< Jean 17 >

1 Jésus parla ainsi; puis, levant les yeux au ciel, il dit: Mon Père, elle est venue l’heure; glorifiez votre Fils, afin que votre Fils vous glorifie;
Da Yesu ya fadi wandannan abubuwa, sai ya tada idanunsa sama ya ce, ya Uba, sa'a ta zo; ka daukaka Danka, domin Dan shi ya daukaka ka,
2 Puisque vous lui avez donné puissance sur toute chair, afin que, quant à tous ceux que vous lui avez donnés, il leur donne la vie éternelle. (aiōnios g166)
kamar yadda ka ba shi iko akan dukkan 'yan adam, ya ba da rai madawwami ga duk wanda ka ba shi. (aiōnios g166)
3 Or la vie éternelle, c’est qu’ils vous connaissent, vous seul vrai Dieu, et celui que vous avez envoyé, Jésus-Christ. (aiōnios g166)
Wannan ne rai madawwami: wato su san ka, Allah makadaici na gaskiya, da shi kuma wanda ka aiko, Yesu Almasihu. (aiōnios g166)
4 Moi, je vous ai glorifié sur la terre; j’ai consommé l’œuvre que vous m’avez donnée à faire;
Na daukaka ka a duniya, na gama aikin da ka ba ni in yi.
5 Et maintenant vous, mon Père, glorifiez-moi en vous-même de la gloire que j’ai eue en vous avant que le monde fût.
Yanzu, ya Uba, ka daukaka ni tare da kai da daukaka wadda ni ke da ita tare da kai tun kafin duniya ta kasanci.
6 J’ai manifesté votre nom aux hommes que vous m’avez donnés; ils étaient à vous, vous me les avez donnés, et ils ont gardé votre parole.
Na bayyana sunanka ga mutunen da ka ba ni acikin duniya. Na ka suke, ka ba ni su, sun kuwa kiyaye maganarka.
7 Maintenant ils ont connu que tout ce que vous m’avez donné vient de vous;
Yanzu kuwa sun san duk iyakar abinda ka ba ni daga gare ka yake,
8 Parce que je leur ai donné les paroles que vous m’avez données; et ils les ont reçues, et ils ont connu véritablement que c’est de vous que je suis sorti, et ils ont cru que c’est vous qui m’avez envoyé.
don kuwa maganganun da ka fada mani. Na fada masu, sun kuma karba, sun sani kuwa hakika na fito daga gareka ne, kuma sun gaskata kai ne ka aiko ni.
9 Moi, je prie pour eux; je ne prie point pour le monde, mais pour ceux que vous m’avez donnés, parce qu’ils sont à vous;
Ina yi masu addu'a. Ba domin duniya ni ke yin addu'a ba, amma domin wadanda ka bani gama na ka ne.
10 Car tout ce qui est à moi est à vous, et tout ce qui est à vous est à moi; et j’ai été glorifié en eux.
Gama dukan abinda ke nawa na ka ne, naka kuwa nawa ne, an kuma daukaka ni a cikinsu.
11 Et déjà je ne suis plus dans le monde, et eux sont dans le monde, et moi je viens à vous. Père saint, conservez en votre nom ceux que vous m’avez donnés, afin qu’ils soient une seule chose, comme nous.
Ba na cikin duniya kuma, amma wadannan mutane suna cikin duniya, ni kuwa ina zuwa wurin ka. Ya Uba mai Tsarki, ka adanasu cikin sunanka da ka ba ni domin su zama daya, kamar dai yadda muke daya.
12 Quand j’étais avec eux, je les conservais en votre nom. Ceux que vous m’avez donnés, je les ai gardés, et pas un d’eux n’a péri, hors le fils de la perdition, afin que l’Ecriture fût accomplie.
Lokacin da ina tare da su, na adanasu acikin sunanka da ka ba ni. Na kiyaye su, kuma ko daya kuwa daga cikinsu ba ya bace ba, sai dai dan hallakar nan, domin Nassi ya cika.
13 Mais maintenant je viens à vous; et je dis ces choses dans le monde, pour qu’ils aient en eux ma joie complète.
Amma yanzu ina zuwa wurinka, Ina fadar wadannan abubuwa tun ina duniya, domin farin cikina ya zama cikakke a zukatansu.
14 Moi, je leur ai donné votre parole, et le monde les a eus en haine, parce qu’ils ne sont point du monde, comme moi-même je ne suis pas du monde.
Na ba su maganarka, kuma duniya ta tsane su domin su ba na duniya ba ne, kamar yadda ni ba na duniya ba ne.
15 Je ne demande point que vous les ôtiez du monde, mais que vous les gardiez du mal.
Ba ina roko ka dauke su daga cikin duniya ba, amma domin ka tsare su daga mugun nan.
16 Ils ne sont point du monde, comme moi-même je ne suis pas du monde.
Su ba na duniya ba ne, kamar yadda ni ba na duniya ba ne.
17 Sanctifiez-les dans la vérité. Votre parole est vérité.
Ka kebe su domin kanka cikin gaskiya. maganarka gaskiya ce.
18 Comme vous m’avez envoyé dans le monde, moi aussi, je les ai envoyés dans le monde.
Kamar dai yadda ka aiko ni cikin duniya, haka kuma na aike su cikin duniya.
19 Et pour eux je me sanctifie moi-même, afin qu’eux aussi soient sanctifiés en vérité.
Na kebe kaina gareka sabili da su, domin su ma kansu a kebe su gareka cikin gaskiya.
20 Je ne prie pas pour eux seulement, mais encore pour ceux qui, par leur parole, croiront en moi;
Ina addu'a ba domin wadannan kadai ba, amma har da wadanda zasu gaskata da ni ta wurin maganarsu,
21 Afin qu’ils soient tous une seule chose, comme vous, mon Père, êtes en moi, et moi en vous; qu’ils soient de même une seule chose en nous, et qu’ainsi le monde croie que c’est vous qui m’avez envoyé.
Domin su zama daya dukansu, kamar yadda kai, ya Uba, ka ke ciki na, ni kuma na ke cikin ka. Ina roko suma su kasance a cikinmu, domin duniya ta gaskata cewa ka aiko ni
22 Pour moi, je leur ai donné la gloire que vous m’avez donnée, afin qu’ils soient une seule chose, comme nous sommes une seule chose.
Daukakar da ka bani, ita nake basu, domin su zama daya, kamar yadda mu ke daya;
23 Je suis en eux et vous en moi, afin qu’ils soient consommés dans l’unité, et que le monde connaisse que c’est vous qui m’avez envoyé, et que vous les avez aimés comme vous m’avez aimé.
ni a cikinsu, kai kuma a ciki na. Domin su kammalu cikin zama daya, domin duniya ta sani cewa ka aiko ni, kuma ka kaunace su, kamar yadda ka kaunace ni.
24 Mon Père, je veux que là où je suis, ceux que vous m’avez donnés soient aussi avec moi; afin qu’ils voient la gloire que vous m’avez donnée; parce que vous m’avez aimé avant la fondation du monde.
Ya Uba, ina so wadanda ka ba ni, su ma su kasance tare da ni inda nake, domin su dubi daukakata da ka yi mani. Domin ka kaunace ni tun kafin halittar duniya.
25 Père juste, le monde ne vous a point connu; mais moi je vous ai connu, et ceux-ci ont connu que c’est vous qui m’avez envoyé.
Ya Uba mai adalci, duniya kam, ba ta sanka ba, amma ni na sanka; kuma wadannan sun sani kai ne ka aiko ni.
26 Je leur ai fait connaître votre nom, et je le leur ferai connaître encore, afin que l’amour dont vous m’avez aimé soit en eux, et moi en eux.
Na sanar masu da sunanka, zan kuma sanar da shi domin kaunar da ka yi mani ta kasance a cikinsu, ni kuma in kasance a cikinsu,

< Jean 17 >