< Job 23 >
1 Mais, répondant, Job dit:
Sa’an nan Ayuba ya amsa,
2 Maintenant encore mes paroles sont pleines d’amertume, et la violence de ma plaie s’est plus aggravée que mes gémissements.
“Ko a yau, ina kuka mai zafi; hannunsa yana da nauyi duk da nishin da nake yi.
3 Qui m’accordera que je sache trouver Dieu, et arriver jusqu’à son trône?
Da a ce na san inda zan same shi; da a ce zan iya zuwa wurin da yake zama!
4 J’exposerai ma cause devant lui, et je remplirai ma bouche de récriminations,
Zan kai damuwata wurinsa in yi gardama da shi.
5 Afin que je sache les paroles qu’il me répondra, et que je comprenne ce qu’il me dira.
Zan nemi in san abin da zai ce mini, in kuma auna abin da zai ce mini.
6 Je ne veux pas qu’il lutte contre moi avec beaucoup de force, ni qu’il m’accable par le poids de sa grandeur.
Zai yi gardama da ni da ikonsa mai girma? Babu, ba zai zarge ni da laifi ba.
7 Qu’il mette en avant contre moi l’équité, et ma cause obtiendra la victoire.
Mai adalci ne zai kawo ƙara a wurinsa, kuma zan samu kuɓuta daga wurin mai shari’an nan har abada.
8 Si je vais à l’orient, il ne paraît pas; si à l’occident, je ne l’aperçois point.
“Amma in na je gabas, ba ya wurin; in na je yamma, ba zan same shi ba.
9 Si c’est à gauche, que ferai-je? je ne l’atteindrai pas; si je me tourne à droite, je ne le verrai pas.
Sa’ad da yake aiki a arewa, ba ni ganinsa; sa’ad da ya juya zuwa kudu, ba na ganinsa.
10 Mais pour lui, il connaît ma voie, et il m’a éprouvé comme l’or qui passe par le feu.
Amma ya san hanyar da nake bi; sa’ad da ya gwada ni zan fito kamar zinariya.
11 Mon pied a suivi ses traces; j’ai gardé sa voie, et je ne m’en suis pas détourné,
Ƙafafuna suna bin ƙafafunsa kurkusa; na bi hanyarsa ba tare da na juya ba.
12 Je ne me suis pas écarté des commandements sortis de ses lèvres, et j’ai caché dans mon sein les paroles de sa bouche.
Ban fasa bin dokokin da ya bayar ba; na riƙe maganarsa da muhimmanci fiye da abincin yau da gobe.
13 Car lui est seul Tout-Puissant, et personne ne peut détourner sa pensée; et tout ce que son âme a voulu, elle l’a fait.
“Amma ya tsaya shi kaɗai, kuma wa ya isa yă ja da shi? Yana yin abin da yake so.
14 Quand il aura accompli en moi sa volonté, il aura encore un grand nombre de moyens semblables à sa disposition.
Yana yi mini abin da ya shirya yă yi mini, kuma yana da sauran irinsu a ajiye.
15 Et c’est pour cela qu’à sa face je suis troublé, et que, le considérant, je suis agité par la crainte.
Shi ya sa na tsorata a gabansa; sa’ad da na yi tunanin wannan duka, nakan ji tsoronsa.
16 Dieu a amolli mon cœur, et, le Tout-Puissant m’a épouvanté.
Allah ya sa zuciyata ta yi sanyi; Maɗaukaki ya tsorata ni.
17 Car je n’ai pas péri à cause des ténèbres qui me pressent, et une obscurité n’a pas couvert ma face.
Duk da haka duhun bai sa in yi shiru ba, duhun da ya rufe mini fuska.