< Jean 6 >

1 Après cela Jésus s’en alla de l’autre côté de la mer de Galilée, c’est-à-dire de Tibériade;
Bayan waddannan abubuwa, Yesu ya ketare tekun Galili, wanda a ke kira tekun Tibariya.
2 Et une grande multitude le suivait, parce qu’ils voyaient les miracles qu’il faisait sur ceux qui étaient malades.
Sai taro mai yawa suka bi shi domin suna ganin alamu da yake yi akan marasa lafiya.
3 Jésus monta donc sur la montagne, et là il était assis avec ses disciples.
Sai Yesu ya hau dutse ya zauna a can tare da almajiransa.
4 Cependant approchait la Pâque, jour de la fête des Juifs.
(Kuma da idin Ketarewa, wato idin Yahudawa, ya kusato.)
5 Jésus donc ayant levé les yeux et vu qu’une très grande multitude était venue à lui, dit à Philippe: Où achèterons-nous des pains, pour que ceux-ci mangent?
Da Yesu ya daga kai sai ya ga babban taro yana zuwa wurinsa, sai ya ce ma Filibus, “Ina za mu sayi gurasar da Mutanen nan za su ci?”
6 Or il disait cela pour l’éprouver; car pour lui il savait ce qu’il devait faire.
( Ya fadi haka ne domin ya gwada shi, saboda shi kansa ya san abin da zai yi.)
7 Philippe lui répondit: Deux cents deniers de pain ne leur suffiraient pas pour que chacun d’eux en eût même un petit morceau.
Filibus ya amsa masa, “gurasar dinari biyu ma ba zata ishi kowannensu ya samu ko kadan ba.”
8 Un de ses disciples, André, frère de Simon-Pierre, lui dit:
Daya daga cikin almajiransa, wato Andarawus, dan'uwan Siman Bitrus, ya ce masa,
9 Il y a ici un petit garçon qui a cinq pains d’orge et deux poissons: mais qu’est-ce que cela pour tant de monde?
“Ga wani dan yaro nan da dunkule biyar na sha'ir, da kifi biyu. Amma menene wadannan za su yi wa mutane masu yawa?”
10 Jésus dit donc: Faites asseoir ces hommes. Or il y avait beaucoup d’herbe en ce lieu. Ces hommes s’assirent donc au nombre d’environ cinq mille.
Yesu ya ce, “ku sa mutane su zauna.”( wurin kuwa akwai ciyawa.) Sai mazajen suka zauna, sun kai wajen dubu biyar.
11 Alors Jésus prit les pains, et quand il eut rendu grâces, il les distribua à ceux qui étaient assis; et de même des poissons, autant qu’ils en voulaient.
Sai Yesu ya dauki gurasar, bayan da ya yi godiya, sai ya rarraba wa wadanda suke zaune. Haka kuma ya rarraba kifin gwargwadon abin da zai ishe su.
12 Lorsqu’ils furent rassasiés, il dit à ses disciples: Amassez les morceaux qui sont restés, pour qu’ils ne se perdent pas.
Da Mutanen suka ci suka kuma koshi, sai ya ce wa almajiransa, ku tattara gutsattsarin da suka rage, kada ya zama asara.”
13 Ils les amassèrent donc, et remplirent douze paniers de morceaux des cinq pains d’orge qui restèrent à ceux qui avaient mangé.
Sai suka cika kwanduna goma sha biyu da gutsattsarin gurasar nan biyar da ya rage bayan da kowa ya ci.
14 Or ces hommes, ayant vu le miracle que Jésus avait fait, disaient: Celui-ci est vraiment le prophète qui doit venir dans le monde.
Da jama'a suka ga alamar da ya yi, sai suka ce, “Hakika wannan shi ne annabin nan mai zuwa cikin duniya.
15 Et Jésus, ayant connu qu’ils devaient venir pour l’enlever et le faire roi, s’enfuit de nouveau sur la montagne tout seul.
“Da Yesu ya gane suna shirin zuwa su dauke shi da karfi da yaji su nada shi sarki, sai ya sake komawa kan dutsen da kansa.
16 Dès que le soir fut venu, ses disciples descendirent à la mer.
Da yamma ta yi, sai almajiransa suka gangara teku.
17 Et quand ils furent montés dans la barque, ils vinrent de l’autre côté de la mer, vers Capharnaüm. Or les ténèbres s’étaient déjà faites, et Jésus n’était pas venu à eux.
Suka shiga cikin jirgi, suka haye teku zuwa kafarnahum. (A lokacin duhu ya yi, Yesu kuwa bai riga ya iso wurinsu ba tukuna.)
18 Cependant, au souffle d’un grand vent, la mer s’enflait.
Iska mai karfin gaske tana kadawa, kuma tekun yana hargowa.
19 Après donc qu’ils eurent ramé environ vingt-cinq ou trente stades, ils virent Jésus marchant sur la mer et s’approchant de la barque, et ils eurent peur.
Bayan da almajiran suka yi tuki na wajen kimanin mil ashirin da biyar ko talatin, sai suka hango Yesu yana tafiya a kan teku ya kuma kusa da jirgin, sai suka firgita.
20 Mais il leur dit: C’est moi, ne craignez point.
Amma ya ce masu, “Ni ne! kada ku firgita.”
21 C’est pourquoi ils voulurent le prendre dans la barque, et aussitôt la barque se trouva à la terre où ils allaient.
Sa'an nan suka yarda suka karbe shi a cikin jirgin, kuma nan da nan jirgin ya kai gacci.
22 Le jour suivant, le peuple, qui se tenait de l’autre côté de la mer, observa qu’il n’y avait eu là qu’une seule barque, que Jésus n’était point entré avec ses disciples dans cette barque, mais que ses disciples seuls étaient partis;
Kashe gari, sauran taron da suke tsaye a dayan hayin tekun suka ga cewa babu wani jirgi a wajen sai dayan, Yesu kuma bai shiga ciki da almajiransa ba, amma almajiransa suka tafi su kadai.
23 Cependant, d’autres barques vinrent de Tibériade, près du lieu où ils avaient mangé le pain, le Seigneur ayant rendu grâces.
Sai dai, akwai wadansu jirage da suka zo daga Tibariya kusa da wurin da taron suka ci gurasa bayan da Ubangiji ya yi godiya.
24 Quand le peuple eut vu que Jésus n’était point là, ni ses disciples, il monta lui aussi dans les barques et vint à Capharnaüm, cherchant Jésus.
Sa'anda taron suka gane cewa Yesu da almajiransa ba su wurin, su da kansu su ka shiga cikin jiragen suka tafi Kafarnahum neman Yesu.
25 Et l’ayant trouvé de l’autre côté de la mer, ils lui dirent: Maître, comment êtes-vous venu ici?
Da suka same shi a hayin tekun, suka ce masa, “Mallam, yaushe ka zo nan?”
26 Jésus leur répondit, et dit: En vérité, en vérité, je vous le dis, vous me cherchez, non parce que vous avez vu des miracles, mais parce que vous avez mangé des pains et avez été rassasiés.
Yesu ya amsa masu, da cewa, “hakika, kuna nema na ne, ba don kun ga alamu ba, amma domin kun ci gurasar nan kun koshi.
27 Travaillez, non pas en vue de la nourriture qui périt, mais de celle qui demeure pour la vie éternelle, et que le Fils de l’homme vous donnera; car Dieu le Père l’a scellée de son sceau. (aiōnios g166)
Ku daina yin wahala a kan neman abinci mai lalacewa, sai dai a kan abinci mai dawwama wanda zai kaiku ga rai madawwami wanda Dan Mutum zai ba ku, domin Ubangiji Allah ya sa hatiminsa a kansa.” (aiōnios g166)
28 Ils lui demandèrent: Que ferons-nous pour travailler aux œuvres de Dieu?
Sai suka ce Masa, “Me za mu yi, domin mu aikata ayyukan Allah?
29 Jésus répondit et leur dit: L’œuvre de Dieu, c’est que vous croyiez en celui qu’il a envoyé.
Yesu ya amsa, “Wannan shi ne aikin Allah: wato ku gaskata da wanda ya aiko.”
30 Ils lui repartirent: Quel miracle donc faites-vous pour que nous voyions et que nous croyions en vous?
Sai suka ce masa, “To wace alama za ka yi, don mu gani mu gaskata ka?
31 Nos pères ont mangé la manne dans le désert, comme il est écrit: Il leur a donné du pain du ciel à manger.
Me za ka yi? Kakanninmu sun ci manna a jeji, kamar yadda aka rubuta, “Ya ba su gurasa daga sama su ci.”
32 Jésus leur dit donc: En vérité, en vérité, je vous le dis, Moïse ne vous a point donné le pain du ciel, mais c’est mon Père qui vous donne le vrai pain du ciel.
Sa'an nan Yesu ya ce masu, “hakika, hakika, ina gaya maku ba Musa ne ya ba ku gurasa nan daga sama ba, amma Ubana ne ya baku gurasa ta gaskiya daga sama.
33 Car le pain de Dieu est celui qui descend du ciel, et donne la vie au monde.
Gurasar Allah itace mai saukowa daga sama mai kuma bada rai ga duniya,”
34 Ils lui dirent donc: Seigneur, donnez-nous toujours ce pain.
Sai suka ce masa, “Mallam, ka rika ba mu irin wannan gurasa kodayaushe.”
35 Et Jésus leur dit: C’est moi qui suis le pain de vie: qui vient à moi n’aura pas faim, et qui croit en moi n’aura jamais soif.
Yesu ya ce masu, “Ni ne gurasa mai ba da rai. Wanda ya zo wurina ba zai ji yunwa ba, wanda kuma ya gaskanta da ni ba zai kara jin kishi ba.
36 Mais je vous l’ai dit, vous m’avez vu, et vous ne croyez point.
Amma na gaya maku cewa, hakika kun gan ni, duk da haka ba ku ba da gaskiya ba.
37 Tout ce que me donne mon Père viendra à moi, et celui qui vient à moi, je ne le rejetterai pas dehors:
Duk wanda Uba ya bani zai zo gare ni, wanda kuwa ya zo gare ni ba zan kore shi ba ko kadan.
38 Parce que je suis descendu du ciel, non pour faire ma volonté, mais la volonté de celui qui m’a envoyé.
Gama na sauko daga sama, ba domin in bi nufin kaina ba, sai dai nufin wanda ya aiko ni.
39 Or c’est la volonté de mon Père qui m’a envoyé, que de tout ce qu’il m’a donné, rien ne se perde, mais que je le ressuscite au dernier jour.
Wannan shi ne nufin wanda ya aiko ni, kada in rasa ko daya daga cikin wadannan da ya bani, sai dai in tashe su a ranar karshe.
40 C’est la volonté de mon Père qui m’a envoyé, que quiconque voit le Fils et croit en lui ait la vie éternelle, et moi je le ressusciterai au dernier jour. (aiōnios g166)
Gama wannan shi ne nufin Ubana, duk wanda yake ganin Dan ya kuma gaskata da shi zai sami rai madawwami, ni kuma zan tashe shi a ranar karshe. (aiōnios g166)
41 Cependant les Juifs murmuraient contre lui, parce qu’il avait dit: Moi je suis le pain vivant qui suis descendu du ciel,
Sai Yahudawa suka yi gunaguni akansa, domin ya ce, “Nine Gurasar da ta sauko daga sama.”
42 Et ils disaient: N’est-ce pas là Jésus, le fils de Joseph, dont nous connaissons le père et la mère? Comment donc dit-il: Je suis descendu du ciel?
Suka ce, “Ba wannan ne Yesu Dan Yusufu, wanda Ubansa da Uwarsa mun san su ba? Ta yaya yanzu zai ce, 'Na ya sauko daga sama'?
43 Mais Jésus répondit et leur dit: Ne murmurez point entre vous;
Yesu ya amsa, ya ce masu, “Kada ku yi gunaguni a junanku.
44 Nul ne peut venir à moi, si le Père qui m’a envoyé ne l’attire; et moi je le ressusciterai au dernier jour.
Ba mai iya zuwa wurina sai dai in Uba wanda ya aiko ni ya jawo shi, ni kuwa zan tashe shi a rana ta karshe.
45 Il est écrit dans les prophètes: Ils seront tous enseignés de Dieu. Quiconque a entendu la voix du Père et a appris, vient à moi.
A rubuce yake cikin litattafan anabawa cewa, 'Dukkansu Allah zai koya masu'. Duk wanda ya ji ya kuma koya daga wurin Uba, ya kan zo gare ni.
46 Non que personne ait vu le Père, si ce n’est celui qui est de Dieu; car celui-là a vu le Père.
Ba cewa wani ya taba ganin Uban ba, sai shi wanda yake daga wurin Allah - shine ya ga Uban.
47 En vérité, en vérité, je vous le dis: Qui croit en moi, a la vie éternelle. (aiōnios g166)
Hakika, hakika, wanda ya bada gaskiya, yana da rai Madawwami. (aiōnios g166)
48 C’est moi qui suis le pain de la vie.
Ni ne Gurasa ta rai.
49 Vos pères ont mangé la manne dans le désert et sont morts.
Ubanninku sun ci manna cikin jeji, suka kuma mutu.
50 Voici le pain qui descend du ciel, afin que si quelqu’un en mange, il ne meure point.
Ga gurasa da ta sauko daga sama, domin mutum ya ci daga cikinta ba kuwa zai mutu ba.
51 Je suis le pain vivant, moi qui suis descendu du ciel. Si quelqu’un mange de ce pain, il vivra éternellement; et le pain que je donnerai, c’est ma chair pour la vie du monde. (aiōn g165)
Ni ne gurasa mai rai da ya sauko daga sama. Duk wanda ya ci daga gurasar, zai rayu har abada. Wannan gurasar da zan bayar jiki na ne don ceton duniya.” (aiōn g165)
52 Les Juifs donc disputaient entre eux, disant: Comment celui-ci peut-il nous donner sa chair à manger?
Sai Yahudawa suka fusata a tsakanin junansu suka kuma fara gardama, cewa, “Yaya mutumin nan zai iya bamu naman jikinsa mu ci?
53 Et Jésus leur dit: En vérité, en vérité, je vous le dis: Si vous ne mangez la chair du Fils de l’homme, et ne buvez son sang, vous n’aurez point la vie en vous.
Sai Yesu ya ce masu, “hakika, hakika, in ba ku ci naman jikin Dan mutum ba, ba ku kuma sha jininsa ba, ba za ku sami rai a cikin ku ba.
54 Qui mange ma chair et boit mon sang a la vie éternelle; et moi, je le ressusciterai au dernier jour. (aiōnios g166)
Dukan wanda ya ci nama na ya kuma sha jinina yana da rai Madawwami, ni kuwa zan tashe shi a ranar karshe. (aiōnios g166)
55 Car ma chair est vraiment nourriture et mon sang est vraiment breuvage;
Domin namana abinci ne na gaske, jinina kuma abin sha ne na gaskiya.
56 Qui mange ma chair et boit mon sang demeure en moi et moi en lui.
Duk wanda ya ci namana, ya kuma sha jinina yana zamne a ciki na, ni kuma a cikinsa.
57 Comme mon Père qui est vivant m’a envoyé, et que moi je vis par mon Père, ainsi celui qui me mange vivra aussi par moi.
Kamar yadda rayayyen Uba ya aiko ni, nake kuma rayuwa saboda Uban, haka ma wanda ya ci namana, zai rayu sabo da ni.
58 Voici le pain qui est descendu du ciel. Ce n’est pas comme vos pères, qui ont mangé la manne et sont morts. Celui qui mange ce pain vivra éternellement. (aiōn g165)
Wannan itace gurasar da ta sauko daga sama, ba irin wadda Ubanninku suka ci suka mutu ba. Dukan wanda ya ci gurasar zai rayu har abada.” (aiōn g165)
59 Il dit ces choses, enseignant dans la synagogue, à Capharnaüm.
Yesu ya fadi wadan nan abubuwa a cikin majami'a sa'ad da yake koyarwa a Kafarnahum.
60 Mais beaucoup de ses disciples l’ayant entendu, dirent: Ces paroles sont dures et qui peut les écouter?
Da jin haka, da yawa daga cikin almajiransa suka ce, “Wannan Magana yana da karfi, wa zai iya jinta?”
61 Or Jésus sachant en lui-même que ses disciples en murmuraient leur dit: Cela vous scandalise?
Yesu, kuwa da yake ya sani a ransa da cewa almajiransa suna gunagunin wannan, sai ya ce masu, “Wannan ya zamar maku laifi?
62 Et si vous voyiez le Fils de l’homme montant où il était auparavant?
Yaya Ke nan in kun ga Dan Mutum yana hawa inda yake a da?
63 C’est l’esprit qui vivifie; la chair ne sert de rien: or les paroles que je vous ai dites sont esprit de vie.
Ruhu shine mai bayar da rai; Jiki ba ya amfana komai. Kalmomin da na fada maku ruhu ne, da kuma rai.
64 Mais il en est parmi vous quelques-uns qui ne croient point. Car Jésus savait, dès le commencement, qui étaient ceux qui ne croyaient pas, et qui devait le trahir.
Amma fa akwai wadansun ku da ba su ba da gaskiya ba. Domin tun farko Yesu ya san wadanda ba su ba da gaskiya ba, da kuma wanda zai bashe shi.
65 Et il disait: C’est pourquoi je vous ai dit que nul ne peut venir à moi, s’il ne lui est donné par mon Père.
Ya fada cewa, “shiyasa na gaya maku, ba mai iya zuwa wurina, sai ta wurin Uban.”
66 Dès lors, beaucoup de ses disciples se retirèrent, et ils n’allaient plus avec lui.
Bayan haka, da yawa daga cikin almajiransa suka koma da baya, ba su kara tafiya tare da shi ba.
67 Jésus donc dit aux douze: Et vous, voulez-vous aussi vous en aller?
Sai Yesu ya ce wa goma sha biyun, “ku ba kwa so ku tafi, ko ba haka ba?
68 Mais Simon-Pierre lui répondit: Seigneur, à qui irions-nous? Vous avez des paroles de vie éternelle; (aiōnios g166)
Bitrus ya amsa masa ya ce, “Ya Ubangiji, gun wa za mu je? kai kake da maganar rai madawwami. (aiōnios g166)
69 Pour nous, nous avons cru, et nous avons connu que vous êtes le Christ, le Fils de Dieu.
Mu kwa mun gaskata mun kuma sani kai ne mai tsarkin nan na Allah.”
70 Jésus leur répondit: N’est-ce pas moi qui vous ai choisis tous les douze? Cependant l’un de vous est un démon.
Yesu ya ce masu, “Ba ni na zabe ku, goma sha biyu ba, amma dayanku Iblis ne?”
71 Il parlait de Judas Iscariote, fils de Simon: car c’était lui qui devait le trahir, quoiqu’il fût un des douze.
Wato yana magana akan Yahuda dan Siman Iskariyoti, shi kuwa daya daga cikin sha-biyun ne, wanda zai ba da Yesu.

< Jean 6 >