< Jérémie 29 >

1 Et voici les paroles de la lettre que Jérémie le prophète envoya de Jérusalem aux restes des anciens de la transmigration, et aux prêtres, et aux prophètes, et à tout le peuple que Nabuchodonosor avait fait passer de Jérusalem à Babylone.
Ga abin da yake cikin wasiƙar annabi Irmiya da ya aika daga Urushalima zuwa ga sauran dattawan da suka ragu a cikin masu zaman bauta da kuma zuwa ga firistoci, annabawa da kuma dukan sauran mutanen da Nebukadnezzar ya kwashe zuwa zaman bauta daga Urushalima zuwa Babilon.
2 Après que le roi Jéchonias fut sorti de Jérusalem, ainsi que la reine, et les eunuques, et les princes de Juda et de Jérusalem, et l’artisan, et le lapidaire;
(Wannan ya faru bayan Sarki Yekoniya da mahaifiyar sarauniya, shugabannin fada da kuma dukan shugabannin Yahuda da Urushalima, gwanayen sana’a da masu sassaƙa suka tafi zaman bauta daga Urushalima.)
3 Par l’entremise d’Elasa, fils de Saphan, et par Gamarias, fils d’Helcias, que Sédécias, roi de Juda, envoya à Nabuchodonosor, roi de Babylone, à Babylone, Jérémie, disait:
Ya ba da wasiƙar ta hannun Eleyasa ɗan Shafan da Gemariya ɗan Hilkiya, waɗanda Zedekiya sarkin Yahuda ya aika wurin Sarki Nebukadnezzar a Babilon. Wasiƙar ta ce,
4 Voici ce que dit le Seigneur des armées, Dieu d’Israël, à tous les fils de la transmigration que j’ai transférés de Jérusalem à Babylone:
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ga dukan waɗanda aka kwashe zuwa zaman bauta daga Urushalima zuwa Babilon.
5 Bâtissez des maisons, et habitez-les; plantez des jardins et mangez-en les fruits;
“Ku gina gidaje ku zauna; ku dasa gonaki ku kuma ci abin da suka haifar.
6 Prenez des femmes, et engendrez des fils et des filles; donnez à vos fils des femmes, et donnez vos filles à des maris, et qu’elles enfantent des fils et des filles; et multipliez-vous là, et ne soyez pas en petit nombre.
Ku yi aure ku kuma haifi’ya’ya maza da mata; ku nemi mata wa’ya’yanku maza, ku kuma ba da’ya’yanku mata ga aure, saboda su ma za su haifi’ya’ya maza da mata. Ku riɓaɓɓanya a can, kada ku ragu.
7 Et recherchez la paix de la cité dans laquelle je vous ai fait émigrer, et priez pour elle le Seigneur, parce que dans sa paix sera votre paix.
Haka kuma, ku nemi zaman salama da cin gaba a birnin da aka kai ku zaman bauta. Ku yi addu’a ga Ubangiji saboda birnin, domin in ya ci gaba, ku ma za ku ci gaba.”
8 Car voici ce que dit le Seigneur des armées. Dieu d’Israël: Qu’ils ne vous séduisent pas, vos prophètes qui sont au milieu de vous, et vos devins; et ne faites pas attention aux songes que vous songez;
I, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa, “Kada ku bar annabawa da masu sihiri a cikinku su ruɗe ku. Kada ku saurari mafarkan da dā kuke ƙarfafa su su yi.
9 Parce que c’est faussement qu’eux vous prophétisent en mon nom, et je ne les ai point envoyés, dit le Seigneur,
Suna muku annabcin ƙarya da sunana. Ban aike su ba,” in ji Ubangiji.
10 Parce que voici ce que dit le Seigneur: Lorsque soixante-dix ans auront commencé d’être accomplis à Babylone, je vous visiterai; et je réaliserai pour vous ma bonne parole en vous ramenant en ce lieu.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Sa’ad da shekaru saba’in suka cika a Babilon, zan zo muku in cika alkawarin alherina don in komo da ku zuwa wannan wuri.
11 Car moi, je sais les pensées que je pense sur vous, dit le Seigneur, pensées de paix et non d’affliction: c’est de vous accorder la fin de vos maux et la patience.
Gama na san shirye-shiryen da na yi muku,” in ji Ubangiji, “shirye-shiryen cin gaba ba na cutarwa ba, shirye-shiryen ba ku sa zuciya da kuma na nan gaba.
12 Et vous m’invoquerez, et vous partirez; vous me prierez, et moi je vous exaucerai.
Sa’an nan za ku kira gare ni ku zo ku kuma yi addu’a gare ni, zan kuwa ji ku.
13 Vous me chercherez et vous me trouverez, lorsque vous m’aurez cherché de tout votre cœur.
Za ku neme ni ku kuwa same ni sa’ad da kuka neme ni da dukan zuciyarku.
14 Et je serai trouvé par vous, dit le Seigneur; et je vous ramènerai vos captifs, et je vous rassemblerai du milieu de toutes les nations et de tous les lieux dans lesquels je vous ai chassés, dit le Seigneur; et je vous ferai revenir du lieu dans lequel je vous ai fait émigrer,
Za ku same ni,” in ji Ubangiji, “zan kuma komo da ku daga bauta. Zan tattaro ku daga dukan al’ummai in sa ku inda na kore ku,” in ji Ubangiji, “zan kuma komo da ku zuwa wurin da na kwashe ku zuwa zaman bauta.”
15 Parce que vous avez dit: Le Seigneur a suscité pour nous des prophètes à Babylone.
Za ku iya ce, “Ubangiji ya tā da annabawa saboda mu a Babilon.”
16 Parce que voici ce que dit le Seigneur au roi qui est assis sur le trône de David, et à tout le peuple habitant de cette ville, à vos frères qui ne sont pas allés avec vous en captivité.
Amma ga abin da Ubangiji yana cewa game da sarki, wanda yake zaune a kursiyin Dawuda da kuma dukan mutanen da suka ragu a wannan birni,’yan’uwanku waɗanda ba su tafi tare da ku zuwa zaman bauta ba.
17 Voici ce que dit le Seigneur des armées: Voilà, j’enverrai contre eux le glaive, la famine et la peste, et je les rendrai comme des figues mauvaises, qui ne peuvent être mangées, parce qu’elles sont très mauvaises.
I, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Zan aika da takobi, yunwa da annoba a kansu zan kuma sa su zama kamar ɓaure marar amfani da suka yi munin da ba a iya ci.
18 Et je les poursuivrai par le glaive, et par la famine, et par la peste; et je les livrerai en vexation à tous les royaumes de la terre; en malédiction, et en stupeur, et en sifflement, et en opprobre, à toutes les nations chez lesquelles moi-même je les ai chassés;
Zan fafare su da takobi, yunwa da annoba zan kuma sa su zama abin ƙyama ga dukan mulkokin duniya da kuma abin la’ana da abin bantsoro, abin dariya da abin reni, a cikin dukan al’umman da aka kore su zuwa.
19 Parce qu’ils n’ont pas écouté mes paroles, dit le Seigneur, que je leur ai adressées par mes serviteurs les prophètes, me levant durant la nuit, et les envoyant; et vous ne m’avez pas écouté, dit le Seigneur.
Gama ba su saurari maganata ba,” in ji Ubangiji, “maganar da na aika gare su sau da sau ta bayina annabawa. Ku kuma masu zaman bauta ba ku saurara ba,” in ji Ubangiji.
20 Vous donc, écoutez la parole du Seigneur, vous tous, fils de la transmigration, que j’ai envoyés de Jérusalem à Babylone.
Saboda haka, ku ji maganar Ubangiji, dukanku masu zaman bauta waɗanda na aika daga Urushalima zuwa Babilon.
21 Voici ce que dit le Seigneur des armées. Dieu d’Israël, à Achab, fils de Colias, et à Sédécias, fils de Maasias, qui vous prophétisent en mon nom le mensonge: Voilà que moi je les livrerai aux mains de Nabuchodonosor, roi de Babylone, et il les frappera sous vos yeux.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa game da Ahab ɗan Kolahiya da Zedekiya ɗan Ma’asehiya, waɗanda suke muku annabcin ƙarya da sunana. “Zan ba da su ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, zai kuwa kashe su a gaban idanunku.
22 Et ils seront pris comme exemple de malédiction par tous les fils de la transmigration de Juda qui sont à Babylone, et qui diront: Que le Seigneur te traite comme Sédécias et comme Achab, que le roi de Babylone a fait griller au feu,
Saboda su, dukan masu zaman bauta daga Yahuda waɗanda suke a Babilon za su yi amfani da wannan la’ana cewa, ‘Ubangiji ka yi da mu kamar Zedekiya da Ahab waɗanda sarkin Babilon ya ƙone da wuta.’
23 Parce qu’ils ont fait une folie dans Israël, et qu’ils ont commis l’adultère avec les femmes de leurs amis, et qu’ils ont dit faussement en mon nom ce que je ne leur ai pas commandé; c’est moi qui suis le juge et le témoin, dit le Seigneur.
Gama sun aikata munanan abubuwa a Isra’ila; sun yi zina da matan maƙwabtansu kuma da sunana suka yi ƙarya, waɗanda ban faɗa musu su yi ba. Na san wannan kuma ni shaida ne ga haka,” in ji Ubangiji.
24 Et tu diras à Séméias, le Néhélamite:
Faɗa wa Shemahiya mutumin Nehelam,
25 Voici ce que dit le Seigneur des armées, Dieu d’Israël: Parce que tu as envoyé des lettres en ton nom à tout le peuple qui est dans Jérusalem et à Sophonias, fils de Maasias et prêtre, et à tous les prêtres, disant:
“Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ka aika da wasiƙu da sunanka ga dukan mutane a Urushalima, zuwa ga Zefaniya ɗan Ma’asehiya firist da kuma ga sauran firistoci. Ka ce wa Zefaniya,
26 Le Seigneur t’a établi prêtre à la place du pontife Joïada, afin que tu sois chef dans la maison du Seigneur, ayant autorité sur tout, homme saisi d’une fureur prophétique, et prophétisant, afin que tu le mettes dans les fers et dans la prison.
‘Ubangiji ya naɗa ka firist a wurin Yehohiyada don ka lura da gidan Ubangiji; ya kamata ka sa kowane mahaukaci wanda yake yi kamar annabi cikin turu da kuma a kangi.
27 Et maintenant pourquoi n’as-lu pas repris Jérémie, l’Anathothite, qui vous prophétise?
To, me ya sa ba ka tsawata wa Irmiya daga Anatot, wanda yana ɗauka kansa annabi a cikinku ba?
28 Parce qu’outre cela, il a envoyé vers nous à Babylone, disant: C’est long; bâtissez des maisons et habitez-les, et plantez des jardins, et mangez-en les fruits.
Ya aiko mana da saƙonsa a Babilon cewa zai ɗauki lokaci ƙwarai. Saboda haka ku gina gidaje ku zauna; ku dasa gonaki ku kuma ci abin da suka haifar.’”
29 Sophonias le prêtre lut donc cette lettre aux oreilles de Jérémie le prophète.
Zefaniya firist kuwa, ya karanta wasiƙar annabi Irmiya.
30 Et la parole du Seigneur fut adressée à Jérémie, disant:
Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
31 Envoie vers tous les fils de la transmigration, disant: Voici ce que dit le Seigneur à Séméias, le Néhélamite: Parce que Séméias a prophétisé, et que moi je ne l’ai pas envoyé; et qu’il vous a fait vous confier dans un mensonge;
“Ka aika da wannan saƙo zuwa ga dukan masu zaman bauta cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa game da Shemahiya, mutumin Nehelam. Domin Shemahiya ya yi muku annabci, ko da yake ban aike shi ba, ya kuma sa kuka gaskata ƙarya,
32 C’est pour cela que voici ce que dit le Seigneur: Voilà que moi je visiterai Séméias le Néhélamite et sa race; il n’aura pas d’homme de sa race assis au milieu de ce peuple, et il ne verra pas le bien que moi je ferai à mon peuple, dit le Seigneur, parce qu’il a proféré des paroles de prévarication contre le Seigneur.
ga abin da Ubangiji yana cewa, tabbatacce zan hukunta Shemahiya mutumin Nehelam da zuriyarsa. Ba zai kasance da wani da ya rage a cikin wannan mutane ba, ba kuwa zai ga abubuwa alherin da zan yi wa mutanena ba, in ji Ubangiji, domin ya yi wa’azin tawaye a kaina.’”

< Jérémie 29 >