< Job 22 >
1 Alors, répondant, Eliphaz, le Thémanite, dit:
Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
2 Est-ce qu’un homme peut être comparé à Dieu, quand il serait d’une science parfaite?
“Mutum yana iya zama da amfani a wurin Allah? Mai hikima ma zai iya zama da amfani a wurin shi?
3 Que sert à Dieu que tu sois juste? ou quel bien lui fais-tu si ta voie est sans tache?
Wane daɗi Allah zai ji in kai mai adalci ne? Wace riba zai samu in rayuwarka marar laifi ce?
4 Est-ce en craignant qu’il t’accusera, et qu’il viendra avec toi en jugement,
“Ko don kana tsoron Allah shi ya sa ya kwaɓe ka ya kuma bari haka yă same ka?
5 Et non pas à cause de ta malice très grande et de tes infinies iniquités?
Ba muguntarka ce ta yi yawa ba? Ba zunubanka ne ba iyaka ba?
6 Car tu as retenu le gage de tes frères sans raison, et tu as dépouillé de leurs vêtements ceux qui étaient nus.
Ka sa ɗan’uwanka yă biya ka bashin da kake binsa ba dalili; ka ƙwace wa mutanen rigunansu ka bar su tsirara.
7 Tu n’as pas donné de l’eau à celui qui était épuisé de lassitude, et à celui qui avait faim tu as soustrait du pain.
Ba ka ba masu jin ƙishirwa su sha ba kuma ka hana wa masu jin yunwa abinci su ci.
8 Par la force de ton bras tu possédais ta terre, et, étant le plus puissant, tu la conservais.
Ko da yake kai mai ƙarfi ne, ka mallaki ƙasa, mutum mai martaba kuma, kana zama cikin ƙasarka.
9 Tu as renvoyé les veuves les mains vides, et tu as brisé les bras des orphelins.
Ka kori gwauraye hannu wofi, ka kuma karya ƙarfin marayu.
10 C’est pour cela que tu es environné de pièges, et qu’une frayeur soudaine te trouble.
Shi ya sa kake kewaye da tarkuna, shi ya sa ka cika da tsoron mugun abin da zai auko maka.
11 Et tu pensais que tu ne verrais point de ténèbres, et que tu ne serais pas accablé par un impétueux débordement d’eaux.
An yi duhu ƙwarai, har ba ka iya gani, shi ya sa ambaliyar ruwa ta rufe ka.
12 Ne songes-tu pas que Dieu est plus élevé que le ciel, et qu’il est au-dessus du sommet des étoiles?
“Ba Allah ne a can sama ba? Dubi yadda taurarin sama suke can nesa a sama!
13 Et tu dis: Mais que connaît Dieu? car c’est comme à travers d’une profonde obscurité qu’il juge.
Duk da haka ka ce, ‘Me Allah ya sani? A cikin duhu ne yake shari’a?
14 Des nuées le cachent; il ne considère pas ce qui est de nous, et il parcourt les pôles du ciel.
Gajimare ya rufe shi, saboda haka ba ya ganinmu lokacin da yake takawa a cikin sammai.’
15 Est-ce que tu désires suivre le sentier des siècles, qu’ont foulé des hommes iniques,
Za ka ci gaba da bin tsohuwar hanyar da mugayen mutane suka bi?
16 Qui ont été enlevés avant leur temps, et dont un fleuve a renversé le fondement?
An ɗauke su kafin lokacinsu yă cika, ruwa ya share tushensu.
17 Qui disaient à Dieu: Retire-toi de nous; et qui estimaient que le Tout-Puissant ne pouvait rien faire;
Suka ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu! Me Maɗaukaki zai yi mana?’
18 Quoique ce fût lui qui eût rempli leurs maisons de biens. Que leur sentiment soit loin de moi!
Duk da haka kuwa shi ne ya cika gidajensu da abubuwa masu kyau, saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
19 Les justes les verront et ils se réjouiront, et l’innocent se moquera d’eux.
“Masu adalci suna gani ana hallaka mugaye, suna jin daɗi; marasa laifi suna yi musu ba’a, suna cewa,
20 Est-ce que leur élévation n’a pas été entièrement détruite? et leurs restes, un feu ne les a-t-il pas dévorés?
‘Ba shakka an hallaka maƙiyanmu, wuta kuma ta ƙona dukiyarsu.’
21 Soumets-toi donc à Dieu, et tu auras la paix; et par là tu auras des fruits excellents.
“Ka miƙa kanka ga Allah ka samu salamarsa; ta haka ne arziki zai zo maka.
22 Reçois de sa bouche sa loi, et mets ses discours dans ton cœur.
Ka bi umarnin da zai fito daga bakinsa kuma ka riƙe maganarsa a cikin zuciyarka.
23 Si tu reviens au Tout-Puissant, tu seras rétabli, et tu éloigneras l’iniquité de ton tabernacle.
In ka komo ga Maɗaukaki, za ka warke. In ka kawar da mugunta daga cikin gidanka.
24 Il te donnera au lieu de terre, un rocher, et au lieu d’un rocher, des torrents d’or.
Ka jefar da zinariyarka a ƙasa, ka jefar da zinariyar Ofir da ka fi so a cikin duwatsu,
25 Et le Tout-Puissant sera contre tes ennemis, et l’argent sera mis en monceaux pour toi.
sa’an nan ne Maɗaukaki zai zama zinariyarka, zai zama azurfa mafi kyau a wurinka.
26 Alors tu abonderas en délices dans le Tout-Puissant, et tu élèveras ta face vers Dieu.
Ba shakka a lokacin ne za ka sami farin ciki daga wurin Maɗaukaki, ku kuma ɗaga idanunku ga Allah
27 Tu le prieras, et il t’exaucera, et tu acquitteras tes vœux.
Za ka yi addu’a zuwa gare shi, zai kuwa ji ka, kuma za ka cika alkawuranka.
28 Tu décideras une chose, et elle se réalisera pour toi, et sur tes voies brillera la lumière.
Abin da ka zaɓa za ka yi za ka yi nasara a ciki, haske kuma zai haskaka hanyarka.
29 Car celui qui aura été humilié sera dans la gloire; et celui qui aura baissé les yeux, celui-là même sera sauvé,
Sa’ad da aka ƙasƙantar da mutane ka kuma ce, ‘A ɗaga su!’ Sa’an nan zai ceci masu tawali’u.
30 L’innocent sera sauvé, mais il sera sauvé à cause de la pureté de ses mains.
Zai ceci wanda ma yake mai laifi, wanda zai tsirar da shi ta wurin tsabtar hannuwanka.”