< Jérémie 11 >

1 Parole qui fut adressée par le Seigneur à Jérémie, disant:
Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji.
2 Ecoutez les paroles de cette alliance, et parlez aux hommes de Juda, et aux habitants de Jérusalem;
“Ka saurari zancen wannan alkawari ka kuma faɗe su ga mutanen Yahuda da kuma waɗanda suke zaune a Urushalima.
3 Et tu leur diras: Voici ce que dit le Seigneur, le Dieu d’Israël: Maudit l’homme qui n’écoutera pas les paroles de cette alliance,
Ka faɗa musu cewa ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa, ‘La’ananne ne wanda bai kula da zancen alkawarin nan ba,
4 Que je prescrivis à vos pères, au jour où je les fis sortir de la terre d’Egypte, de la fournaise de fer, disant: Ecoutez ma voix, et faites tout ce que je vous ordonne; et vous serez mon peuple, et moi je serai votre Dieu;
zancen da na umarci kakanni-kakanninku sa’ad da na fitar da su daga Masar, daga cikin tanderun narkewar ƙarfe.’ Na ce, ‘Ku yi mini biyayya ku kuma aikata kowane abin da na umarce ku, za ku kuwa zama mutanena, ni kuwa zan zama Allahnku.
5 Afin que je fasse revivre le serment que je jurai à vos pères de leur donner une terre où couleraient du lait et du miel, comme c’est en ce jour. Et je répondis et je dis: Amen, Seigneur.
Sa’an nan zan cika rantsuwar da na yi wa kakanni-kakanninku, da zan ba su ƙasa mai zub da madara da kuma zuma’ ƙasar da kuka mallaka a yau.” Sai na amsa na ce, “Amin, Ubangiji.”
6 Et le Seigneur me dit: Crie à haute voix ces paroles dans toutes les cités de Juda, et en dehors de Jérusalem, disant: Ecoutez les paroles de cette alliance et observez-les;
Sai Ubangiji ya ce mini, “Ka yi shelar dukan maganan nan a biranen Yahuda da titunan Urushalima duka cewa, ‘Su saurari zancen alkawarin nan, su aikata.
7 Car prenant à témoin, j’ai pris à témoin vos pères, depuis le jour où je les fis sortir de la terre d’Egypte jusqu’à ce jour; me levant dès le matin, je les ai pris à témoin et j’ai dit: Ecoutez ma voix;
Daga lokacin da na fitar da kakanni-kakanninku daga Masar har yă zuwa yau, na gargaɗe su sau da sau, ina cewa, “Ku yi mini biyayya.”
8 Et ils n’ont pas écouté, et ils n’ont pas incliné leur oreille; mais ils ont suivi chacun la dépravation de son cœur mauvais; et j’ai amené sur eux toutes les paroles de cette alliance que je leur ai commandé d’observer, et qu’ils n’ont pas observée.
Amma ba su kasa kunne ko su saurara ba, a maimako, sai suka bi taurinkai na mugayen zukatansu. Saboda haka na kawo musu dukan la’anonin alkawarin da na riga na umarce su, su bi amma ba su kiyaye ba.’”
9 Et le Seigneur me dit: Il a été découvert une conjuration parmi les hommes de Juda et les habitants de Jérusalem.
Sa’an nan Ubangiji ya ce mini, “Akwai maƙarƙashiya a cikin mutanen Yahuda da waɗanda suke zaune a Urushalima.
10 Ils sont revenus aux premières iniquités de leurs pères, qui n’ont pas voulu écouter mes paroles; ceux-ci donc sont allés de même après des dieux étrangers, afin de les servir; la maison d’Israël et la maison de Juda ont rendu vaine l’alliance que j’avais conclue avec leurs pères.
Sun koma ga zunuban kakanni kakanninsu, waɗanda suka ƙi su saurari maganata. Suka bi waɗansu alloli don su bauta musu. Da gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda duk sun take alkawarin da na yi da kakanni kakanninsu.
11 À cause de cela, voici ce que dit le Seigneur: Voilà que j’amènerai sur eux des maux dont ils ne pourront sortir; et ils crieront vers moi, et je ne les exaucerai pas.
Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Zan kawo masifa a kansu wadda ba za su iya tsere mata ba. Ko da yake suna kuka gare ni, ba zan saurare su ba.
12 Et les cités de Juda et les habitants de Jérusalem iront et crieront aux dieux auxquels ils font des libations, et ces dieux ne les sauveront pas au temps de leur affliction.
Garuruwan Yahuda da mutanen Urushalima za su tafi su yi kuka ga allolin da suke ƙona wa turare, amma ba za su taimake su ba sam sa’ad da masifar ta auku.
13 Car selon le nombre de tes cités étaient tes dieux, ô Juda, et selon le nombre de tes rues, ô Jérusalem, tu as élevé des autels de confusion, des autels pour faire des libations aux Baalim.
Kuna da alloli masu yawa yadda kuke da garuruwa, ya Yahuda; kuma bagadan da kuka yi don ƙona turare wa allahn nan Ba’al abin kunya sun yi yawa kamar titunan Urushalima.’
14 Toi donc, ne prie pas pour ce peuple, et ne m’adresse pour eux ni louange, ni prière, parce que je ne les exaucerai pas au temps de leur cri vers moi, au temps de leur affliction.
“Kada ka yi addu’a domin wannan mutane ko ka miƙa wani roƙo ko kuka dominsu, domin ba zan saurara ba sa’ad da suka kira gare ni a lokacin ƙuncinsu.
15 Pourquoi est-ce que mon bien-aimé a dans ma maison commis beaucoup de crimes? est-ce que des chairs saintes ôteront de toi tes méchancetés dont tu t’es glorifiée?
“Mene ne ƙaunatacciyata take yi a haikali da yake ta yin ƙulle-ƙullen mugayen makircinta tare da mutane masu yawa? Tsarkakar nama zai iya kawar da hukuncinki? Sa’ad da kike yin muguntarki sa’an nan ki yi farin ciki.”
16 Olivier fertile, beau, chargé de fruits, superbe, le Seigneur t’a appelée de ce nom; à la voix de sa parole, un grand feu s’est allumé dans cet olivier, et ses rameaux ont été brûlés.
Ubangiji ya kira ki itacen zaitun mai inuwa kyakkyawa mai’ya’ya masu kyau. Amma da ƙugin babbar hadari zai cinna masa wuta, rassansa za su kakkarye.
17 Et le Seigneur des armées qui t’a planté, a prononcé le mal sur toi, à cause des maux de la maison d’Israël et de la maison de Juda, qu’elles se sont faits à elles-mêmes pour m’irriter en faisant des libations aux Baalim.
Ubangiji Maɗaukaki, wanda ya dasa ki, ya furta miki masifa, domin gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda sun aikata mugunta suka kuma tsokane ni in yi fushi ta wurin ƙona wa Ba’al turare.
18 Mais vous. Seigneur, vous m’avez fait voir leurs pensées, et je les ai connues; alors vous m’avez montré leurs œuvres.
Domin Ubangiji ya bayyana mini maƙarƙashiyarsu, na santa, gama a wannan lokaci ya nuna mini abin da suke yi.
19 Et moi, j’ai été comme un agneau plein de douceur que l’on porte pour en faire une victime; et je n’ai pas su qu’ils formaient contre moi des projets, disant: Mettons du bois dans son pain, rayons-le de la terre des vivants, et que son nom ne soit plus rappelé dans la mémoire.
Na kasance kamar ɗan rago marar faɗa wanda aka kai mayanka; ban gane cewa sun ƙulla mini maƙarƙashiya, suna cewa, “Bari mu lalatar da itacen duk da’ya’yansa; bari mu datse shi daga ƙasar masu rai, har da ba za a ƙara tunawa da sunansa ba.”
20 Mais vous, Seigneur Sabaoth, vous qui jugez justement et qui éprouvez les reins et les cœurs, que je voie votre vengeance sur eux; car je vous ai révélé ma cause.
Amma, ya Ubangiji Maɗaukaki, kai da kake yin shari’a da adalci kake gwada zuciya da kuma tunani, ka sa in ga sakayyar da za ka yi musu, gama a gare ka na danƙa maganata.
21 À cause de cela, voici ce que dit le Seigneur aux hommes d’Anathoth, qui cherchent mon âme, et disent: Tu ne prophétiseras pas au nom du Seigneur, et tu ne mourras pas de nos mains.
“Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa game da mutanen Anatot, waɗanda suke neman ranka suna kuma cewa, ‘Kada ka yi annabci da sunan Ubangiji in ba haka za ka mutu a hannunmu’
22 C’est pourquoi voici ce que dit le Seigneur des armées: Voilà que moi je les visiterai; les jeunes hommes mourront par le glaive, leurs fils et leurs filles mourront de faim.
saboda haka ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, ‘Zan hukunta su. Samarinsu za su mutu ta wurin takobi,’ya’yansu maza da mata kuwa ta wurin yunwa.
23 Et rien ne restera d’eux; car j’amènerai le mal sur les hommes d’Anathoth, l’année de leur visite.
Babu raguwar da za a bar musu, domin zan kawo masifa a kan mutanen Anatot a shekarar hukuncinsu.’”

< Jérémie 11 >