< Isaïe 7 >

1 Et il arriva dans les jours d’Achaz, fils de Joathan, fils d’Ozias, roi de Juda, que Rasin, roi de Syrie, et Phacée, fils de Romélie, roi d’Israël, montèrent à Jérusalem pour lui livrer bataille; et ils ne purent la réduire.
Sa’ad da Ahaz ɗan Yotam, ɗan Uzziya, yake sarkin Yahuda, Sarki Rezin na Aram da Feka ɗan Remaliya sarkin Isra’ila suka haura don su yaƙi Urushalima, amma ba su iya cinta da yaƙi ba.
2 Et on l’annonça à la maison de David, en disant: La Syrie a trouvé un appui dans Ephraïm; et le cœur d’Achaz fut agité ainsi que le cœur du peuple, comme la face du vent.
Sai fa aka faɗa wa gidan Dawuda cewa, “Aram ya haɗa kansa da Efraim”; saboda haka zuciyar Ahaz da ta mutanensa suka firgita, sai ka ce itatuwa a kurmin da iska ta girgiza.
3 Et le Seigneur dit à Isaïe: Sors au-devant d’Achaz, toi et Jasub ton fils qui t’est resté, et va à l’extrémité du canal de la piscine supérieure, sur la voie du champ du foulon.
Sai Ubangiji ya ce wa Ishaya, “Fita, kai da ɗanka Sheyar-Yashub, don ku sadu da Ahaz a ƙarshen wuriyar da take kawo ruwa daga Tafkin Tudu, a hanyar Filin Mai Wanki.
4 Et tu lui diras: Voyez à vous tenir en repos; ne craignez point, et que votre cœur ne tremble point à cause de ces deux bouts de tisons fumants, devant la colère de Rasin, roi de Syrie, et du fils de Romélie;
Ka faɗa masa, ‘Ka yi hankali, ka natsu kada kuma ka ji tsoro ko ka damu, kada ka ji tsoron fushin sarki Rezin da na Aram da na ɗan Remaliya, ba wani abu mai hatsari ba ne, bai fi hayaƙin’yan ƙirare biyu da suke cin wuta ba.
5 Parce que la Syrie, Ephraïm et le fils de Romélie ont formé de mauvais desseins contre vous, disant:
Aram, Efraim da ɗan Remaliya sun ƙulla maƙarƙashiya, suna cewa,
6 Montons contre Juda, et mettons-le en mouvement, faisons-le venir à nous, et établissons-y pour roi le fils de Tabéei.
“Bari mu kai wa Yahuda hari; bari mu yayyage su mu rarraba su a tsakaninmu, mu naɗa Tabeyel sarki a kansu.”
7 Voici ce que dit le Seigneur Dieu: Cela ne subsistera pas et ne sera même pas.
Duk da haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “‘Ba zai faru ba, ba zai auku ba,
8 Mais la capitale de la Syrie est Damas, et le chef de Damas est Rasin; et encore soixante-cinq ans, et Ephraïm cessera d’être un peuple.
gama kan Aram shi ne Damaskus, kan Damaskus kuma kawai shi ne Rezin. Cikin shekaru sittin da biyar za a wargaje Efraim har ba za tă iya rayuwa ta zama al’umma ba.
9 Et la capitale d’Ephraïm est Samarie, et le chef de Samarie le fils de Romélie. Si vous ne croyez pas, vous ne persévérerez pas.
Kan Efraim shi ne Samariya, kan Samariya kuma kawai shi ne ɗan Remaliya. In ba ku tsaya da ƙarfi cikin bangaskiyarku ba, ba za ku dawwama ba.’”
10 Le Seigneur parla encore à Achaz, disant:
Ubangiji ya kuma yi magana wa Ahaz ya ce,
11 Demande pour toi un miracle au Seigneur ton Dieu, au fond de l’enfer, ou au plus haut des cieux. (Sheol h7585)
“Ka roƙi Ubangiji Allahnka yă ba ka alama, ko daga zurfafa masu zurfi ko kuwa daga can cikin sama.” (Sheol h7585)
12 Et Achaz dit: Je n’en demanderai pas, et je ne tenterai pas le Seigneur.
Amma Ahaz ya ce, “Ba zan nema ba; ba zan gwada Ubangiji ba.”
13 Et le prophète dit: Écoutez donc, maison de David: Est-ce peu pour vous d’être fâcheux aux hommes, puisque vous êtes fâcheux même à mon Dieu?
Sa’an nan Ishaya ya ce, “To, ku saurara, ya ku gidan Dawuda! Abin kirki kuke yi ne da kuka ƙure haƙurin jama’a? Ko haƙurin Allah ne kuma kuke so ku ƙure?
14 À cause de cela le Seigneur lui-même vous donnera un signe. Voilà que la vierge concevra et enfantera un fils, et son nom sera appelé Emmanuel.
Saboda haka Ubangiji kansa zai ba ku alama. Ga shi budurwa za tă yi ciki, za tă haifi ɗa, za tă kuwa kira shi Immanuwel.
15 Il mangera du beurre et du miel, en sorte qu’il sache réprouver le mal et choisir le bien.
In ya yi girma har ya isa yanke shawara don kansa, madara da zuma ne abincinsa.
16 Parce qu’avant que l’enfant sache réprouver le mal et choisir le bien, la terre que tu détestes sera abandonnée de ses deux rois.
Amma kafin yaron yă isa yanke shawara yă ƙi abin da yake mummuna, yă zaɓi abin da yake nagari, ƙasashen sarakunan nan biyu da kuke tsoro za su zama kango.
17 Le Seigneur amènera, avec le roi des Assyriens, sur toi, sur ton peuple et sur la maison de ton père, des jours qui ne sont pas venus depuis la séparation d’Ephraïm d’avec Juda.
Ubangiji zai aukar maka da kwanakin wahala, kai da jama’arka, da dukan iyalin gidan sarauta, waɗanda suka fi muni tun lokacin da aka raba mulkin Efraim daga na Yahuda, zai kawo sarkin Assuriya.”
18 Il arrivera en ce jour que Dieu sifflera pour appeler la mouche qui est à l’extrémité des fleuves de l’Égypte, et l’abeille qui est dans la terre d’Assur;
A wannan rana Ubangiji zai yi feɗuwa yă kira ƙudaje daga rafuffuka masu nisa na Masar da kuma ƙudan zuma daga ƙasar Assuriya.
19 Et elles viendront et elles se reposeront toutes dans les torrents des vallées, et dans les cavernes des pierres, et sur tous les arbrisseaux et dans tous les trous.
Za su zo su mamaye kwazazzabai da kogwanni cikin duwatsu, a kan dukan ƙayayyuwa da dukan rammukan ruwa.
20 En ce jour-là, le Seigneur rasera avec un rasoir emprunté sur ceux qui sont au-delà fleuve et sur le roi des Assyriens la tête, et le poil des pieds et toute la barbe.
A wannan rana Ubangiji zai yi amfani da rezan da aka yi haya daga ƙetaren Kogi, sarkin Assuriya ke nan, yă aske kanku da gashin ƙafafunku, zai kuma aske gemunku.
21 Et il arrivera en ce temps-là qu’un homme nourrira une vache et deux brebis,
A ranar, mutum zai bar karsana ɗaya da awaki biyu da rai.
22 Et à cause de l’abondance du lait il mangera du beurre; car il mangera du beurre et du lait, quiconque aura été laissé au milieu de la terre.
Kuma saboda yalwa madarar da suke bayarwa, zai kasance da madarar da zai sha. Dukan waɗanda suka rage a ƙasar za su sha madara da zuma.
23 Et il arrivera en ce jour-là, qu’en tout lieu où il y aura eu mille pieds de vigne, à mille pièces d’argent, ces pieds de vigne seront changés en épines et en ronces.
A wannan rana, a kowane wuri inda akwai kuringa dubu da kuɗinsu ya kai shekel dubu na azurfa, ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne kawai za su kasance a can.
24 On y entrera avec les flèches et l’arc; car les ronces et les épines seront sur toute la terre.
Mutane za su je can da baka da kibiyoyi, gama ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne za su rufe ƙasar.
25 Quant à toutes les montagnes qui seront bien sarclées, la crainte des épines et des ronces ne les atteindra pas, mais elles serviront de pâturage au bœuf, et le menu bétail les foulera aux pieds.
Game da dukan tuddai da dā ake nome da garemani kuwa, ba za ku ƙara je wurin ba saboda tsoron ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya; za su zama wuraren da ake kai shanu a sake su su yi ta yawo da kansu, tumaki kuma su yi ta gudu.

< Isaïe 7 >