< Jacques 2 >

1 Mes frères, ne joignez pas l’acception des personnes à la foi que vous avez en Notre Seigneur Jésus-Christ, le Seigneur de la gloire.
’Yan’uwana, a matsayinmu cikin Ubangiji Yesu Kiristi maɗaukaki, kada ku nuna bambanci.
2 Car s’il entre dans votre assemblée un homme ayant un anneau d’or et un vêtement splendide, et qu’il y entre aussi un pauvre mal vêtu,
A ce wani ya shigo cikin taronku saye da zoben zinariya da riguna masu tsada, wani matalauci kuma saye da tsummoki shi ma ya shigo,
3 Et que vous arrêtiez la vue sur celui qui aie vêtement splendide, et lui disiez: Assieds-toi bien ici; tandis qu’au pauvre vous disiez: Tiens-toi là debout, où assieds-toi sur l’escabeau de mes pieds;
in kuka mai da hankali na musamman ga mutumin da yake da riguna masu tsadan nan kuka kuma ce, “Ga wurin zama mai kyau dominka,” amma kuka ce wa matalaucin nan, “Kai tsaya daga can,” ko kuwa, “Ka zauna a ƙasa kusa da ƙafafuna,”
4 Ne jugez-vous pas par vous-mêmes, et ne vous faites-vous pas juges avec des pensées d’iniquité?
ashe, ba ku nuna bambanci a tsakaninku ke nan ba, kuka kuma zama alƙalai masu mugayen tunani?
5 Ecoutez, mes frères bien-aimés; Dieu n’a-t-il pas choisi les pauvres en ce monde pour être riches dans la foi, et héritiers du royaume que Dieu a promis à ceux qui l’aiment?
Ku saurara,’yan’uwana ƙaunatattu. Ashe, Allah bai zaɓi waɗanda suke matalauta a idon duniya don su zama masu wadata cikin bangaskiya, su kuma gāji mulkin da ya yi wa masu ƙaunarsa alkawari ba?
6 Mais vous avez, vous, déshonoré le pauvre. Ne sont-ce pas les riches qui vous oppriment par leur puissance, et eux-mêmes qui vous traînent devant les tribunaux?
Ga shi kun wulaƙanta matalauta. Ashe, ba masu arziki ne suke cutarku ba? Ba su ba ne suke jan ku zuwa kotu?
7 Ne sont-ce pas eux qui blasphèment le saint nom qui a été invoqué sur vous?
Ba su ba ne suke ɓata sunan nan mai martaba wanda aka san ku da shi ba?
8 Si cependant vous accomplissez la loi royale selon les Ecritures: Tu aimeras ton prochain comme toi-même, vous faites bien.
In fa kun kiyaye dokan nan ta mulki wadda take cikin Nassi mai cewa, “Ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka,” kun yi daidai.
9 Mais si vous faites acception des personnes, vous commettez un péché, et vous êtes condamnés par la loi comme transgresseurs.
Amma in kuka nuna bambanci, kun yi zunubi ke nan shari’a kuma ta same ku da laifi a matsayin masu karya doka.
10 Car quiconque a gardé toute la loi, et l’a violée en un seul point, devient coupable de tous.
Gama duk wanda ya kiyaye dukan doka amma ya yi tuntuɓe a kan abu ɗaya kaɗai, ya zama mai laifin karya dukansu ke nan.
11 En effet, celui qui a dit: Tu ne commettras point d’adultère, a dit aussi: Tu ne tueras point. Si donc tu ne commets pas d’adultère, mais que tu tues, tu es violateur de la loi.
Gama shi da ya ce, “Kada ka yi zina,” shi ne kuma ya ce, “Kada ka yi kisankai.” In kuwa ba ka zina amma kana kisankai, ka zama mai karya doka ke nan.
12 Parlez et agissez comme devant être jugés par la loi de la liberté.
Ku yi magana ku kuma yi aiki kamar waɗanda za a yi musu shari’a bisa ga doka mai ba da’yanci,
13 Car le jugement est sans miséricorde pour celui qui n’a pas fait miséricorde; mais la miséricorde s’élève au-dessus du jugement.
gama za a yi wa duk wanda bai nuna jinƙai ba hukunci babu jinƙai. Jinƙai yakan yi nasara a kan hukunci!
14 Que servira-t-il, mes frères, que quelqu’un dise qu’il a la foi, s’il n’a point les œuvres? Est-ce que la foi pourra le sauver?
Wanda amfani ne,’yan’uwana, a ce wani yă ce yana da bangaskiya, amma ba shi da ayyuka? Anya, wannan bangaskiya za tă iya cetonsa kuwa?
15 Si un de vos frères ou une de vos sœurs sont nus, et s’ils manquent de la nourriture de chaque jour,
A ce wani ɗan’uwa ko’yar’uwa ba shi da riguna ko abincin yini,
16 Et qu’un de vous leur dise: Allez en paix, réchauffez-vous et rassasiez-vous, sans leur donner ce qui est nécessaire au corps, à quoi cela leur servira-t-il?
sai waninku yă ce masa, “Sauka lafiya, Allah ya ba da ci da sha da kuma sutura,” amma bai yi wani abu game da bukatunsa na jiki ba, ina amfani?
17 Ainsi la foi, si elle n’a pas les œuvres, est morte en elle-même.
Haka ma bangaskiya ita kaɗai, in ba tare da ayyuka ba, matacciya ce.
18 Mais, dira quelqu’un: Toi, tu as la foi, et moi j’ai les œuvres; montre-moi ta foi sans les œuvres, et moi je te montrerai ma foi par mes œuvres.
Amma wani zai ce, “Kai kana da bangaskiya; ni kuma ina da ayyuka.” Ka nuna mini bangaskiyarka ba tare da ayyuka ba, ni kuma zan nuna maka bangaskiyata ta wurin abin da nake yi.
19 Tu crois qu’il n’y a qu’un Dieu, tu fais bien; mais les démons croient aussi, et ils tremblent.
Ka gaskata cewa Allah ɗaya ne. To, da kyau! Ai, ko aljanu ma sun gaskata wannan, har da rawan jiki.
20 Or veux-tu savoir, ô homme vain, que la foi sans les œuvres est morte?
Kai wawa, kana son tabbaci cewa bangaskiya marar ayyuka banza ce?
21 Abraham, notre père, ne fut-il pas justifié par les œuvres, lorsqu’il offrit son fils Isaac sur l’autel?
Ashe, ba a mai da kakanmu Ibrahim mai adalci saboda abin da ya yi ba ne sa’ad da ya miƙa ɗansa Ishaku a bisa bagade?
22 Tu vois que la foi coopérait à ces œuvres, et que c’est par ses œuvres que la loi fut consommée.
Ai, ka gani cewa bangaskiyarsa da ayyukansa sun yi aiki tare, bangaskiyarsa kuma ta zama cikakkiya ta wurin abin da ya yi.
23 Et ainsi fut accomplie l’Ecriture, qui dit: Abraham crut, et ce lui fut imputé à justice, et il fut appelé ami de Dieu.
Aka kuma cika nassin nan da ya ce, “Ibrahim ya gaskata Allah, aka kuma lissafta wannan adalci ne gare shi,” aka kuma ce da shi abokin Allah.
24 Vous voyez donc que c’est par les œuvres que l’homme est justifié, et non par la foi seulement.
Kun ga cewa ashe mutum zai sami kuɓuta ta wurin abin da ya yi ne ba ta wurin bangaskiya kaɗai ba.
25 De même Rahab, cette femme de mauvaise vie, n’est-ce pas par les œuvres qu’elle fut justifiée, recevant les espions et les renvoyant par un autre chemin?
Ta haka kuma ashe, Rahab karuwan nan ba a ɗauke ta mai adalci ce saboda abin da ta yi ba ne sa’ad da ta ba wa’yan leƙen asirin nan masauƙi ta kuma sallame su suka tafi ta wata hanya dabam?
26 Car comme le corps sans l’esprit est mort, ainsi la foi elle-même sans les œuvres est morte.
Kamar yadda jikin da babu ruhu matacce ne, haka ma bangaskiyar da babu ayyuka matacciya ce.

< Jacques 2 >