< Job 3 >
1 Après cela Job ouvrit la bouche, et maudit le jour de sa naissance.
Bayan wannan Ayuba ya buɗe baki ya la’anta ranar da aka haife shi.
3 Périsse le jour auquel je suis né, et la nuit dans laquelle il fut dit: Un homme a été conçu!
“A hallaka ranar da aka haife ni, da kuma daren da aka ce, ‘An haifi jariri namiji!’
4 Que ce jour soit changé en ténèbres; que Dieu ne s’en enquière pas d’en haut, et qu’il ne soit point éclairé de la lumière.
Bari ranan nan ta zama duhu; kada Allah yă kula da ita; kada rana tă yi haske a wannan rana.
5 Que des ténèbres et une ombre de mort l’obscurcissent; qu’une obscurité s’en empare, et qu’il soit enveloppé d’amertume.
Bari duhu da inuwa mai duhu ta sāke rufe ta; gizagizai kuma su rufe ta; duhu kuma ya rufe haskenta.
6 Cette nuit, qu’un tourbillon ténébreux en prenne possession, qu’elle ne soit pas comptée dans les jours de l’année, ni mise au nombre des mois.
Bari duhu mai yawa yă rufe daren nan; kada a haɗa ta cikin kwanakin shekara, ko kuma cikin kwanakin watanni.
7 Que cette nuit soit solitaire, et qu’elle ne mérite pas de louanges.
Bari daren yă zama marar amfani; kada a ji wata sowa ta farin ciki.
8 Qu’ils la maudissent, ceux qui maudissent le jour, qui sont prêts à susciter Léviathan.
Bari waɗanda suke la’anta ranaku su la’anta wannan rana su waɗanda suke umartar dodon ruwa.
9 Que les étoiles soient couvertes des ténèbres de son obscurité; qu’elle attende une lumière, et ne la voie point, ni la naissance de l’aurore qui se lève;
Bari taurarinta na safe su zama duhu; bari ranar tă yi ta jiran ganin haske amma kada tă gani,
10 Parce qu’elle n’a pas fermé le sein qui ma formé, et qu’elle n’a pas ôté les maux de devant mes yeux.
gama ba tă hana uwata ɗaukar cikina, don ta hana ni shan wahalan nan ba.
11 Pourquoi ne suis-je pas mort dans le sein de ma mère? pourquoi, sorti de son sein, n’ai-je pas aussitôt péri?
“Me ya sa ban mutu ba da za a haife ni, ko kuma in mutu sa’ad da ana haihuwata ba?
12 Pourquoi ai-je été reçu sur des genoux? pourquoi allaité par des mamelles?
Me ya sa aka haife ni, aka tanada nono na sha na rayu?
13 Car maintenant, dormant, je serais en silence, et je reposerais dans mon sommeil,
Da yanzu ina kwance cikin salama; da ina barcina cikin salama
14 Avec les rois et les consuls; de la terre, qui se bâtissent de vastes solitudes;
tare da sarakuna da mashawarta a cikin ƙasa, waɗanda suka gina wa kansu wuraren da yanzu duk sun rushe,
15 Avec les princes qui possèdent de l’or, et remplissent leurs maisons d’argent.
da shugabanni waɗanda suke da zinariya, waɗanda suka cika gidajensu da azurfa.
16 Ou bien je n’existerais pas, comme un avorton caché dans le sein de sa mère, ou comme ceux qui, conçus, n’ont pas vu la lumière.
Ko kuma don me ba a ɓoye ni a cikin ƙasa kamar jaririn da aka haifa ba rai ba, kamar jaririn da bai taɓa ganin hasken rana ba.
17 C’est là que des impies ont cessé leur tumulte, et là que se reposent ceux qui ont perdu leur force.
A wurin mugaye za su daina yin mugunta, gajiyayyu kuma za su huta.
18 Et ceux qui autrefois étaient enchaînes ensemble sont sans inquiétude; ils n’entendent pas la voix d’un exacteur.
Waɗanda aka daure za su sami jin daɗin; an sake su ba za su sāke jin ana tsawata masu ba.
19 Des grands et des petits sont là, et un esclave est délivré de son maître.
Manyan da ƙanana suna a can, bawa kuma ya sami’yanci daga wurin maigidansa.
20 Pourquoi la lumière a-t-elle été donnée aux malheureux, et la vie à ceux qui sont dans l’amertume de l’âme,
“Don me ake ba da haske ga waɗanda suke cikin ƙunci, rai kuma ga masu ɗacin rai
21 Qui attendent la mort (et elle ne vient pas), comme s’ils déterraient un trésor,
ga waɗanda suke neman mutuwa amma ba su samu ba, waɗanda suke nemanta kamar wani abu mai daraja a ɓoye,
22 Et qui se réjouissent extrêmement, lorsqu’ils ont trouvé un sépulcre;
waɗanda suke farin ciki sa’ad da suka kai kabari?
23 À un homme dont la voie est cachée, et que Dieu entoure de ténèbres?
Don me aka ba mutum rai, mutumin da bai san wani abu game da kansa ba, mutumin da Allah ya kange shi.
24 Avant que je mange, je soupire; et comme les eaux qui débordent, ainsi sont mes rugissements,
Baƙin ciki ya ishe ni maimakon abinci; ina ta yin nishi ba fasawa;
25 Parce que la frayeur que je redoutais m’est venue, et ce que j’appréhendais est arrivé.
Abin da nake tsoro ya faru da ni; abin da ba na so ya same ni.
26 N’ai-je pas dissimulé? n’ai-je pas gardé le silence? ne suis-je pas resté dans le repos? Cependant l’indignation de Dieu est venue sur moi.
Ba ni da salama, ba natsuwa; ba ni da hutu, sai wahala kawai.”