< Jérémie 4 >
1 Si tu reviens, Israël, dit le Seigneur, convertis-toi à moi: si tu ôtes de devant ma face tes pierres d’achoppement, tu ne seras pas ébranlé.
“In za ka komo, ya Isra’ila, ka komo gare ni,” in ji Ubangiji. “In ka kau da gumakanka masu banƙyama daga gabana ba ka ƙara karkace ba,
2 Et tu jureras dans la vérité, et dans le jugement, et dans la justice, disant: Le Seigneur vit, et les nations le béniront, et c’est lui qu’elles loueront.
kuma in cikin gaskiya da adalci ka rantse, ‘Muddin Ubangiji yana raye,’ to al’ummai za su sami albarka ta wurinsa kuma a cikinsa za su ɗaukaka.”
3 Car voici ce que dit le Seigneur à l’homme de Juda et de Jérusalem: Défrichez-vous une novale, et ne semez pas sur des épines;
Ga abin da Ubangiji yana ce wa mutanen Yahuda da kuma na Urushalima. “Ku nome ƙasarku kuma kada ku yi shuka cikin ƙayayyuwa.
4 Soyez circoncis au Seigneur, et ôtez les prépuces de vos cœurs, hommes de Juda, et habitants de Jérusalem; de peur que mon indignation ne sorte comme le feu, et qu’elle ne s’embrase, et qu’il n’y ait personne qui l’éteigne, à cause de la malice de vos pensées.
Ku yi wa kanku kaciya ga Ubangiji ku yi wa zukatanku kaciya, ku mutanen Yahuda da mutanen Urushalima, in ba haka ba hasalata za tă sauko ta ci kamar wuta saboda muguntar da kuka aikata za tă ci ba wanda zai kashe ta.
5 Annoncez dans Juda, et faites entendre dans Jérusalem; parlez et sonnez de la trompette sur la terre; criez fortement et dites: Assemblez-vous, et entrons dans les cités fortifiées;
“Ku yi shela a Yahuda ku kuma furta a Urushalima ku ce, ‘Ku busa ƙaho a ko’ina a ƙasar!’ Ku tā da murya da ƙarfi ku ce, ‘Ku tattaru! Bari mu gudu zuwa birane masu katanga!’
6 Levez un étendard en Sion. Fortifiez-vous, ne vous arrêtez pas, parce que moi, j’amène de l’aquilon un malheur et une grande destruction.
Ku tā da tuta don zuwa Sihiyona! Ku gudu ku nemi mafaka ba tare da jinkiri ba! Gama ina kawowa masifa daga arewa, mummunan hallaka kuwa.”
7 Le lion est monté de sa tanière, le brigand des nations s’est levé, il est sorti de son lieu, afin de faire de ta terre une solitude; tes cités seront ravagées, demeurant sans habitant.
Zaki ya fito daga ruƙuƙinsa; mai hallakarwar al’ummai ya kama hanya. Ya bar wurinsa don yă lalace ƙasarku. Garuruwanku za su zama kufai babu mazauna.
8 C’est pourquoi, ceignez-vous de cilices, pleurez et hurlez, parce que la colère de la fureur du Seigneur ne s’est pas détournée de nous.
Saboda haka ku yafa tufafin makoki, ku yi makoki da kuka, gama fushin Ubangiji bai juye daga gare mu ba.
9 Et il arrivera en ce jour-là, dit le Seigneur, le cœur du roi dépérira, ainsi que le cœur des princes; les prêtres seront dans la stupeur, et les prophètes seront consternés.
“A wannan rana,” in ji Ubangiji, “sarki da shugabanni za su fid da zuciya, firistoci za su razana, annabawa kuma za su yi mamaki.”
10 Et j’ai dit: Hélas, hélas, hélas, Seigneur Dieu, avez-vous donc trompé ce peuple et Jérusalem, disant: La paix sera avec vous; et voilà qu’un glaive est parvenu jusqu’à l’âme?
Sai na ce, “Kash, Ubangiji Mai Iko Duka, yaya ka ruɗi mutanen nan da kuma Urushalima gaba ɗaya haka ta wurin cewa, ‘Za ku zauna lafiya,’ sa’ad da takobi yana a maƙogwaronmu.”
11 En ce temps-là, on dira à ce peuple et à Jérusalem: Un vent brûlant s’élève dans les voies qui sont dans le désert de la voie de la fille de mon peuple, non pour vanner, et pour nettoyer le blé.
A lokacin za a faɗa wa mutanen nan da kuma Urushalima cewa, “Iska mai zafi daga tuddan hamada za tă hura zuwa wajen mutanena, amma ba don ta sheƙe ko ta rairaye; ba;
12 Un vent plein viendra d’elles vers moi, et alors moi je prononcerai mon arrêt contre eux.
iska mafificin ƙarfi da ta fito daga gare ni. Yanzu na zartar da hukuncina a kansu.”
13 Voilà qu’il montera comme une nuée, et ses chars seront comme la tempête, et ses chevaux plus rapides que les aigles; malheur à nous, parce que nous avons été dévastés.
Duba! Yana zuwa kamar gizagizai, kekunan yaƙinsa suna zuwa kamar guguwa, dawakansa sun fi gaggafa sauri. Kaiton mu! Mun shiga uku!
14 Purifie ton cœur de sa malice, ô Jérusalem, afin que tu sois sauvée; jusques à quand demeureront en toi les pensées funestes?
Ya Urushalima, ki wanke mugunta daga zuciyarki ki sami ceto. Har yaushe za ki zauna riƙe da mugayen tunani?
15 Car voici la voix de celui qui annonce de Dan, et qui fait connaître l’idole venant de la montagne d’Ephraïm.
Murya ta shela daga Dan, tana furtawa masifa daga tuddan Efraim.
16 Dites aux nations: Voilà qu’on a entendu dans Jérusalem que des gardes viennent d’une terre lointaine, et font entendre leur voix contre les cités de Juda.
“A faɗa wa al’ummai wannan, a furta wannan game Urushalima. ‘Sojoji masu ƙawanya suna zuwa daga ƙasa mai nisa, suna tā da kirarin yaƙi a kan biranen Yahuda.
17 Comme les gardiens d’un champ, ils se sont formés en cercle autour de Jérusalem, parce qu’elle m’a provoqué au courroux, dit le Seigneur.
Sun kewaye ta kamar masu gadin fili, domin ta yi mini tawaye,’” in ji Ubangiji.
18 Ce sont tes voies et tes pensées qui t’ont fait ces maux: c’est là ta malice, parce qu’elle est amère, parce qu’elle a atteint ton cœur.
“Halinki da ayyukanki sun kawo wannan a kanki. Hukuncinki ke nan. Yana da ɗaci! Ya soke ki har zuciyarki!”
19 Mes entrailles, mes entrailles sont pleines de douleur; les sentiments de mon cœur sont troublés au dedans de moi; je ne me tairai pas, parce que mon âme a entendu la voix d’une trompette, la clameur d’une bataille.
Azabana, azabana! Ina birgima cikin zafi. Azabana, azabar zuciyata! Zuciyata yana bugu a cikina, Ba zan yi shiru ba. Gama na ji karan ƙaho; na ji kirarin yaƙi.
20 Une ruine a été appelée sur une ruine, et toute la terre a été dévastée; tout à coup mes tabernacles, soudain mes pavillons ont été dévastés.
Masifa kan masifa; dukan ƙasar ta zama kufai. Cikin ɗan lokaci aka rurrushe tentuna nawa, mafakata ba zato.
21 Jusques à quand verrai-je des fuyards, entendrai-je la voix d’une trompette?
Har yaushe zan dubi tutar yaƙi in kuma ji karar ƙaho?
22 Parce que mon peuple insensé ne m’a pas connu; ce sont des fils déraisonnables et sans cœur, ils sont intelligents pour faire le mal, mais faire le bien, ils ne savent pas.
“Mutanena wawaye ne; ba su san ni ba. Su’ya’ya ne marasa azanci; ba su da fahimi. Suna da dabarar aikata mugunta; ba su san yadda za su aikata alheri ba.”
23 J’ai regardé la terre, et voici qu’elle était vide et de nulle valeur; J’ai regardé les cieux, et il n’y avait pas de lumière en eux.
Na dubi duniya, na ga cewa marar siffa ce babu kome; sammai kuma, haskensu ya tafi.
24 J’ai vu les montagnes, et voici qu’elles étaient ébranlées; et toutes les collines ont été bouleversées.
Na dubi duwatsu, sai na ga suna makyarkyata; dukan tuddai kuwa suna lilo.
25 J’ai regardé attentivement, et il n’y avait pas d’homme; et tout volatile du ciel s’était retiré.
Na duba, sai na ga ba kowa; kowane tsuntsu a sarari da ya tsere.
26 J’ai regardé, et voici que le Carmel était désert; et toutes ses villes ont été détruites devant la face du Seigneur, devant la face de la colère de sa fureur.
Na duba, sai na ga ƙasa mai amfani ta zama hamada; dukan garuruwanta sun zama kufai a gaban Ubangiji, a gaban zafin fushinsa.
27 Car voici ce que dit le Seigneur: Toute la terre sera déserte, mais cependant je n’achèverai pas sa ruine.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Dukan ƙasar za tă zama kufai, ko da yake ba zan hallaka ta gaba ɗaya ba.
28 La terre pleurera, et les cieux en haut s’affligeront de ce que j’ai parlé; j’ai formé un dessein, et je ne m’en suis point repenti, et je ne m’en détournerai pas.
Saboda haka duniya za tă yi kuka sammai a bisa kuma za su yi duhu, domin na yi magana kuma ba zan fasa ba, na yanke shawara ba kuwa zan janye ba.”
29 Au bruit des cavaliers et de ceux qui lancent des flèches, toute la ville a fui; ils sont entrés dans les lieux élevés; et ils ont gravi les rochers; toutes les villes ont été abandonnées, et il n’y habite pas d’homme.
Da jin motsin mahayan dawakai da maharba kowane gari ya ruga da gudu. Waɗansu suka shiga kurmi; waɗansu suka hau cikin duwatsu. Dukan garuruwan sun fashe tas; babu wani da yake zama a ciki.
30 Mais toi, dévastée, que feras-tu? quand tu te revêtirais de pourpre, quand tu serais ornée d’un collier d’or, et que tu peindrais tes yeux avec de l’antimoine, en vain tu serais embellie; ils t’ont méprisée, ceux qui t’aimaient, c’est ton âme qu’ils chercheront.
Me kike yi, ya wadda aka ragargaza? Me ya sa kika sanya mulufi kika sa kayan adon zinariya? Me ya sa kika sa wa idanunki tozali? Kin yi kwalliyarki a banza. Masoyanki sun bar ki; suna neman ranki.
31 J’ai entendu la voix comme d’une femme en travail; les angoisses comme d’une femme en couches; c’est la voix de la fille de Sion, qui se meurt, et qui étend les mains, en criant: Malheur à moi parce que mon âme a défailli à cause des tués.
Na ji kuka kamar na mace mai naƙuda, nishi kamar na wadda take haihuwa ɗanta na fari, kukan Diyar Sihiyona tana haki, da ƙyar take numfashi, tana miƙa hannuwanta tana cewa, “Wayyo ni kaina! Na suma; an ba da raina ga masu kisana.”