< Job 27 >

1 Job, prenant encore de nouveau sa parabole, dit:
Ayuba kuwa ya ci gaba da magana,
2 Vive Dieu, qui a écarté mon jugement, et le Tout-Puissant, qui a plongé mon âme dans l’amertume!
“Na rantse da Allah mai rai, wanda ya danne mini gaskiyata, Maɗaukaki, wanda ya sa nake cikin ɗacin rai.
3 Tant qu’il y aura haleine en moi, et un souffle de Dieu dans mes narines,
Muddin ina da rai a cikina kuma numfashin Allah yana cikin hancina,
4 Mes lèvres ne prononceront pas d’iniquité, et ma langue ne murmurera pas de mensonge.
bakina ba zai faɗi mugun abu ba, harshena kuma ba zai yi ƙarya ba.
5 Loin de moi que je juge que vous êtes justes; jusqu’à ce que je défaille, je ne me désisterai pas de mon innocence.
Ba zan taɓa yarda cewa kuna da gaskiya ba; har in mutu, ba zan daina kāre mutuncina ba.
6 Je n’abandonnerai pas ma justification que j’ai commencé à faire; car mon cœur ne me reproche rien dans toute ma vie.
Zan ci gaba da adalcina, ba zan fasa ba; lamirina ba zai taɓa yashe ni ba, dukan kwanakin raina.
7 Que mon ennemi soit comme un impie, et mon adversaire comme un injuste.
“Bari maƙiyana su zama kamar mugaye, masu gāba da ni kuma su zama kamar marasa adalci.
8 Car quel est l’espoir d’un hypocrite, s’il ravit par avarice, et que Dieu ne délivre point son âme?
Gama wane bege marar tsoron Allah yake da shi, lokacin da aka datse shi, lokacin da Allah ya ɗauke ransa?
9 Est-ce que Dieu entendra son cri, lorsque viendra sur lui l’angoisse?
Ko Allah yana sauraron kukansa lokacin da ƙunci ya auko masa?
10 Ou bien pourra-t-il mettre ses délices dans le Tout-Puissant, et invoquer Dieu en tout temps?
Ko zai sami farin ciki daga Maɗaukaki? Ko zai yi kira ga Allah a kowane lokaci?
11 Je vous enseignerai avec le secours de Dieu, ce que fait le Tout-Puissant, et je ne le cacherai pas.
“Zan koya muku game da ikon Allah; ba zan ɓoye hanyoyin Maɗaukaki ba.
12 Mais vous tous, vous le savez; et pourquoi dites-vous sans raison des choses vaines?
Duk kun ga wannan ku da kanku saboda haka me ya sa kuke maganganun nan marasa ma’ana?
13 Voici la part d’un homme impie devant Dieu, et l’héritage que les violents recevront du Tout-Puissant.
“Ga abin da mugaye za su samu gādon da azzalumi zai samu daga Maɗaukaki.
14 Si ses enfants se multiplient, ils appartiendront au glaive; et ses descendants ne se rassasieront pas de pain.
Kome yawan’ya’yansa, takobi za tă gama da su; zuriyarsa ba za su taɓa samun isashen abinci ba.
15 Ceux qui resteront de lui, seront ensevelis dans leur ruine, et ses veuves ne pleureront pas.
Waɗanda suka tsira annoba za tă kashe su, kuma gwaurayensu ba za su yi kukan mutuwarsu ba.
16 S’il accumule l’argent comme de la poussière, et s’il amasse des vêtements comme il ferait de la boue,
Ko da yake ya tara azurfa kamar ƙasa, tufafi kuma kamar tarin ƙasa,
17 Il les préparera, il est vrai, mais un juste s’en revêtira; et son argent, un innocent le partagera.
abin da ya tara masu adalci za su sa marasa laifi za su raba azurfarsa.
18 Il a bâti, comme les vers, sa maison, et, comme le gardien, il s’est fait un abri.
Gidan da ya gina kamar gidan gizo-gizo, kamar bukkar mai tsaro.
19 Un riche, lorsqu’il s’endormira, n’emportera rien avec lui; il ouvrira ses yeux, et il ne trouvera rien.
Attajiri zai kwanta, amma daga wannan shi ke nan; lokacin da zai buɗe idanunsa, kome ya tafi.
20 L’indigence le surprendra comme l’eau, qui déborde; pendant la nuit, une tempête l’accablera.
Tsoro zai kwashe shi kamar ambaliyar ruwa; Da dare iska za tă tafi da shi.
21 Un vent brûlant le saisira et l’emportera; et comme un tourbillon l’enlèvera de sa place.
Iskar gabas za tă tafi da shi; shi ke nan ya ƙare; za tă share shi daga wurinsa.
22 Et Dieu enverra sur lui l’infortune, et ne l’épargnera pas; lui fera tous ses efforts pour s’enfuir de sa main.
Za tă murɗe shi ba tausayi, lokacin da yake guje wa ikon iskar.
23 Celui qui regardera son lieu frappera sur lui des mains, et sifflera sur lui.
Zai tafa hannu yă yi tsaki yă kawar da shi daga wurinsa.”

< Job 27 >