< Job 40 >
1 Et le Seigneur continua à parler à Job:
Ubangiji ya ce wa Ayuba,
2 Est-ce que celui qui dispute avec Dieu se réduit si facilement au silence? Certainement celui qui reprend Dieu doit lui répondre.
“Mai neman sa wa wani laifi zai iya ja da Maɗaukaki? Bari mai tuhumar Allah yă amsa masa.”
3 Répondant alors au Seigneur, Job dit:
Sai Ayuba ya amsa wa Ubangiji,
4 Moi qui a parlé légèrement, que peux-je répondre? Je mettrai ma main sur ma bouche.
“Ai, ni ba a bakin kome nake ba ne, ta yaya zan iya amsa maka? Na rufe bakina da hannuna.
5 J’ai dit une chose (plut à Dieu que je ne l’eusse pas dite!) et une autre; je n’y ajouterai rien de plus.
Na yi magana sau ɗaya amma ba ni da amsa, sau biyu, amma ba zan ƙara cewa kome ba.”
6 Or, répondant à Job du milieu d’un tourbillon, le Seigneur dit:
Sa’an nan Ubangiji ya yi wa Ayuba magana ta cikin guguwa,
7 Ceins tes reins comme un homme de cœur; je t’interrogerai, et réponds-moi.
“Ka tashi tsaye ka tsaya da ƙarfi kamar namiji; zan yi maka tambaya kuma za ka amsa mini.
8 Est-ce que tu rendras vain mon jugement; et me condamneras-tu, pour que toi, tu sois justifié?
“Ko za ka ƙi yarda da shari’ata? Za ka ba ni laifi don ka nuna kai marar laifi ne?
9 Et as-tu un bras comme Dieu, et tonnes-tu d’une voix semblable?
Ko hannunka irin na Allah ne, kuma ko muryarka za tă iya tsawa kamar ta Allah?
10 Environne-toi de majesté, et élève-toi dans les airs, et sois glorieux, et revêts-toi de splendides vêtements.
Sai ka yi wa kanka ado da ɗaukaka da girma, ka yafa daraja da muƙami.
11 Dissipe les superbes dans ta fureur, et d’un regard humilie tout arrogant.
Ka saki fushinka, ka dubi dukan wani mai girman kai ka wulaƙanta shi.
12 Regarde tous les superbes et confonds-les; et brise les impies en leur lieu.
Ka dubi duk wani mai girman kai ka ƙasƙantar da shi, ka tattake mugaye a inda ka tsaya.
13 Cache-les dans la poussière tous ensemble, et plonge leurs faces dans la fosse.
Ka bizne su duka tare ka rufe fuskokinsu a cikin kabari.
14 Et moi, je confesserai que ta droite peut te sauver.
Sa’an nan ni kaina zan shaida maka cewa hannun damanka zai iya cetonka.
15 Vois, Béhémoth que j’ai fait avec toi mangera du foin comme le bœuf.
“Dubi dorina, wadda na halicce ku tare kuma ciyawa take ci kamar sa.
16 Sa force est dans ses reins, et sa vertu dans le nombril de son ventre.
Ga shi ƙarfinta yana a ƙugunta ikonta yana cikin tsokar cikinta.
17 Il serre sa queue qui est semblable à un cèdre; les nerfs de ses cuisses sont entrelacés.
Wutsiyarta tana da ƙarfi kamar itacen al’ul; jijiyoyin cinyoyinta suna haɗe a wuri ɗaya.
18 Ses os sont des tuyaux d’airain, ses cartilages comme des lames de fer.
Ƙasusuwanta bututun tagulla ne, haƙarƙarinta kamar sandunan ƙarfe.
19 C’est lui qui est le commencement des voies de Dieu; celui qui l’a fait appliquera son glaive.
Tana ta farko cikin ayyukan Allah, Mahaliccinta kaɗai yake iya tunkarar ta da takobi.
20 C’est pour lui que les montagnes portent des herbes; toutes les bêtes de la campagne viendront se jouer là.
Tuddai su suke tanada mata abinci a inda duk namun jeji suke wasa.
21 Il dort sous l’ombre, dans le secret des roseaux et dans des lieux humides.
Tana kwanciya a ƙarƙashin inuwar itacen lotus ta ɓuya cikin kyauro da fadama.
22 Des ombres couvrent son ombre, et les saules du torrent l’environneront.
Inuwa ta rufe ta da ƙaddaji, itatuwan wardi na rafi, sun kewaye ta.
23 Voici qu’il absorbera un fleuve, et il ne s’en étonnera point; il a même la confiance que le Jourdain viendra couler dans sa bouche.
Sa’ad da kogi ya cika yana hauka, ba tă damu ba; ba abin da zai same ta ko da a gaban bakinta Urdun yake wucewa.
24 On le prendra par les yeux comme à l’hameçon, et, avec des harpons, on percera ses narines.
Ko akwai wanda zai iya kama ta ba ta kallo, ko kuma a kama ta da tarko a huda hancinta?