< Jérémie 35 >
1 Parole qui fut adressée à Jérémie par le Seigneur, dans les jours de Joakim, fils de Josias, roi de Juda, disant:
Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji a lokacin mulkin Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda.
2 Vas à la maison des Réchabites, et parle-leur; et tu les introduiras dans la maison du Seigneur, dans une des salles des trésors; et tu leur donneras à boire du vin.
“Ka tafi wurin iyalin Rekabawa ka gayyace su su zo a ɗaya daga cikin ɗakunan da suke gefe a gidan Ubangiji ka kuma ba su ruwan inabi su sha.”
3 Et je pris Jézonias, fils de Jérémie, fils d’Habsanias, et ses frères, et tous ses fils, et toute la maison des Réchabites;
Sai na tafi don in kawo Ya’azaniya ɗan Irmiya, ɗan Habazziniya, da’yan’uwansa da kuma dukan’ya’yansa maza, dukan iyalin Rekabawa.
4 Et je les introduisis dans la maison du Seigneur, dans la chambre du trésor des fils d’Hanan, fils de Jégédélias, homme de Dieu, laquelle chambre était près de la chambre du trésor des princes, au-dessus du trésor de Maasias, fils de Sellum, qui était garde du vestibule.
Na kawo su cikin gidan Ubangiji, a cikin ɗakin’ya’yan Hanan ɗan Igdaliya maza mutumin Allah. Ɗakin ne kusa da ɗakin fadawa, wanda yake bisa na Ma’asehiya ɗan Shallum mai tsaron ƙofa.
5 Et je mis devant les enfants de la maison des Réchabites des tasses pleines de vin et des coupes; et je leur dis: Buvez du vin.
Sai na ajiye ƙwarya cike da ruwan inabi da waɗansu kwaf a gaban iyalin Rekabawan na kuma ce musu, “Ku sha ruwan inabin.”
6 Et ils répondirent: Nous ne boirons pas de vin, parce que Jonadab, notre père, fils de Réchab, nous a ordonné, disant: Vous ne boirez jamais de vin, ni vous, ni vos enfants;
Amma sai suka amsa suka ce, “Ba ma shan ruwan inabi, domin kakanmu Yehonadab ɗan Rekab ya umarce mu cewa, ‘Ko ku, ko zuriyarku kada ku sha ruwan inabi.
7 Et vous ne bâtirez pas de maison, et vous ne sèmerez point de grains, et vous ne planterez pas de vignes, et vous n’en aurez point à vous, mais vous habiterez sous des tabernacles tous vos jours, afin que vous viviez de longs jours sur la terre dans laquelle vous êtes étrangers.
Haka kuma ba za ku gina gidaje, ku dasa iri ko ku nome gonakin inabi ba; kada ku kasance da wani daga cikin waɗannan abubuwa, amma dole kullum ku zauna a tentuna. Ta haka za ku yi dogon rai a cikin ƙasar baƙuncinku.’
8 Nous avons donc obéi à la voix de Jonadab, notre père, fils de Réchab, dans toutes les choses qu’il nous a ordonnées, en sorte que nous n’avons pas bu de vin durant tous nos jours, ni nous, ni nos femmes, ni nos fils, ni nos filles.
Mun yi biyayya da kome da kakanmu Yehonadab ɗan Rekab ya umarce mu. Mu ko matanmu ko’ya’yanmu maza da mata ba mu taɓa shan ruwan inabi ba
9 Et que nous n’avons pas bâti de maisons pour y habiter; et nous n’avons eu ni vigne, ni champ, ni grain.
ba mu kuma gina gidaje mu zauna a ciki ba ko mu yi gonakin inabi, gonaki ko hatsi ba.
10 Mais nous avons habité dans des tabernacles, et nous avons obéi à toutes les choses que nous a ordonnées Jonadab notre père.
Mun yi rayuwarmu a cikin tentuna mun kuma yi biyayya ƙwarai da kowane abin da kakanmu Yehonadab ya umarce mu.
11 Mais lorsque Nabuchodonosor, roi de Babylone, est monté dans notre terre, nous avons dit: Venez, et entrons dans Jérusalem, à cause de l’armée des Chaldéens et à cause de l’armée de Syrie; et nous sommes demeurés dans Jérusalem.
Amma da Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kawo wa ƙasan nan hari, sai muka ce, ‘Ku zo, dole mu tafi Urushalima don mu tsira daga Babiloniyawa da kuma sojojin Arameyawa.’ Saboda haka ne muke a Urushalima.”
12 Et la parole du Seigneur a été adressée à Jérémie, disant:
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
13 Voici ce que dit le Seigneur des armées, Dieu d’Israël: Va, et dis aux hommes de Juda et aux habitants de Jérusalem: Est-ce que vous ne recevrez jamais la correction, afin d’obéir à mes paroles, dit le Seigneur?
“Ga abin da Ubangiji, Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ka tafi ka faɗa wa mutanen Yahuda da kuma mutanen Urushalima cewa, ‘Ba za ku koyi darasi ku kuma yi biyayya da maganata ba?’ In ji Ubangiji.
14 Elles ont prévalu, les paroles de Jonadab, fils de Réchab, par lesquelles il ordonna à ses enfants de ne point boire de vin, et ils n’en ont pas bu jusqu’à ce jour, parce qu’ils ont obéi au précepte de leur père; mais moi je vous ai parlé, me levant dès le matin, et parlant, et vous ne m’avez pas obéi.
‘Yehonadab ɗan Rekab ya umarci’ya’yansa maza kada su sha ruwan inabi sun kuma kiyaye wannan umarni. Har yă zuwa yau ba sa shan ruwan inabi, domin sun yi biyayya da umarnin kakansu. Amma na yi muku magana sau da sau, duk da haka ba ku yi biyayya ba.
15 Et j’ai envoyé vers vous mes serviteurs, les prophètes, me levant au point du jour, envoyant, et disant: Détournez-vous chacun de vos voies très mauvaises, et rendez bonnes vos œuvres; ne suivez pas des dieux étrangers, et ne les adorez pas; et vous habiterez dans la terre que je vous ai donnée à vous et à vos pères; et vous n’avez pas incliné votre oreille, et vous ne m’avez pas écouté.
Sau da sau na aika dukan bayina annabawa gare ku. Suka ce, “Kowannenku ya juyo daga mugayen hanyoyinsa ya sabunta ayyukansa; kada yă bi waɗansu alloli don yă bauta musu. Ta haka za ku zauna a cikin ƙasar da na ba ku da kuma kakanninku.” Amma ba ku saurara ba, ba ku kuwa ji ni ba.
16 Ainsi les enfants de Jonadab, fils de Réchab, ont gardé fermement l’ordre que leur père leur avait donné; mais ce peuple ne m’a pas obéi.
Zuriyar Yehonadab ɗan Rekab sun yi biyayya da umarnin da kakansu ya ba su, amma waɗannan mutane ba su yi mini biyayya ba.’
17 C’est pourquoi voici ce que dit le Seigneur des armées, Dieu d’Israël: Voilà que moi j’amènerai sur Juda et sur tous les habitants de Jérusalem toute l’affliction que j’ai prononcée contre eux; parce que je leur ai parlé, et ils n’ont pas écouté; je les ai appelés, et ils ne m’ont pas répondu.
“Saboda haka, ga abin da Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Ku saurara! Zan kawo wa Yahuda da kuma kowane mutumin da yake zama a Urushalima kowace masifar da na ambata a kansu. Na yi musu magana, amma ba su saurara ba; na kira su, amma ba su amsa ba.’”
18 Or Jérémie dit à la maison des Réchabites: Voici ce que dit le Seigneur des armées. Dieu d’Israël: Parce que vous avez obéi au précepte de Jonadab votre père, que vous avez gardé tous ses commandements, et que vous avez fait toutes les choses qu’il vous a ordonnées;
Sai Irmiya ya ce wa iyalin Rekabawa, “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Kun yi biyayya da umarnin kakanku Yehonadab kuka kuma kiyaye dukan umarnansa kuka yi kome bisa ga tsari.’
19 À cause de cela, voici ce que dit le Seigneur des armées. Dieu d’Israël: Il ne manquera pas dans la race de Jonadab, fils de Réchab, d’homme se tenant tous les jours en ma présence.
Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Yehonadab ɗan Rekab ba zai taɓa rasa mutumin da zai yi mini hidima ba.’”