< Job 30 >

1 Mais maintenant je suis tourné en ridicule par des hommes plus jeunes que moi, dont autrefois je n’aurais pas daigné mettre les pères avec les chiens de mon troupeau;
“Amma yanzu suna yi mini ba’a waɗanda na girme su, waɗanda iyayensu maza ba su isa su zama karnukan kiwon garken tumakina ba.
2 Dont je comptais pour rien la force de la main, et qui me paraissaient même indignes de la vie;
Ina amfani ƙarfin hannuwansu gare ni, tun da ba su da sauran kuzari?
3 Qui desséchés par la détresse et la faim, rongeaient dans un désert ce qu’ils pouvaient y trouver, défigurés par le malheur et la misère;
Duk sun rame don rashi da yunwa, suna yawo a gaigayar ƙasa a kufai da dare.
4 Qui mangeaient des herbes et des écorces d’arbres, et dont la racine des genévriers était la nourriture;
A cikin jeji suna tsinkar ganyaye marasa daɗi, jijiyoyin itacen kwakwa ne abincinsu.
5 Qui allaient les enlever dans les vallées, et qui, en ayant trouvé quelqu’une, y accouraient en criant;
An kore su daga cikin mutanensu, aka yi musu ihu kamar ɓarayi.
6 Qui habitaient dans des déserts auprès des torrents, dans les cavernes de la terre, ou sur le gravier;
An sa dole su zauna a kwazazzabai da kuma cikin kogunan duwatsu da kuma cikin ramummuka cikin ƙasa.
7 Qui au milieu de choses semblables se livraient à la joie, et mettaient leurs délices à être sous des ronces.
Suka yi ta kuka kamar dabbobi a jeji, suka taru a ƙarƙashin sarƙaƙƙiya.
8 Fils de pères insensés et vils, et qui ne paraissent nullement sur la terre.
Mutane marasa hankali marasa suna, an kore su daga ƙasar.
9 Maintenant je suis devenu le sujet de leurs chansons, et je suis passé parmi eux en proverbe.
“Yanzu kuma’ya’yansu maza su suke yi mini ba’a cikin waƙa na zama abin banza a gare su.
10 Ils m’ont en horreur, et ils fuient loin de moi, et ils n’ont pas honte de cracher sur ma face.
Suna ƙyamata suna guduna; suna tofa mini miyau a fuska.
11 Car Dieu a ouvert son carquois, et il m’a abattu, et il a mis un frein à ma bouche.
Yanzu da Allah ya kunce bakana ya ba ni wahala sun raba ni da mutuncina.
12 À ma droite, quand j’ai commencé à paraître, mes maux se sont soudain élevés; ils ont renversé mes pieds, et m’ont foulé dans leurs sentiers comme sous des flots.
A hannun damana’yan tā-da-na-zaune-tsaye sun tayar; sun sa tarko a ƙafafuna, sun yi shirin hallaka ni.
13 Ils ont détruit mes chemins, ils m’ont dressé des pièges et ils ont prévalu, et il n’y a eu personne qui me portât secours.
Sun ɓata mini hanyata; sun yi nasara cikin hallaka ni, ba tare da wani ya taimake su ba.
14 Comme par la brèche d’un mur et par une porte ouverte ils ont fondu sur moi, et ils ont accouru pour m’accabler dans ma misère.
Suka nufo ni daga kowane gefe; suka auko mini da dukan ƙarfinsu.
15 J’ai été réduit au néant; comme le vent, vous avez emporté l’objet de mes désirs, et comme un nuage, a passé mon bonheur.
Tsoro ya rufe ni; an kawar mini mutuncina kamar da iska, dukiyata ta watse kamar girgije.
16 Aussi maintenant mon âme se flétrit en moi-même, et des jours d’affliction ont pris possession de moi.
“Yanzu raina yana ƙarewa; kwanakin wahala sun kama ni.
17 Pendant la nuit mes os sont transpercés de douleurs; et ceux qui me dévorent ne dorment pas.
Dare ya huda ƙasusuwana; ina ta shan azaba ba hutawa.
18 Leur multitude consume mon vêtement, et ils m’ont couvert comme d’un capuchon de tunique.
A cikin girman ikonsa Allah ya zama kamar riga a jikina; ya shaƙe ni kamar wuyan rigata.
19 Je suis devenu comme la boue, et je suis semblable à la braise et à la cendre.
Ya jefa ni cikin laka, na zama ba kome ba sai ƙura da toka.
20 Je crie vers vous, et vous ne m’exaucez pas; je me liens devant vous, et vous ne me regardez pas.
“Na yi kuka gare ka ya Allah, amma ba ka amsa mini ba. Na tashi tsaye, amma sai ka dube ni kawai.
21 Vous êtes changé et devenu cruel envers moi; et c’est avec la dureté de votre main que vous me combattez.
Ka dube ni ba tausayi; Ka kai mini hari da ƙarfin hannunka.
22 Vous m’avez élevé, et me posant comme sur le vent, vous m’avez brisé entièrement.
Ka ɗaga ni sama ka ɗora ni a kan iska; ka jujjuya ni cikin hadari.
23 Je sais que vous me livrerez à la mort, où est marquée la maison de tous les vivants.
Na san za ka sauko da ni ga mutuwa zuwa wurin da kowane mai rai zai je.
24 Cependant ce n’est pas pour leur ruine que vous étendez votre main; car s’ils tombent, vous les sauvez.
“Ba shakka ba mai ɗora hannu a kan mutumin da yake cikin wahala. Lokacin da ya yi kukan neman taimako a cikin wahalarsa.
25 Je pleurais autrefois sur celui qui était affligé, et mon âme était compatissante pour le pauvre.
Ashe ban yi kuka domin waɗanda suke cikin damuwa ba? Ko zuciyata ba tă yi baƙin ciki domin matalauta ba?
26 J’attendais des biens, et il m’est venu des maux; j’espérais la lumière, et des ténèbres se sont répandues autour de moi.
Duk da haka sa’ad da nake begen abu mai kyau, mugun abu ne ya zo; Sa’ad da nake neman haske, sai duhu ya zo.
27 Un feu ardent n’a cessé de brûler dans mes entrailles; des jours d’affliction m’ont prévenu.
Zuciyata ba tă daina ƙuna ba; ina fuskantar kwanakin wahala.
28 Je marchais triste, sans fureur; me levant, je poussais des cris au milieu de la foule.
Na yi baƙi ƙirin, amma ba rana ce ta ƙona ni ba. Na tsaya a cikin mutane, na kuma yi kuka don taimako.
29 J’ai été frère des dragons et compagnon des autruches.
Na zama ɗan’uwan diloli, na zama abokan mujiyoyi.
30 Ma peau est devenue noire sur moi, et mes os se sont desséchés dans une ardeur brûlante.
Fatar jikina ta yi baƙi tana ɓarewa; jikina yana ƙuna da zazzaɓi.
31 Ma harpe s’est changée en plainte lugubre, et mon orgue en voix de pleureurs.
Garayata ta zama ta makoki, sarewata kuma ta zama ta kuka.

< Job 30 >