< Job 7 >
1 C’est une milice que la vie de l’homme sur la terre; et ses jours sont comme les jours d’un mercenaire.
“Mutum bai sha wahalar aiki ba a duniya? Rayuwarsa ba kamar ta wanda aka yi hayarsa ba ne?
2 Comme un esclave désire l’ombre, et comme un mercenaire attend la fin de son ouvrage,
Kamar yadda bawa yakan jira yamma ta yi, ko kuma kamar yadda wanda aka yi hayarsa yakan jira a biya shi kuɗin aikin da ya yi.
3 Ainsi moi aussi j’ai eu des mois vides, et j’ai compté des nuits laborieuses.
Saboda haka rabona shi ne watanni na zama banza, kowane dare kuwa sai ɓacin rai nake samu.
4 Si je m’endors, je dis: Quand me lèverai-je? et de nouveau j’attends le soir, et je suis rempli de douleur jusqu’aux ténèbres.
Lokacin da na kwanta ina tunani, ‘Har sai yaushe zan tashi?’ Gari ya ƙi wayewa, ina ta jujjuyawa har safe.
5 Ma chair est revêtue de pourriture et d’une sale poussière; ma peau s’est desséchée et contractée.
Jikina duk tsutsotsi da ƙuraje sun rufe shi, fatar jikina ta ruɓe tana fitar da ruwan miki.
6 Mes jours ont passé plus promptement que la trame n’est coupée par un tisserand; et ils ont été consumés sans aucune espérance.
“Kwanakina suna wucewa da sauri, fiye da yadda ƙoshiyar masaƙa take wucewa da sauri, za su kawo ga ƙarshe ba bege.
7 Souvenez-vous que ma vie est un souffle, et que mon œil ne reviendra pas pour voir le bonheur.
Ka tuna, ya Allah, raina numfashi ne kawai; idanuna ba za su taɓa sāke ganin farin ciki ba.
8 Le regard de l’homme ne m’apercevra pas; vos yeux se porteront sur moi, mais je ne serai plus.
Idanun da suke ganina yanzu ba za su sāke ganina ba; za ku neme ni amma ba za ku same ni ba.
9 Comme un nuage se dissipe et passe, ainsi celui qui descend dans les enfers ne montera pas. (Sheol )
Kamar yadda girgije yakan ɓace yă tafi, haka mutum yake shige zuwa kabari ba kuwa zai dawo ba. (Sheol )
10 Il ne reviendra plus dans sa maison, et son lieu ne le connaîtra plus.
Ba zai taɓa zuwa gidansa ba; ba za a sāke san da shi ba.
11 C’est pourquoi moi-même je ne retiendrai pas ma bouche; je parlerai dans la tribulation de mon esprit; je m’entretiendrai avec l’amertume de mon âme.
“Saboda haka ba zan yi shiru ba; zan yi magana cikin ɓacin raina, zan nuna ɓacin raina cikin ruhu, cikin ƙuncin raina.
12 Est-ce que je suis une mer, ou un monstre marin, pour que vous m’ayez enfermé dans une prison?
Ni teku ne, ko kuwa dodon ruwa, don me kake tsaro na?
13 Si je dis: Mon lit me consolera, et je serai soulagé en me parlant sur ma couche,
Lokacin da nake zato zan sami salama in na kwanta a gadona don in huta,
14 Vous m’épouvanterez par des songes, et par des visions vous m’agiterez d’horreur.
duk da haka kana ba ni tsoro da mafarke-mafarke, kana tsorata ni da wahayi.
15 C’est pour ce motif que mon âme a choisi une destruction violente, et mes os, la mort.
Na gwammace a shaƙe ni in mutu maimakon in kasance cikin wannan jiki.
16 J’ai perdu toute espérance; je ne saurais vivre davantage: épargnez-moi; car mes jours ne sont rien.
Ba na so in zauna da rai; ba zan rayu ba har abada. Ku rabu da ni; rayuwata ba ta da amfani.
17 Qu’est-ce qu’un homme, pour que vous fassiez un si grand cas de lui? ou pourquoi mettez-vous sur lui votre cœur?
“Mene ne mutum har da ka kula da shi haka, har ka mai da hankali a kansa,
18 Vous le visitez au point du jour, et aussitôt vous l’éprouvez,
har kake duba shi kowace safiya, kake kuma gwada shi koyaushe?
19 Jusques à quand ne m’épargnerez-vous point, et ne me laisserez-vous pas avaler ma salive?
Ba za ka ɗan daina kallo na ba ko ka rabu da ni na ɗan lokaci?
20 J’ai péché, que ferai-je pour vous, ô gardien des hommes? Pourquoi m’avez-vous mis en opposition avec vous, et suis-je à charge à moi-même?
In na yi zunubi, me na yi maka, kai mai lura da mutane? Don me ka sa ni a gaba? Na zame maka kaya mai nauyi ne?
21 Pourquoi n’ôtez-vous point mon péché, et pourquoi n’enlevez-vous pas mon iniquité? Voilà que maintenant je dormirai dans la poussière, et, si vous me cherchez dès le matin, je ne serai plus.
Me ya sa ba za ka gafarta mini laifofina ba? Gama na kusa kwantawa cikin ƙasa; za ka neme ni, amma ba za ka same ni ba.”