< Jean 15 >

1 Moi je suis la vraie vigne, et mon Père est le vigneron.
“Nine itacen inabi na hakika, Ubana kuwa shi ne manomin.
2 Tous les sarments qui ne portent pas de fruit en moi, il les retranchera; et tous ceux qui portent du fruit, il les émondera, pour qu’ils portent plus de fruit encore.
Yakan cire duk wani rashe a cikina da ba ya bada 'ya'ya, mai bada 'ya'ya kuwa ya kan gyara shi domin ya kara bada 'ya'ya.
3 Vous êtes déjà purs, vous, à cause des paroles que je vous ai dites.
Kun rigaya kun tsarkaka saboda maganar da na yi muku.
4 Demeurez en moi, et moi en vous. Comme le sarment ne peut porter de fruit par lui-même, s’il ne demeure uni à la vigne; ainsi vous non plus, si vous ne demeurez en moi.
Ku zauna ciki na, Ni kuma cikin ku. Kamar yadda reshe ba ya iya bada 'ya'ya shi kadai sai ya zauna cikin itacen, haka kuma ba za ku iya ba, sai kun zauna ciki na.
5 Moi je suis la vigne, et vous les sarments. Celui qui demeure en moi et moi en lui portera beaucoup de fruit; parce que sans moi vous ne pouvez rien faire.
Ni ne itacen inabi, ku ne rassan. Wanda ya zauna ciki na, ni kuma cikin sa, yana bada 'ya'ya dayawa, gama in ba tare da ni ba, ba za ku iya yin kome ba.
6 Si quelqu’un ne demeure pas en moi, il sera jeté dehors comme le sarment, et il séchera; et on le ramassera, et on le jettera au feu, et il brûlera.
Wanda kuma bai zauna a ciki na ba, akan jefar da shi kamar reshe, ya bushe, kuma sukan tattara rassan su jefa a wuta, su kone.
7 Si vous demeurez en moi, et que mes paroles demeurent en vous, vous demanderez tout ce que vous voudrez, et il vous sera fait.
In kun zauna a ciki na, maganata kuma ta zauna a cikin ku, sai ku roki duk abinda kuke so, za a kuwa yi maku.
8 C’est la gloire de mon Père que vous portiez beaucoup de fruit, et que vous deveniez mes disciples.
Ta haka ake daukaka Ubana: cewa ku bada 'ya'ya dayawa, kuma cewa ku almajiraina ne.
9 Comme mon Père m’a aimé, moi je vous ai aimés. Demeurez dans mon amour.
Kamar yadda Ubana ya kaunace ni, haka Ni ma na kaunace ku; Ku zauna cikin kaunata.
10 Si vous gardez mes commandements, vous demeurerez dans mon amour; comme moi-même j’ai gardé les commandements de mon Père, et je demeure dans son amour.
Idan kun kiyaye dokokina, za ku zauna cikin kaunata kamar yadda Na kiyaye dokokin Ubana, na kuma zauna cikin kaunarsa.
11 Je vous ai dit ces choses, afin que ma joie soit en vous, et que votre joie soit complète.
Ina gaya maku wadannan al'amura domin farincikina ya kasance a cikin ku, kuma domin farincikinku ya zama cikakke.
12 Voici mon commandement, c’est que vous vous aimiez les uns les autres comme je vous ai aimés.
“Wannan shine umarnina, cewa ku kaunaci juna kamar yadda na kaunace ku.
13 Personne n’a un plus grand amour que celui qui donne sa vie pour ses amis.
Babu wanda ke da kaunar da tafi haka, wato ya bada ransa domin abokansa.
14 Vous êtes mes amis, si vous faites ce que je vous commande.
Ku abokaina ne idan kuna yin abubuwan da na umarce ku.
15 Je ne vous appellerai plus serviteurs, parce que le serviteur ne sait pas ce que fait son maître. Mais je vous ai appelés mes amis, parce que tout ce que j’ai entendu de mon Père, je vous l’ai fait connaître.
Nan gaba ba zan kara ce da ku bayi ba, don bawa bai san abinda Ubangijinsa ke yi ba. Na kira ku abokaina, domin na sanar da ku duk abinda na ji daga wurin Ubana.
16 Ce n’est pas vous qui m’avez choisi, mais c’est moi qui vous ai choisis et vous ai établis, pour que vous alliez, et rapportiez du fruit, et que votre fruit demeure, afin que tout ce que vous demanderez à mon Père en mon nom il vous le donne.
Ba ku kuka zabe ni ba, amma Ni ne na zabe ku, na aike ku don ku je ku bada 'ya'ya, 'ya'yanku kuma su tabbata. Wannan ya zama domin duk abinda kuka roki Uba a cikin sunana, zai baku.
17 Ce que je vous commande, c’est que vous vous aimiez les uns les autres.
Na baku wannan umarni: domin ku kaunaci juna.
18 Si le monde vous hait, sachez qu’il m’a eu en haine avant vous.
In duniya ta ki ku, ku sani cewa ta kini kafin ta ki ku.
19 Si vous aviez été du monde, le monde aimerait ce qui est à lui; mais parce que vous n’êtes point du monde, et que je vous ai choisis du milieu du monde, c’est pour cela que le monde vous hait.
Da ku na duniya ne, da duniya ta kaunace ku kamar nata. Amma saboda ku ba na duniya bane, na kuma zabe ku daga duniya, don haka duniya take kin ku.
20 Souvenez-vous de la parole que je vous ai dite: Le serviteur n’est pas plus grand que son maître. S’ils m’ont persécuté, ils vous persécuteront aussi; s’ils ont gardé ma parole, ils garderont aussi la vôtre.
Ku tuna da maganar da na yi muku, 'Bawa ba ya fi Ubangijinsa girma ba.' Idan sun tsananta mani, ku ma za su tsananta maku; Idan sun kiyaye maganata, za su kuma kiyaye maganarku.
21 Mais ils vous feront toutes ces choses à cause de mon nom; parce qu’ils ne connaissent point celui qui m’a envoyé.
Za su yi maku duk wadannan abubuwa saboda sunana, don basu san wanda ya aiko ni ba.
22 Si je n’étais pas venu, et que je ne leur eusse point parlé, ils n’auraient point de péché; mais maintenant ils n’ont point d’excuse de leur péché.
Da ban zo na yi masu magana ba, da basu da zunubi, amma yanzu, basu da wata hujja don zunubinsu.
23 Qui me hait, hait aussi mon Père.
Duk wanda ya ki ni ya ki Ubana.
24 Si je n’avais fait parmi eux les œuvres que nul autre n’a faites, ils n’auraient point de péchés; mais maintenant, et ils les ont vues, et ils ont haï et moi et mon Père.
Da ban yi ayyukan da babu wanda ya taba yinsu a cikin su ba, da basu da zunubi, amma yanzu sun gani, sun kuma ki ni da Ubana duka.
25 Mais c’est afin que s’accomplisse la parole qui est écrite dans leur loi: Ils m’ont haï gratuitement.
An yi wannan kuwa domin a cika maganar da ke rubuce a cikin shari'arsu, ' Sun ki ni ba dalili.'
26 Mais lorsque sera venu le Paraclet que je vous enverrai du Père, l’Esprit de vérité qui procède du Père, il rendra témoignage de moi;
Sa'adda Mai Ta'aziya- wanda zan aiko maku daga wurin Uban, wato, Ruhun gaskiya, wanda ke fita daga wurin Uban-ya zo, zai bada shaida a kai na.
27 Et vous aussi, vous rendrez témoignage, parce que, dès le commencement, vous êtes avec moi.
Ku ma kuna bada shaida saboda kuna tare da ni tun daga farko.

< Jean 15 >