< Job 33 >

1 Ecoute donc, Job, mes paroles, et sois attentif à tous mes discours.
“Amma yanzu, Ayuba, ka saurari abin da zan ce; ka sa hankali ga kowane abin da zan faɗa.
2 Voilà que j’ai ouvert ma bouche, que ma langue parle dans ma gorge.
Zan yi magana; kalmomina suna dab da fitowa daga bakina.
3 C’est d’un cœur simple que sortiront mes discours, et c’est un sentiment pur que mes lèvres exprimeront.
Abin da zan faɗa gaskiya ne daga cikin zuciyata; bakina zai faɗi gaskiyar abin da na sani.
4 L’Esprit de Dieu m’a fait, le souffle du Tout-Puissant m’a donné la vie.
Ruhun Allah ne ya yi ni; numfashin Maɗaukaki ya ba ni rai.
5 Si tu peux, réponds-moi, et tiens ferme en ma présence,
Ka amsa mini in za ka iya; ka yi shirin fuskanta ta.
6 Vois, Dieu m’a fait comme il t’a fait, et c est de la même boue que j’ai été formé.
Ni kamar ka nake a gaban Allah; ni ma daga ƙasa aka yi ni.
7 Cependant, que ce qu’il y a de merveilleux en moi ne t’épouvante point, et que mon éloquence ne soit pas accablante pour toi.
Kada ka ji tsorona, ba abin da zai fi ƙarfinka.
8 Tu as donc dit à mes oreilles, et j’ai entendu la voix de tes paroles:
“Amma ka faɗa na ji, na ji daidai abin da ka faɗa,
9 Je suis pur et sans péché; sans tache, et il n’y a point d’iniquité en moi.
‘ni mai tsarki ne marar zunubi; ina da tsabta kuma ba ni da laifi.
10 C’est parce que Dieu a trouvé des sujets de plaintes contre moi, qu’il a pensé que j’étais son ennemi.
Duk da haka Allah ya same ni da laifi; ya ɗauke ni maƙiyinsa,
11 Il a mis mes pieds dans les chaînes, et il a gardé toutes mes voies.
ya daure ƙafafuna da sarƙa; yana tsaron duk inda na bi.’
12 C’est donc en cela que tu n’as pas été justifié; car je te répondrai que Dieu est plus grand que l’homme.
“Amma na gaya maka, a nan ba ka yi daidai ba, gama Allah ya fi mutum girma.
13 Disputes-tu contre lui, parce qu’il ne t’a pas répondu sur toutes tes paroles?
Don me ka yi masa gunaguni cewa ba ya amsa tambayoyin mutum?
14 Dieu ne parle qu’une fois, et il ne répète pas ce qu’il a dit.
Gama Allah yana magana, yanzu ga wannan hanya, yanzu kuma ga wata hanya ko da yake ba lalle mutum yă lura ba.
15 Pendant un songe, dans une vision nocturne, quand un profond sommeil s’empare des hommes et qu’ils dorment dans leur lit:
A cikin mafarki, cikin wahayi da dare, sa’ad da barci mai zurfi ya fāɗo a kan mutane lokacin da suke cikin barci kan gadajensu,
16 C’est alors qu’il ouvre les oreilles des hommes, et que, les instruisant, il leur enseigne la science,
mai yiwuwa yă yi musu magana a cikin kunnuwansu yă razana su da gargaɗinsa,
17 Pour détourner ainsi un homme des choses qu’il fait, et le délivrer de l’orgueil;
don a juyar da su daga abin da yake yi da ba daidai ba a kuma hana su daga girman kai,
18 Retirant son âme de la corruption, et empêchant que sa vie ne tombe sous le glaive.
don a kāre su daga fāɗuwa cikin rami, a kāre su daga hallaka ta wurin takobi.
19 Il le châtie encore par la douleur dans son lit, et il fait sécher tous ses os.
“Ko kuma mutum yă sha horo ta wurin kwanciya da ciwo da rashin jin daɗi cikin ƙasusuwansa,
20 Durant sa vie, le pain lui devient un objet d’aversion, ainsi que le devient pour son âme une nourriture auparavant très recherchée.
yadda zai ji ƙyamar abinci, har yă ƙi son abinci mafi daɗi.
21 Toute sa chair se consumera, et ses os, qui étaient couverts, seront mis à nu.
Naman jikinsa ya lalace ba wani abu mai kyau a ciki kuma ƙasusuwansa da suke a rufe da tsoka yanzu duk sun fito.
22 Son âme a été proche de la corruption, et sa vie de tout ce qui pouvait lui donner la mort.
Ransa yana matsawa kusa da rami, ransa kuma kusa da’yan aikan mutuwa.
23 Si un ange, un d’entre mille, parle pour lui, et qu’il annonce l’équité de cet homme,
Duk da haka, in akwai mala’ika a gefensa kamar matsakanci, ɗaya daga cikin dubu, da zai gaya wa mutum abin da yake daidai gare shi,
24 Dieu aura compassion de lui, et il dira: Délivre-le, afin qu’il ne descende pas dans la corruption; j’ai trouvé ce en quoi je peux lui être propice.
yă yi masa alheri yă ce, ‘Kada ka bari yă fāɗa cikin rami, na samu fansa dominsa.’
25 Sa chair est consumée par les supplices; qu’il retourne aux jours de sa jeunesse.
Sa’an nan fatar jikinsa za tă zama sabuwa kamar ta jariri; za tă zama kamar lokacin da yake matashi.
26 Il priera Dieu, et Dieu se laissera apaiser en sa faveur; il verra sa face avec jubilation, et il rendra à cet homme sa justice.
Ya yi addu’a ga Allah ya kuwa samu alheri a wurinsa, yana ganin fuskar Allah yana kuma yin sowa don murna; Allah ya mayar da shi ya zama mai adalci.
27 Il regardera les hommes et il dira: J’ai péché, je me suis vraiment rendu coupable, et je n’ai pas reçu le châtiment dont j’étais digne.
Sa’an nan sai ya zo wurin, wurin mutane ya ce, ‘Na yi zunubi, na kauce wa abin da yake daidai, amma ban samu abin da ya kamata in samu ba.
28 Il a délivré son âme, afin qu’elle n’allât pas à la mort, mais que, vivant, elle vît la lumière.
Ya fanshi raina daga fāɗawa cikin rami, kuma zan rayu in ji daɗin hasken.’
29 Remarque bien, Dieu fait trois fois ces choses en chaque homme,
“Allah ya yi wa mutum duk waɗannan, sau biyu, har ma sau uku.
30 Afin de rappeler leurs âmes de la corruption, et de les illuminer de la lumière des vivants.
Ya juyo da ransa daga fāɗawa cikin rami, don hasken rai ya haskaka a kansa.
31 Prête attention, Job, écoute-moi; garde le silence, pendant que je parle.
“Ka sa hankali da kyau, Ayuba, ka saurare ni; ka yi shiru zan yi magana.
32 Mais si tu as quelque chose à dire, réponds-moi; car je veux que tu paraisses juste.
In kana da abin da za ka ce, ka amsa mini; yi magana, domin ina so in’yantar da kai.
33 Que si tu n’as rien, écoute-moi; garde le silence, et je t’enseignerai la sagesse.
Amma in ba haka ba, sai ka saurare ni; yi shiru, zan kuma koya maka hikima.”

< Job 33 >