< Job 34 >

1 C’est pourquoi continuant son discours, Eliu dit encore ceci:
Sa’an nan Elihu ya ce,
2 Sages, écoutez mes paroles, et vous, savants, prêtez-moi attention;
“Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
3 Car l’oreille discerne les paroles comme le palais juge des mets par le goût.
Gama kunne yana rarrabe magana kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci.
4 Formons-nous un jugement, et voyons entre nous ce qu’il y a de mieux.
Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
5 Job a dit: Je suis juste, et Dieu détruit mon bon droit.
“Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
6 Car dans le jugement porté contre moi, il y a fausseté: une flèche ardente m’a percé sans qu’il y ait en moi aucun péché.
Ko da yake ina da gaskiya, an ɗauke ni maƙaryaci; ko da yake ba ni da laifi, kibiyoyinsa sun ji mini ciwo wanda ba ya warkewa.’
7 Quel est l’homme comme est Job, qui boit la dérision comme l’eau;
Wane mutum ne kamar Ayuba, wanda yake shan ba’a kamar ruwa?
8 Qui marche avec ceux qui opèrent l’iniquité, et chemine avec les hommes impies?
Yana abokantaka da masu aikata mugunta; yana cuɗanya da mugaye.
9 Car il a dit: L’homme ne plaira pas à Dieu, quand même il aurait couru avec lui.
Gama ya ce, ‘Ba ribar da mutum zai samu lokacin da yake ƙoƙari yă faranta wa Allah zuciya.’
10 C’est pourquoi, hommes sensés, écoutez-moi: Loin de Dieu l’impiété, et loin du Tout-Puissant l’iniquité!
“Saboda haka ku saurare ni, ku masu ganewa. Ko kaɗan Allah ba ya mugunta, Maɗaukaki ba ya kuskure.
11 Car il rendra à l’homme selon ses œuvres, et il traitera chacun selon ses voies.
Yana biyan mutum bisa ga abin da ya yi; yana kawo masa abin da ayyukansa suka jawo.
12 Certainement Dieu ne condamnera pas sans sujet, et le Tout-Puissant ne détruira pas le bon droit.
Ba zai yiwu Allah yă yi ba daidai ba, Maɗaukaki ba zai yi shari’a marar gaskiya ba.
13 Quel autre que lui a-t-il constitué sur la terre? ou qui a-t-il établi sur l’univers, qu’il a formé?
Wane ne ya ba shi iko yă lura da duniya? Wane ne ya ba shi iko kan dukan duniya?
14 S’il dirigeait vers lui son cœur, il attirerait à soi son esprit et son souffle.
In nufinsa ne ya kuma janye ruhunsa da numfashinsa,
15 Toute chair périrait en même temps, et l’homme retournerait en cendre.
’yan adam duka za su hallaka tare, mutum kuma zai koma ƙasa.
16 Si donc tu as l’intelligence, écoute ce que l’on dit, et sois attentif à mes paroles.
“In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
17 Est-ce que celui qui n’aime pas la justice, peut être guéri? et comment toi condamnes-tu si hautement celui qui est juste?
Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
18 Celui qui dit à un roi: Apostat; qui appelle les grands impies;
Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
19 Qui ne fait point acception de la personne des princes, qui n’a pas connu un tyran, lorsqu’il disputait contre un pauvre, parce que tous les hommes sont l’ouvrage de ses mains.
wanda ba ya nuna sonkai ga’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
20 Ils mourront tout à coup, et au milieu de la nuit les peuples se troubleront, ils passeront et le violent sera emporté sans la main de l’homme.
Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
21 Car les yeux de Dieu sont sur les voies des hommes, et il considère tous leurs pas.
“Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
22 Il n’y a pas de ténèbres, et il n’y a pas d’ombre de mort, où puissent se cacher ceux qui opèrent l’iniquité.
Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
23 Car il n’est plus au pouvoir de l’homme de venir devant Dieu en jugement.
Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
24 Il en brisera une multitude innombrable, et il en établira d’autres à leur place.
Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
25 Car il connaît leurs œuvres, et c’est pourquoi il fera venir la nuit, et ils seront brisés.
Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
26 Il les a frappés comme impies, dans un lieu où on les voyait.
Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
27 Eux qui, de propos délibéré, se sont retirés de lui, et n’ont pas voulu comprendre toutes ses voies;
domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
28 En sorte qu’ils ont fait parvenir jusqu’à lui le cri de l’indigent, et qu’il a entendu la voix des pauvres.
Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
29 Car, lui accordant la paix, qui est celui qui condamnera? et s’il cache son visage aux nations et à tous les hommes, qui est-ce qui pourra le contempler?
Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
30 C’est lui qui fait régner un homme hypocrite, à cause des péchés du peuple.
yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
31 Puis donc que j’ai parlé à Dieu, je ne t’empêcherai pas de parler aussi.
“A ce mutum ya ce wa Allah, ‘Na yi laifi, amma ba zan sāke saɓa wa wani ba.
32 Si j’ai erré, instruis-moi; si j’ai parlé iniquité, je n’ajouterai plus rien.
Ka koya mini abin da ba zan iya gani ba; in na yi ba daidai ba, ba zan sāke yi ba.’
33 N’est-ce pas à toi que Dieu demande compte de cette iniquité qui t’a déplu? car c’est toi qui as commencé à parler, et non pas moi; si tu sais quelque chose de meilleur, parle.
Ya kamata Allah yă yi maka bisa ga abin da ka ce ne, sa’ad da ka ƙi ka tuba? Dole kai ka zaɓa, ba ni ba; yanzu ka gaya mini abin da ka sani.
34 Que des hommes intelligents me parlent, et qu’un homme sage m’écoute.
“Mutane masu ganewa za su ce, masu hikima waɗanda suka ji ni za su ce mini,
35 Pour Job, il a parlé follement, et ses paroles n’annoncent pas la science.
‘Ayuba ya yi magana cikin rashin sani; maganganunsa na marar hikima ne.’
36 Mon père, que Job soit éprouvé jusqu’à la fin; ne cessez point de frapper un homme d’iniquité.
Kash, da za a gwada Ayuba har ƙarshe, domin yana ba da amsa kamar mugun mutum.
37 Parce qu’il ajoute à ses péchés le blasphème, qu’il soit, malgré cela, pressé par nos raisons; et qu’alors il appelle Dieu en jugement par ses discours.
Ya ƙara tawaye a kan zunubansa; ya tafa hannuwansa na reni a cikinmu ya kuma ƙara yawan maganganunsa ga Allah.”

< Job 34 >