverez ma vie de la corruption, Seigneur mon Dieu.
Na nutsa har ƙarƙashin tuddai; a ƙarƙashin duniya, ka rufe ni har abada. Amma ka dawo da raina daga rami, Ya Ubangiji Allahna.
7 Lorsque mon âme était resserrée en moi, je me suis souvenu du Seigneur, afin que ma prière vienne jusqu’à vous, jusqu’à votre temple saint.
“Sa’ad da na ji raina yana rabuwa da ni, na tuna da kai ya Ubangiji, addu’ata kuma ta kai gare ka, a haikalinka mai tsarki.
8 Ceux qui s’attachent aux vanités inutilement, abandonnent leur miséricorde.
“Waɗanda suka maƙale wa gumaka marasa amfani, sukan ƙyale alherin da zai kasance nasu.
9 Mais moi, je vous immolerai des victimes avec la voix de la louange; tout ce que j’ai voué, je le rendrai au Seigneur, pour mon salut.
Amma ni, da waƙar godiya, zan miƙa tawa hadaya gare ka. Abin da na yi alkawari, shi ne zan yi. Ceto yakan zo ne kawai daga wurin Ubangiji.”
10 Et le Seigneur parla au poisson, et il jeta Jonas sur la terre.
Sai Ubangiji ya umarci kifin, kifin kuwa ya amayar da Yunana a gaɓan teku.

< Jonas 2 >